Sashe 91
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana zaune kan kujerar k'arfe tana girki a k'aramin gas d'in ta taji muryarta, mik'ewa tayi da murna ita ma ta d'an fito daga cikin runfar zanar da tayi shamaki a wurin, suna ganin juna Amna ta rumgumeta sosai tana farin ciki, ita ma rumgumeta tayi tana fad'in "Auta ta, ke ce haka bazata? Ke da wa?"
D'agowa tayi ta juya bayanta da tsantsar farin ciki tace "Tare da Hamna da yah Ammar, shine ya kawo mu."
Murmushi tayi ta kama hancinta tace "Kice dake da angon naki ko? Ja'ira kawai ai nasan komai, Ummynku ta fad'a min a waya."
Sake fad'awa tayi jikinta tace "Kai Mama, da saura fa."
Da d'an mamaki tace "Amma ya akayi kika riga Hamna shigowa? Kullum ita ke fara shigowa da ihun murna, ko dai dan kuna tare da d'an albarka ne yasa ya daidaita mata zama?"
Tab'e baki Amna tayi tace "Tace bata da lafiya ne, tun jiya nima na kasa gane kanta."
K'arasowar Hamna yasa Hadiza kallonta, yanayin fuskarta ne ya canja lokaci d'aya saboda ganin wani sabon yanayi a tare da Hamnar, hatta tafiya ma da k'yar take yinta alamar tana mata wahala, Amna ce tayi bayan mahaifiyarta su tana bud'a fridge d'in dake kusa dasu ta d'auko ruwan sanyi, Hamna ma na zuwa fad'awa tayi jikin mamansu ta fashe da kuka, wannan abu shi ya d'aga hankalin Hadiza harda Amna dake shirin shan ruwa amma ta dakata tana kallonta da mamaki, cikin rud'u Hadiza ta d'agota tace "Hamna, lafiya? Meye na kuka kuma? Wani abu ne ya faru?"
Amna ce tayi saurin cewa "Mama kawai ki rabu da ita iskanci ne, na fad'a miki tun jiya fa take wani basarwa tana share mutane, ba wani abinda ke damunta."
Juyawa Hadiza tayi ta kalleta tace "Yi min shiru Amna, akan me zaki ce a rabu da ita? Kinsan me yale damunta ne? Ai kamata yayi ace ke kika fi kowa sanin abinda ke damunta duba da 'yan biyunki ce."
Mayar da hankalinta tayi kan Hamna da har yanzu take kuka ta jata suka zauna kan kujerun wurin ta ci gaba da tambayarta, amma sai Hamna ta share hawaye cikin shagwab'a tace "Mama kawai nayi kewarki ne sosai, munfi shekara bamu ganki ba fa, muna so mu zo amma Hajia ta hana mu, na fidda rai da zan ganki sai kawai boss ya kawo mu, dole nayi kukan farin ciki."
Dangware mata kai Hadiza tayi tace "Ke dai akwai sakarya wallahi, yanzu akan hakane kika d'aga min hankali."
Amna ce ta cire takalmi ta shiga d'akin tana fad'in "Ai dama na fad'a miki iskanci ne."
Da kallon jin haushi Hamna ta bita tace "Ke wallahi bana son iskanci kinji ko, ni sa'arki ce da zaki tsaya kina fad'a min abinda kika ga dama?"
Daga cikin d'akin tana cire kaya tace "Aje anyi d'in, inba raina mutane ba meye na duk wani canzawa lokaci d'aya? Tun jiya da kika je karatu d'akin Ummy kika zama wata iri dake."
Mik'ewa Hamna tayi ta shiga cikin d'akin tana fad'in "Wallahi kika min rashin kunya saina ci ubanki a wurin nan, ina ruwanki da canzawata to? Idan kinji haushi ki fita harkata mana, yar jaraba kai."
Daga waje Hadiza tace "Ya isa haka to, kar na sake ji bakin kowa a wurin nan."
Amna ce tace "Mama ki rabu da ita ta ci uban nawa mana idan zata iya."
