Sashe 140
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kallonta duk sukayi, anya kuwa! To ai ba zaune suke ba da zata fad'i haka, Ummy ce tace "Ban sani ba nima Hamna, kuma yanzu daga asibiti nake ba can suka je ba."
Karaf ta fizgi makullin motar Ummy ta nufi k'ofa tana fad'in "Zan duba duk asibitin dake garin nan."
Bayanta Ummy tabi da sauri haka ma Zeituna, suna fita daga farfajiyar motarsu ta shigo gidan, tsayawa duka sukayi suna kallonsu, anan Jibril ya tsaya Ammar ya fito yana rintse ido da takawa da k'yar, tana ganinshi ta taka da sauri tana dudduba jikinshi, k'ura mata ido yayi yana kallo saida ta gama dubawa ta d'ago suka had'a ido, hannu tasa ta share yar k'wallar data taho mata ta kalleshi tace "Kana lafiya?"
Saida ya d'an sunkuyo da kanshi kusanta yace "Kankana duk damuwa ne a kaina ta saki zubar da hawaye?"
Kallonshi tayi sai taji haushin kanta da kunyar kanta sun kamata, saida ta d'an kalli gefenta taga Jibril ya sakar mata ido yana kallo, bata yarda ta juya ta kalli su Ummy ba kawai ta ruga a guje tayi b'angaren Amna, saida ta b'acewa ganinshi sannan ya kalli gabanshi, ido cikin ido suka kalli juna shi da Ummy, ga damuwa da tashin hankali da kuma soyayyarshi fal idonta, amma ba zata iya matsowa inda yake ba, Zeituna ce ta matso tace "Yah Ammar ya jikin? Hatsari kukayi?"
Murmushi ya mata yace "Uwata karki damu kinji, ba wani babban abu bane ai, k'afata ce kawai ta d'an bugu, gashi ma da kaina na zo gida."
"Allah ya k'ara kiyayewa to." Murmushi ya mata yace "Nagode, zan shiga ciki."
B'angarensu ya nufa shima, su Zeituna na komawa suka fad'a ma su Husseina, nan suka fito suka nufi nasu b'angaren, yana shiga Amna na zaune kan kujera tana kallon Hamna data shigo mata a gigice ta ganshi yana d'angyasawa, da sauri ta taso tana fad'in "Duniyata lafiya? Meya sameka?"
Rumgumeta yayi jikinshi wanda hakan yasa ya kalli Hamna dake bayansu zaune, murmushi ya mata inda yace "Kwantar da hankalinki me ni, d'an k'aramin ciwo ne karki sa min kanki a damuwa, ina lafiya."
Ganin su Husseina sun shigo yasa ta raba kanta dashi ta taimaka mishi ya zauna, suma zaune sukayi inda suke jajata mishi suna tambayar ba'asi, nan ma wani zagin ya dinga zunduma ma mai motar nan su kam banda dariya babu abinda suke, sai Hamna dake kallonshi da mamakin irin halinshi, tana so ta tashi ta bar wurin amma ta rasa me yasa bata son yin nesa da wajen, Husseina ce tace ma Amna "Ki samu ruwan zafi saiki gasa masa k'afar, idan kin kamalla sai ki shafa masa rob ko victago."
Mik'ewa Amna tayi kamar ba mai rumk'umemen ciki ba tana fad'in "To."
Saida ta shiga madafa Hamna ta mik'e zata bi bayanta ta kalleshi tace "Ya kamata ka fad'a musu rob ya k'ara tsada, ina ga yanzu zaka buk'aci likitan k'ashin nan."
Shigewa tayi su dai babu abinda suka gane, amma sai gani sukayi ya saki murmushi mai tsadar gaske, basu d'auki lokaci ba Amna ta fito ta nufi teburin abinci ta d'auko kwanuka ruwa da duk abun buk'ata, Hamna kuma na rik'e da roba d'auke da ruwan d'umi da k'aramin towel mai taushi sosai, a tare suka aje gabanshi sai Amna data shiga d'aki ta d'auko victago, cike da mugunta Hamna tace "Ban shi da kaina zan shafa mishi, yau zan gane k'aryar jarumtar da ake mana."