Kallon Hamna tayi tace "Ke kinsan ko gawata wallahi tafi k'arfin ki, dan kin rigani fitowa duniya bafa tazara mai tsayi kika ban ba."
K'wafa Hamna tayi ita ma ta fara cire kayanta da nufin shiga wanka, kusan a tare suka jero kowace da d'aurin k'irji da zanin Hadiza na atamfa zasu fito hakan yasa suka matse junansu, ture juna sukayi inda Hamna ta bita da harara da tsaki, Hadiza dai na kallonsu tana jin dad'i dan ko ba komai yau tana jin hayaniya a gidanta na yara, Amna ce ta d'auki bokiti ta tara ruwa a bakin panpo inda Hamna ta d'auke kwandon sabulun wankan, Amna ce ta kalli mahaifiyar tasu tace "Mama ki fad'a mata ta ban kwandon nan."
Kallonta Maman tayi tace "Hamna ki bata kwandon idan ta fito kya shiga."
Cikin turo baki Hamna tace "Wallahi Mama ba zan bata ba saina fara yi, tun a hanya fa tasan ina cewa fitsari nake ji."
Hadiza ce tace "To ki shiga kiyi fitsarin ki fito saiki bata wurin."
Cikin yanayin sangarta tace "Mama kawai ki k'yalemu kiyi kallonmu, karki sa wannan sakaryar ta raina ni saboda kina d'aukar ta autarki."
Hadiza ce tace "To shikenan na saka muku ido, kafin nan ku fad'a min ina yaron kirkin yake ne? Kunce shi ya kawoku kuma banga ya shigo ba har yanzu."
Tab'e baki Hamna tayi tace "Waya sanin masa mugun kawai, Allah yasa ma ya tafi ya barmu nan mu kwana."
Girgiza kai kawai Hadiza tayi ta ci gaba da duba girkinta, tana kallo Hamna ta damk'i bokitin ruwan tana so ta raba Amna dashi, ita ma rik'ewa tayi sosai tace ba zata saki ba, hakan ne ya janyo musu kokawa da bokitin ruwan har suna ta zubewa a banza, wajen wannan tak'ak'abuwa bokitin ya fad'i k'asa ruwan suka watse a banza, da sauri Hadiza ta lek'o daga yar rumfar tana fad'in "La'ilaha illalahu, wai ku yanzu haka abun naku ya zama? Meye ha...?" Shiru tayi saboda ganin Ammar ya shigo cikin gidan.
Amna ce tayi k'asa da kanta yayin da Hamna kuma ta zabga mishi harara ta d'auke kanta, Ammar kam kawar da idonshi yayi daga kallonsu saboda ganinsu kamar 'ya'yan gwarawa, kowace da d'aurin k'irji hallitarsu ta fito fili, ta bayan Amna ya bi ya wuce yana kallon Hamna dake masa wani kallon iya shege, tun kafin ya k'arasa Hadiza ta aje masa kujera tana fad'in "Ammar ina ka shiga? Sun ce kai ka kawosu amma shiru baka shigo ba."
Sam babu fara'a a fuskarshi ya zauna akan labb'anshi ya amsa da "Masallaci na tafi Tanti."
Da fara'a sosai tace "Haba shiyasa, to anyi sallah lafiya?"
Ciki ciki ya amsa da "Lafiya lau." Kallonshi Tanti tayi tana murmushi a zuciyarta tana ayyanawa yau 'yan mulkin ne akan shi shiyasa ko gaisheta ya kasa yi, kallonsu Amna tayi da har yanzu suka kasa sulhunta kansu, girgiza kai tayi tace "Auta, ki barta tayi sai kiyi kinji, ki zo ki kawowa yayanku ruwa yasha kya samu lada ma."