Su Zeituna ta kalla tace "Aunty ku duba mana idonshi idan kuka ga alamar hawaye to akwai buk'atar ku fara d'inka masa atamfa."
Rintse ido yayi, wannan magana ta k'arshe ba k'aramin tab'a shi tayi ba, shi Hamna zata ce a had'a da atamfa? Ma'ana fa ta mayar dashi d'an daudu, jar ubancen, shi kam da Hamna a matsayin matarsa take tayi wannan maganar daya mata luguden bulaliyarshi ko zata shiga hankalinta, dan ya fahimci duka ko zagi ba zai sata shakkarshi, tsayawa ya nuna mata mazantaka shine zaisa ta shiga hankalinta. Su Husseina dariya sukayi tare da tashi Zeituna na fad'in "Na yarda da jarumtar yah Ammar Hamna, ba zai bani kunya ba dan yana da uwa bafulatana, juriya da b'oye hawaye ba sabon abu bane ga fillo."
Tana kallon cikin idonshi tace "Zamu gani."
Husseina ma cewa tayi "Saida safenku." Kallonshi tayi tace "Ammarun Hajia yau fa gaka hannun 'yan biyun Ummynka, ya zata kasance gobe da safe kun bamu labari."
Dariya akayi suka fice, Amna abinci ta zubo ta zauna kusa dashi ta dinga bashi a baki cikin kwanciyar hankali, jimawar da sukayi yasa Hamna cewa "Ke dallah kiyi sauri ki gama bashi sai kace zai cinye abincin shi na k'arshe."
Kallonta tayi tana turo baki tace "Haba Hamna ke baki da imani ne, dubi fa yanda k'afarsa tayi ko motsi bayayi da kyau."
Sunkuyar da kanta tayi hakan yasa shi tallabo fuskarta, hawaye ne suka kwaranyo wanda yasa shi jin tausayinta, tunani dayawa ne ya zo masa a daidai lokacin, yanzu fa irin wannan da ace akwai k'arar kwana da ya zatayi? Gashi tana da tsohon ciki daga yanzu zuwa kowane lokaci zata iya haihuwa, sannan akwai wata kulalliya tsakaninshi da yer uwarta da yake buk'atar ta yafe masa ko da bata san da al'amarin ba. Share mata hawayen yayi yace "Karki zubar min da hawayenki kinji, kada ki karya min zuciyata nima nayi kuka."
Jinjina kai tayi tace "To na daina." Murmushi yayi yace "Yawwa to bani magani na nasha."
D'aukowa tayi ta bashi yasha kafin ta kalli Hamna tace "Mik'o min ruwan."
A daidai wannan lokacin sosai taji zafi zuciyarta, dan abun a bayyane yake cewa yar uwarta tafi iko da shi duk da ita ya fara sani, kuma bata da yanda zatayi daya wuce hak'uri, kasa tausar kanta tayi tana mik'a mata ta fice a d'akin da sauri har ta bar makullin motar Ummy anan, Amna bata kula da komai ba sai dai shi ya fahimci ranta bai mata dad'i ba, fuskar matarshi ya ci gaba da kallo tana gasa mishi k'afarshi wacce ke luf da bak'in gashi kwance kan jar fatarshi.