Da sauri Hamna ta kalli Hadiza Amna ita kuma turo baki tayi ta sakar mata bokitin tana hararanta, cikin sand'a take takowa kamar wata marar gaskiya saboda ganin yanda Ammar ya had'e rai kamar hadarin gabas, cikin tsoron kar ya daketa ta samu ta shige d'akin ta d'auko hijab ta saka ta fito, ruwa ta d'auko mishi ta zuba ta bashi a lokacin da Hadiza ke tambayarshi meyasa bai tsaya d'aurin auren babban shi ba? Saida ya karb'i ruwan ya d'an kurb'a ya kalli Amna da jajayen ido yace "Wuce d'aki."
Kallonshi tayi kamar zatayi kuka cikin muryar tsoro tace "Yah Ammar..dama...alwala zanyi kafin ta fito."
Sake wurgo mata idonshi yayi wanda yasa gabanta fad'uwa, dan a yanda suka sani ko gaban mahaifiyarsu ta kama saiya kasheka da mari har ma ya d'auki madaki, ajiyar zuciya ta sauke mai sautin gaske saboda alamar daya mata da ido ta wuce, da sauri ta nufi wajen buta ta zuwa ruwa lokacin Hamna ta shiga wanka, bai sake tankawa ba har saida ya ga shigar Amna d'aki kafin ya kalli Hadiza dake kwashe abinci a kwanuka ya tab'e baki yace "Me yasa zanje d'aurin auren?"
Juyowa tayi ta kalleshi ita har ta manta ma data tambayeshi, tun yana k'aramin yaro take k'aunar shi har zuciyarta, ta sanshi tasan halinshi fiye da uwar data haifeshi, hakan yasa bata damu ba saima murmushi da tayi tace "Saboda mahaifinka ne mana, kuma zaiyi farin cikin ganinka a wurin a kusa da shi."
Murmushin rainin hankali yayi tare da kallon farfajiyar gidan yace "Ba zan iya wannan abun kunyar ba, tsofai-tsofai da kai kayi wani wai aure, auren ma ba da babbar mace ba ko wata bazawara, yarinya mai k'ananun shekaru, ko ni dake d'ansa wannan yarinyar ta min kad'an na aureta wallahi bare kuma shi."
Wani wawan tsaki yayi alamun dai abun ya dameshi sosai, banda dariya ba abinda Hadiza keyi kafin tace "Yaron kirki kenan, amma me yasa kake ganin ta maka kad'an?"
Sam babu alamar wasa ko kunya yace "Saboda ba zata iya d'aukata ba, zata iya mutuwa tun kafin aje ko ina, sannan ni banga albarkatun dake jikinta ba wanda zasu iya d'ebewa mutum kewa."
Murje ido Hadiza tayi ta nuna abun bai wani dameta ba dan tasan halin katob'aran yaronta tace "To dama wacece zata iya da kai yarona? Ai sai yar baiwa, amma fa duk da haka ita yarinyar ta dace da mahaifinku, tunda kaga kai sabon jini ne ka mata yawa, shi kuma an kwana biyu zai iya tafiya da ita yanda ya dace."
Cike da jin an fasa mishi kai yayi wani shak'iyin murmushi yace "Hmm; shi ma fa da sauranshi, dan yanzu haka zai iya samo mana cikakken k'ane."
Kafin tayi magana Hamna ta fito daga wanka, har tayi alwala bakin panpo ta basu sake magana ba, saida ta zo daf dashi zata wuce ta gabanshi dan hanyar da zata iya sadaka da d'akin ce kawai yace "Tanti ai duk wacce na kwanta da ita na tashi ita ma kuma ta mik'e da k'afafunta, to wannan ita ce daidai dani saboda ni jaruma nake so ba raguwa ba."
Da k'arfi Hamna ta kalleshi amma kash kamar ma baisan da tsayuwarta a wurin ba, cikin murmushi Hadiza tace "Zaka sameta mai jarumta yaro na, zanyi k'ok'arin ganin haka ta faru ko saboda jin dad'in ka."
Juyawa tayi ta kalli mahaifiyar tasu dake ta harkar gabanta, sake juyowa tayi ta kalle shi tayi k'wafa ta wuce, zata shiga ciki taji ya sake cewa"Kankana."