*Alhamdulillah*
14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*RAYUWAR RAYAM*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
_*MY BK* INA TAYAKI MURNAR FARA SABON NOVEL D'IN KI, ALLAH YASA MU ANFANA DA DARASIN DAKE CIKI, ALLAH YASA YANDA KIKA FARA LAFIYA KI GAMA LAFIYA, ALLAH YA K'ARA MIKI LAFIYA MASOYIYA._
🦯🚔🦯👮♀️ *KUTKALE*👮♀️🦯🚔 🦯
*(PRISON)*
_MA SADIJA BARKA BARKA DA KAMMALA NOVEL D'INKI *KUTKALE*, ALLAH UBANGIJI YASA MU ANFANA DA DARASIN DAKE CIKI, ALLAH YA YAFE MIKI KURAKUREN DA KIKAYI A CIKI, ALLAH YA BAKI LADAR FADAK'ARWA, SAI MUN JIKI A NOVEL NA GABA INSHA ALLAH._
🎂 *Sis Chappa*🎂
_Barka da k'arin shekara 3 a duniya, Allah ya karo shekaru masu albarka, Allah ya baki lafiyar anfanarsu ta hanyar data dace, bébé Khalid yace yana tayaki murna._
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
_51_
Ummy ta fito goye da Shureim zata tafi duba jikin Ammar Hajia ta fito daga d'akinta, tana ganinta tace "Ke kuma ina zaki je yanzu da dare da kika goya shi?"
Cikin ladabi tace "Hajia zan duba Ammar ne."
Da wani kallon rashin mutumci ta kalleta tace "Ban gane ba? Ammar d'in baya lafiya?"
"Eh Hajia, d'azu ne ya samu hatsari a hanya, amma da sauk'i sosai k'afarsa ce kawai ta bugu."
Cikin fad'a tace "Amma kuma shine banda darajar da wani zai shiga ya fad'a min halin da ake ciki."
Tsaki tayi ta nufi hanyar fita waje, Ummy kuma tunaninta ko dai ta d'auka Amar aka ce shalelenta, dan haka tace "Kiyi hak'uri Hajia, dan naga ba kya jin dad'i ne shiyasa."
Bata juyo tace komai ba sai ci gaba da tafiya da takeyi, ganin dai sun doshi b'angaren tare yasa Ummy cewa "Hajia Ammar ne fa."
Cak ta tsaya ta juyo tana kallonta tace "Ammar ne fa? Eh Ammar d'in, me kike tunani? To saurara kiji da kyau, na jima ina rayuwa cikin k'arya da yaudara, jiya zuwa yau ne kad'ai nasan masoyana na gaskiya, duk gidan nan babu mai k'aunata kamar shi Ammar d'in."
Juyawa tayi ta shiga ita ma tana biye da ita, babu sallama ta shiga ta samu Amna ta gama gasa masa k'afarsa, zaune tayi kan kujera kusa dashi tana kallon k'afarsa tace "Mijin ya jikin? Ashe takaba ka kusa sani, kaji yanda zuciyata ta buga, kada ka sake min irin haka gaskiya."
Yanda ta gama maganar da shagwab'a, dariya sukayi sai Ummy data saki baki tana kallon, me ya samu Hajia ne? Ammar ne fa ko ta manta? Yaushe haka ta fara faruwa? Cikin murmushi Ammar ya ja hancinta yana rera mata baitin wak'ar gari ya waye yace "Haba, na gwadaki ne kawai dan ramawa."
Cikin turo baki tace "Kuma duk gidan nan babu wanda ya iya fad'a min ma sai yanzu na sani."
Saida ya saci kallon Ummy sannan ya kalli Hajia yace "Ai Hajia sai munsha lahaula, dan soyayyata dake yanda zata jijjiga wasu zaisa a kafa mana na mujiya, dan tunaninsu yaushe ne kuma tayaya haka ta fara faruwa."
Wani kallo Ummy ta masa jin ya karanta mata tunaninta, dariya Hajia tayi ta mik'e tana dafe k'afarshi tace "Zan tafi saida safe zan zo muyi hira."
Murmushi yayi har ta juya zata tafi sai kuma ta juyo, ba zato ba tsammani ta rarumeshi ta rumgume tana fad'in "Nima na rama buru-ubar da kake min."
Sakinta tayi ta juya shi kuma yace "Ramuwa mai citta."
Fita tayi Ummy na kallo al'ajabi duk ya kasheta, kallonta yayi yace "Ummy zauna mana, kawo min shi dan Allah." Ya fad'a yana tara hannu ta bashi Shureim.