Cak ta tsaya ta juyo tana aika mishi wani mugun kallo, kallonta yayi ya gyara zama tare da shafar gemunshi yana dariyar iskanci ya kashe mata ido d'aya yace "...
*Alhamdulillah Allah*👏
09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
D'agowa tayi ta juya bayanta da tsantsar farin ciki tace "Tare da Hamna da yah Ammar, shine ya kawo mu."
Murmushi tayi ta kama hancinta tace "Kice dake da angon naki ko? Ja'ira kawai ai nasan komai, Ummynku ta fad'a min a waya."
Sake fad'awa tayi jikinta tace "Kai Mama, da saura fa."
Da d'an mamaki tace "Amma ya akayi kika riga Hamna shigowa? Kullum ita ke fara shigowa da ihun murna, ko dai dan kuna tare da d'an albarka ne yasa ya daidaita mata zama?"
Tab'e baki Amna tayi tace "Tace bata da lafiya ne, tun jiya nima na kasa gane kanta."
K'arasowar Hamna yasa Hadiza kallonta, yanayin fuskarta ne ya canja lokaci d'aya saboda ganin wani sabon yanayi a tare da Hamnar, hatta tafiya ma da k'yar take yinta alamar tana mata wahala, Amna ce tayi bayan mahaifiyarta su tana bud'a fridge d'in dake kusa dasu ta d'auko ruwan sanyi, Hamna ma na zuwa fad'awa tayi jikin mamansu ta fashe da kuka, wannan abu shi ya d'aga hankalin Hadiza harda Amna dake shirin shan ruwa amma ta dakata tana kallonta da mamaki, cikin rud'u Hadiza ta d'agota tace "Hamna, lafiya? Meye na kuka kuma? Wani abu ne ya faru?"
Amna ce tayi saurin cewa "Mama kawai ki rabu da ita iskanci ne, na fad'a miki tun jiya fa take wani basarwa tana share mutane, ba wani abinda ke damunta."
Juyawa Hadiza tayi ta kalleta tace "Yi min shiru Amna, akan me zaki ce a rabu da ita? Kinsan me yale damunta ne? Ai kamata yayi ace ke kika fi kowa sanin abinda ke damunta duba da 'yan biyunki ce."
Mayar da hankalinta tayi kan Hamna da har yanzu take kuka ta jata suka zauna kan kujerun wurin ta ci gaba da tambayarta, amma sai Hamna ta share hawaye cikin shagwab'a tace "Mama kawai nayi kewarki ne sosai, munfi shekara bamu ganki ba fa, muna so mu zo amma Hajia ta hana mu, na fidda rai da zan ganki sai kawai boss ya kawo mu, dole nayi kukan farin ciki."
Dangware mata kai Hadiza tayi tace "Ke dai akwai sakarya wallahi, yanzu akan hakane kika d'aga min hankali."
Amna ce ta cire takalmi ta shiga d'akin tana fad'in "Ai dama na fad'a miki iskanci ne."
Da kallon jin haushi Hamna ta bita tace "Ke wallahi bana son iskanci kinji ko, ni sa'arki ce da zaki tsaya kina fad'a min abinda kika ga dama?"
Daga cikin d'akin tana cire kaya tace "Aje anyi d'in, inba raina mutane ba meye na duk wani canzawa lokaci d'aya? Tun jiya da kika je karatu d'akin Ummy kika zama wata iri dake."
Mik'ewa Hamna tayi ta shiga cikin d'akin tana fad'in "Wallahi kika min rashin kunya saina ci ubanki a wurin nan, ina ruwanki da canzawata to? Idan kinji haushi ki fita harkata mana, yar jaraba kai."
Daga waje Hadiza tace "Ya isa haka to, kar na sake ji bakin kowa a wurin nan."
Amna ce tace "Mama ki rabu da ita ta ci uban nawa mana idan zata iya."
Kallon Hamna tayi tace "Ke kinsan ko gawata wallahi tafi k'arfin ki, dan kin rigani fitowa duniya bafa tazara mai tsayi kika ban ba."
K'wafa Hamna tayi ita ma ta fara cire kayanta da nufin shiga wanka, kusan a tare suka jero kowace da d'aurin k'irji da zanin Hadiza na atamfa zasu fito hakan yasa suka matse junansu, ture juna sukayi inda Hamna ta bita da harara da tsaki, Hadiza dai na kallonsu tana jin dad'i dan ko ba komai yau tana jin hayaniya a gidanta na yara, Amna ce ta d'auki bokiti ta tara ruwa a bakin panpo inda Hamna ta d'auke kwandon sabulun wankan, Amna ce ta kalli mahaifiyar tasu tace "Mama ki fad'a mata ta ban kwandon nan."
Kallonta Maman tayi tace "Hamna ki bata kwandon idan ta fito kya shiga."
Cikin turo baki Hamna tace "Wallahi Mama ba zan bata ba saina fara yi, tun a hanya fa tasan ina cewa fitsari nake ji."
Hadiza ce tace "To ki shiga kiyi fitsarin ki fito saiki bata wurin."
Cikin yanayin sangarta tace "Mama kawai ki k'yalemu kiyi kallonmu, karki sa wannan sakaryar ta raina ni saboda kina d'aukar ta autarki."
Hadiza ce tace "To shikenan na saka muku ido, kafin nan ku fad'a min ina yaron kirkin yake ne? Kunce shi ya kawoku kuma banga ya shigo ba har yanzu."
Tab'e baki Hamna tayi tace "Waya sanin masa mugun kawai, Allah yasa ma ya tafi ya barmu nan mu kwana."
Girgiza kai kawai Hadiza tayi ta ci gaba da duba girkinta, tana kallo Hamna ta damk'i bokitin ruwan tana so ta raba Amna dashi, ita ma rik'ewa tayi sosai tace ba zata saki ba, hakan ne ya janyo musu kokawa da bokitin ruwan har suna ta zubewa a banza, wajen wannan tak'ak'abuwa bokitin ya fad'i k'asa ruwan suka watse a banza, da sauri Hadiza ta lek'o daga yar rumfar tana fad'in "La'ilaha illalahu, wai ku yanzu haka abun naku ya zama? Meye ha...?" Shiru tayi saboda ganin Ammar ya shigo cikin gidan.
Amna ce tayi k'asa da kanta yayin da Hamna kuma ta zabga mishi harara ta d'auke kanta, Ammar kam kawar da idonshi yayi daga kallonsu saboda ganinsu kamar 'ya'yan gwarawa, kowace da d'aurin k'irji hallitarsu ta fito fili, ta bayan Amna ya bi ya wuce yana kallon Hamna dake masa wani kallon iya shege, tun kafin ya k'arasa Hadiza ta aje masa kujera tana fad'in "Ammar ina ka shiga? Sun ce kai ka kawosu amma shiru baka shigo ba."
Sam babu fara'a a fuskarshi ya zauna akan labb'anshi ya amsa da "Masallaci na tafi Tanti."
Da fara'a sosai tace "Haba shiyasa, to anyi sallah lafiya?"
Ciki ciki ya amsa da "Lafiya lau." Kallonshi Tanti tayi tana murmushi a zuciyarta tana ayyanawa yau 'yan mulkin ne akan shi shiyasa ko gaisheta ya kasa yi, kallonsu Amna tayi da har yanzu suka kasa sulhunta kansu, girgiza kai tayi tace "Auta, ki barta tayi sai kiyi kinji, ki zo ki kawowa yayanku ruwa yasha kya samu lada ma."
Da sauri Hamna ta kalli Hadiza Amna ita kuma turo baki tayi ta sakar mata bokitin tana hararanta, cikin sand'a take takowa kamar wata marar gaskiya saboda ganin yanda Ammar ya had'e rai kamar hadarin gabas, cikin tsoron kar ya daketa ta samu ta shige d'akin ta d'auko hijab ta saka ta fito, ruwa ta d'auko mishi ta zuba ta bashi a lokacin da Hadiza ke tambayarshi meyasa bai tsaya d'aurin auren babban shi ba? Saida ya karb'i ruwan ya d'an kurb'a ya kalli Amna da jajayen ido yace "Wuce d'aki."