Kujerar da tayi niyyar zama ta kalla sai taga makullin motar ta, takawa tayi ta d'auki makullin ta nuna masa tace "Dama shi na zo d'auka."
Karaf ta fizgi makullin motar Ummy ta nufi k'ofa tana fad'in "Zan duba duk asibitin dake garin nan."
Bayanta Ummy tabi da sauri haka ma Zeituna, suna fita daga farfajiyar motarsu ta shigo gidan, tsayawa duka sukayi suna kallonsu, anan Jibril ya tsaya Ammar ya fito yana rintse ido da takawa da k'yar, tana ganinshi ta taka da sauri tana dudduba jikinshi, k'ura mata ido yayi yana kallo saida ta gama dubawa ta d'ago suka had'a ido, hannu tasa ta share yar k'wallar data taho mata ta kalleshi tace "Kana lafiya?"
Saida ya d'an sunkuyo da kanshi kusanta yace "Kankana duk damuwa ne a kaina ta saki zubar da hawaye?"
Kallonshi tayi sai taji haushin kanta da kunyar kanta sun kamata, saida ta d'an kalli gefenta taga Jibril ya sakar mata ido yana kallo, bata yarda ta juya ta kalli su Ummy ba kawai ta ruga a guje tayi b'angaren Amna, saida ta b'acewa ganinshi sannan ya kalli gabanshi, ido cikin ido suka kalli juna shi da Ummy, ga damuwa da tashin hankali da kuma soyayyarshi fal idonta, amma ba zata iya matsowa inda yake ba, Zeituna ce ta matso tace "Yah Ammar ya jikin? Hatsari kukayi?"
Murmushi ya mata yace "Uwata karki damu kinji, ba wani babban abu bane ai, k'afata ce kawai ta d'an bugu, gashi ma da kaina na zo gida."
"Allah ya k'ara kiyayewa to." Murmushi ya mata yace "Nagode, zan shiga ciki."
B'angarensu ya nufa shima, su Zeituna na komawa suka fad'a ma su Husseina, nan suka fito suka nufi nasu b'angaren, yana shiga Amna na zaune kan kujera tana kallon Hamna data shigo mata a gigice ta ganshi yana d'angyasawa, da sauri ta taso tana fad'in "Duniyata lafiya? Meya sameka?"
Rumgumeta yayi jikinshi wanda hakan yasa ya kalli Hamna dake bayansu zaune, murmushi ya mata inda yace "Kwantar da hankalinki me ni, d'an k'aramin ciwo ne karki sa min kanki a damuwa, ina lafiya."
Ganin su Husseina sun shigo yasa ta raba kanta dashi ta taimaka mishi ya zauna, suma zaune sukayi inda suke jajata mishi suna tambayar ba'asi, nan ma wani zagin ya dinga zunduma ma mai motar nan su kam banda dariya babu abinda suke, sai Hamna dake kallonshi da mamakin irin halinshi, tana so ta tashi ta bar wurin amma ta rasa me yasa bata son yin nesa da wajen, Husseina ce tace ma Amna "Ki samu ruwan zafi saiki gasa masa k'afar, idan kin kamalla sai ki shafa masa rob ko victago."
Mik'ewa Amna tayi kamar ba mai rumk'umemen ciki ba tana fad'in "To."
Saida ta shiga madafa Hamna ta mik'e zata bi bayanta ta kalleshi tace "Ya kamata ka fad'a musu rob ya k'ara tsada, ina ga yanzu zaka buk'aci likitan k'ashin nan."
Shigewa tayi su dai babu abinda suka gane, amma sai gani sukayi ya saki murmushi mai tsadar gaske, basu d'auki lokaci ba Amna ta fito ta nufi teburin abinci ta d'auko kwanuka ruwa da duk abun buk'ata, Hamna kuma na rik'e da roba d'auke da ruwan d'umi da k'aramin towel mai taushi sosai, a tare suka aje gabanshi sai Amna data shiga d'aki ta d'auko victago, cike da mugunta Hamna tace "Ban shi da kaina zan shafa mishi, yau zan gane k'aryar jarumtar da ake mana."
Su Zeituna ta kalla tace "Aunty ku duba mana idonshi idan kuka ga alamar hawaye to akwai buk'atar ku fara d'inka masa atamfa."
Rintse ido yayi, wannan magana ta k'arshe ba k'aramin tab'a shi tayi ba, shi Hamna zata ce a had'a da atamfa? Ma'ana fa ta mayar dashi d'an daudu, jar ubancen, shi kam da Hamna a matsayin matarsa take tayi wannan maganar daya mata luguden bulaliyarshi ko zata shiga hankalinta, dan ya fahimci duka ko zagi ba zai sata shakkarshi, tsayawa ya nuna mata mazantaka shine zaisa ta shiga hankalinta. Su Husseina dariya sukayi tare da tashi Zeituna na fad'in "Na yarda da jarumtar yah Ammar Hamna, ba zai bani kunya ba dan yana da uwa bafulatana, juriya da b'oye hawaye ba sabon abu bane ga fillo."
Tana kallon cikin idonshi tace "Zamu gani."
Husseina ma cewa tayi "Saida safenku." Kallonshi tayi tace "Ammarun Hajia yau fa gaka hannun 'yan biyun Ummynka, ya zata kasance gobe da safe kun bamu labari."
Dariya akayi suka fice, Amna abinci ta zubo ta zauna kusa dashi ta dinga bashi a baki cikin kwanciyar hankali, jimawar da sukayi yasa Hamna cewa "Ke dallah kiyi sauri ki gama bashi sai kace zai cinye abincin shi na k'arshe."
Kallonta tayi tana turo baki tace "Haba Hamna ke baki da imani ne, dubi fa yanda k'afarsa tayi ko motsi bayayi da kyau."
Sunkuyar da kanta tayi hakan yasa shi tallabo fuskarta, hawaye ne suka kwaranyo wanda yasa shi jin tausayinta, tunani dayawa ne ya zo masa a daidai lokacin, yanzu fa irin wannan da ace akwai k'arar kwana da ya zatayi? Gashi tana da tsohon ciki daga yanzu zuwa kowane lokaci zata iya haihuwa, sannan akwai wata kulalliya tsakaninshi da yer uwarta da yake buk'atar ta yafe masa ko da bata san da al'amarin ba. Share mata hawayen yayi yace "Karki zubar min da hawayenki kinji, kada ki karya min zuciyata nima nayi kuka."
Jinjina kai tayi tace "To na daina." Murmushi yayi yace "Yawwa to bani magani na nasha."
D'aukowa tayi ta bashi yasha kafin ta kalli Hamna tace "Mik'o min ruwan."
A daidai wannan lokacin sosai taji zafi zuciyarta, dan abun a bayyane yake cewa yar uwarta tafi iko da shi duk da ita ya fara sani, kuma bata da yanda zatayi daya wuce hak'uri, kasa tausar kanta tayi tana mik'a mata ta fice a d'akin da sauri har ta bar makullin motar Ummy anan, Amna bata kula da komai ba sai dai shi ya fahimci ranta bai mata dad'i ba, fuskar matarshi ya ci gaba da kallo tana gasa mishi k'afarshi wacce ke luf da bak'in gashi kwance kan jar fatarshi.
*Alhamdulillah*
14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
*RAYUWAR RAYAM*
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
_*MY BK* INA TAYAKI MURNAR FARA SABON NOVEL D'IN KI, ALLAH YASA MU ANFANA DA DARASIN DAKE CIKI, ALLAH YASA YANDA KIKA FARA LAFIYA KI GAMA LAFIYA, ALLAH YA K'ARA MIKI LAFIYA MASOYIYA._
🦯🚔🦯👮♀️ *KUTKALE*👮♀️🦯🚔 🦯
*(PRISON)*
_MA SADIJA BARKA BARKA DA KAMMALA NOVEL D'INKI *KUTKALE*, ALLAH UBANGIJI YASA MU ANFANA DA DARASIN DAKE CIKI, ALLAH YA YAFE MIKI KURAKUREN DA KIKAYI A CIKI, ALLAH YA BAKI LADAR FADAK'ARWA, SAI MUN JIKI A NOVEL NA GABA INSHA ALLAH._
🎂 *Sis Chappa*🎂
_Barka da k'arin shekara 3 a duniya, Allah ya karo shekaru masu albarka, Allah ya baki lafiyar anfanarsu ta hanyar data dace, bébé Khalid yace yana tayaki murna._
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
_51_
Ummy ta fito goye da Shureim zata tafi duba jikin Ammar Hajia ta fito daga d'akinta, tana ganinta tace "Ke kuma ina zaki je yanzu da dare da kika goya shi?"