Kallonshi tayi kamar zatayi kuka cikin muryar tsoro tace "Yah Ammar..dama...alwala zanyi kafin ta fito."
Sake wurgo mata idonshi yayi wanda yasa gabanta fad'uwa, dan a yanda suka sani ko gaban mahaifiyarsu ta kama saiya kasheka da mari har ma ya d'auki madaki, ajiyar zuciya ta sauke mai sautin gaske saboda alamar daya mata da ido ta wuce, da sauri ta nufi wajen buta ta zuwa ruwa lokacin Hamna ta shiga wanka, bai sake tankawa ba har saida ya ga shigar Amna d'aki kafin ya kalli Hadiza dake kwashe abinci a kwanuka ya tab'e baki yace "Me yasa zanje d'aurin auren?"
Juyowa tayi ta kalleshi ita har ta manta ma data tambayeshi, tun yana k'aramin yaro take k'aunar shi har zuciyarta, ta sanshi tasan halinshi fiye da uwar data haifeshi, hakan yasa bata damu ba saima murmushi da tayi tace "Saboda mahaifinka ne mana, kuma zaiyi farin cikin ganinka a wurin a kusa da shi."
Murmushin rainin hankali yayi tare da kallon farfajiyar gidan yace "Ba zan iya wannan abun kunyar ba, tsofai-tsofai da kai kayi wani wai aure, auren ma ba da babbar mace ba ko wata bazawara, yarinya mai k'ananun shekaru, ko ni dake d'ansa wannan yarinyar ta min kad'an na aureta wallahi bare kuma shi."
Wani wawan tsaki yayi alamun dai abun ya dameshi sosai, banda dariya ba abinda Hadiza keyi kafin tace "Yaron kirki kenan, amma me yasa kake ganin ta maka kad'an?"
Sam babu alamar wasa ko kunya yace "Saboda ba zata iya d'aukata ba, zata iya mutuwa tun kafin aje ko ina, sannan ni banga albarkatun dake jikinta ba wanda zasu iya d'ebewa mutum kewa."
Murje ido Hadiza tayi ta nuna abun bai wani dameta ba dan tasan halin katob'aran yaronta tace "To dama wacece zata iya da kai yarona? Ai sai yar baiwa, amma fa duk da haka ita yarinyar ta dace da mahaifinku, tunda kaga kai sabon jini ne ka mata yawa, shi kuma an kwana biyu zai iya tafiya da ita yanda ya dace."
Cike da jin an fasa mishi kai yayi wani shak'iyin murmushi yace "Hmm; shi ma fa da sauranshi, dan yanzu haka zai iya samo mana cikakken k'ane."
Kafin tayi magana Hamna ta fito daga wanka, har tayi alwala bakin panpo ta basu sake magana ba, saida ta zo daf dashi zata wuce ta gabanshi dan hanyar da zata iya sadaka da d'akin ce kawai yace "Tanti ai duk wacce na kwanta da ita na tashi ita ma kuma ta mik'e da k'afafunta, to wannan ita ce daidai dani saboda ni jaruma nake so ba raguwa ba."
Da k'arfi Hamna ta kalleshi amma kash kamar ma baisan da tsayuwarta a wurin ba, cikin murmushi Hadiza tace "Zaka sameta mai jarumta yaro na, zanyi k'ok'arin ganin haka ta faru ko saboda jin dad'in ka."
Juyawa tayi ta kalli mahaifiyar tasu dake ta harkar gabanta, sake juyowa tayi ta kalle shi tayi k'wafa ta wuce, zata shiga ciki taji ya sake cewa"Kankana."
Cak ta tsaya ta juyo tana aika mishi wani mugun kallo, kallonta yayi ya gyara zama tare da shafar gemunshi yana dariyar iskanci ya kashe mata ido d'aya yace "...
*Alhamdulillah Allah*👏
09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*