Cikin ladabi tace "Hajia zan duba Ammar ne."
Da wani kallon rashin mutumci ta kalleta tace "Ban gane ba? Ammar d'in baya lafiya?"
"Eh Hajia, d'azu ne ya samu hatsari a hanya, amma da sauk'i sosai k'afarsa ce kawai ta bugu."
Cikin fad'a tace "Amma kuma shine banda darajar da wani zai shiga ya fad'a min halin da ake ciki."
Tsaki tayi ta nufi hanyar fita waje, Ummy kuma tunaninta ko dai ta d'auka Amar aka ce shalelenta, dan haka tace "Kiyi hak'uri Hajia, dan naga ba kya jin dad'i ne shiyasa."
Bata juyo tace komai ba sai ci gaba da tafiya da takeyi, ganin dai sun doshi b'angaren tare yasa Ummy cewa "Hajia Ammar ne fa."
Cak ta tsaya ta juyo tana kallonta tace "Ammar ne fa? Eh Ammar d'in, me kike tunani? To saurara kiji da kyau, na jima ina rayuwa cikin k'arya da yaudara, jiya zuwa yau ne kad'ai nasan masoyana na gaskiya, duk gidan nan babu mai k'aunata kamar shi Ammar d'in."
Juyawa tayi ta shiga ita ma tana biye da ita, babu sallama ta shiga ta samu Amna ta gama gasa masa k'afarsa, zaune tayi kan kujera kusa dashi tana kallon k'afarsa tace "Mijin ya jikin? Ashe takaba ka kusa sani, kaji yanda zuciyata ta buga, kada ka sake min irin haka gaskiya."
Yanda ta gama maganar da shagwab'a, dariya sukayi sai Ummy data saki baki tana kallon, me ya samu Hajia ne? Ammar ne fa ko ta manta? Yaushe haka ta fara faruwa? Cikin murmushi Ammar ya ja hancinta yana rera mata baitin wak'ar gari ya waye yace "Haba, na gwadaki ne kawai dan ramawa."
Cikin turo baki tace "Kuma duk gidan nan babu wanda ya iya fad'a min ma sai yanzu na sani."
Saida ya saci kallon Ummy sannan ya kalli Hajia yace "Ai Hajia sai munsha lahaula, dan soyayyata dake yanda zata jijjiga wasu zaisa a kafa mana na mujiya, dan tunaninsu yaushe ne kuma tayaya haka ta fara faruwa."
Wani kallo Ummy ta masa jin ya karanta mata tunaninta, dariya Hajia tayi ta mik'e tana dafe k'afarshi tace "Zan tafi saida safe zan zo muyi hira."
Murmushi yayi har ta juya zata tafi sai kuma ta juyo, ba zato ba tsammani ta rarumeshi ta rumgume tana fad'in "Nima na rama buru-ubar da kake min."
Sakinta tayi ta juya shi kuma yace "Ramuwa mai citta."
Fita tayi Ummy na kallo al'ajabi duk ya kasheta, kallonta yayi yace "Ummy zauna mana, kawo min shi dan Allah." Ya fad'a yana tara hannu ta bashi Shureim.
Kujerar da tayi niyyar zama ta kalla sai taga makullin motar ta, takawa tayi ta d'auki makullin ta nuna masa tace "Dama shi na zo d'auka."