Sashe 3
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Marin da Maryama ta d'auke ta dashi yasa yarinyar fad'uwa k'asa, wani daga cikin masu zama a k'ofar gidan ne ya kama Huda ya d'auke ta yana rarrashi.
Iklima dake amsa wayar Junaid shi kuma a daidai lokacin ya k'araso k'ofar gidan, cikin rashin sani tace "Mari ai tun rana rabona da ita dana barota gida, izuwa yanzu kuma nasan ta yada zango a wani wurin."
Daga inda yake ya hango fitowarta sai Maryama dake bayanta, daga cikin wayar yayi murmushi yace "...
*Allah ka mana kyakyawan k'arshe.*👏
18/05/2020 à 13:46 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
_Bismillahir rahamanir rahim_
_2_
Daga cikin wayar yayi murmushi yace "Karki damu ma naga hasken idaniyar tawa."
Da sauri ta d'auke wayar daga kunne ta juya hagu bata ganshi, tana juyawa dama ta hangoshi yana fitowa daga motar, a hankali ta fara takawa wajen shi sai Maryama dake biye da ita a baya wacce bata san meke faruwa ba, saida taga Iklima ta tsaya wajenshi kad'ai ta fahimci mayenta ne ya sake dawowa, tsaki tayi ta tafi a harzuk'e zata wucesu kamar bata gansu ba ma, da sauri ya tare gabanta da gudu gudu, kallon juna sukayi kafin tace "Malam matsa min a hanya ko."
Kai ya girgiza duk yayi kalar tausayi yace "Ba zan iya ba Maryama."
Tab'e baki tayi tace "To saika zauna kayi gadin wurin ko, ai shi zaka iya na sani dan kamar kaine ka yankewa wahala cibiya lokacin da ta zo duniya."
Murmushi yayi dan kalaman da suka fi wannan ma ya jisu a bakinta, zata rab'a ta wuceshi ya sake tare gabanta yace "Dan Allah Maryama ki saurare ni, wai me ya sa har yanzu idonki sun kasa gane miki masoyinki na gaskiya ne? Maryama me ya sa ba zaki yarda da soyayyar da nake miki ba?"
Da k'arfi tace "Saboda duk maza halinku d'aya ne, kana son samun soyayyata ne saboda kawai kana son jikina, kuma na fad'a maka ni yanzu a ruwa nake, karuwa ce ni, ba buk'atar saika yaudareni kafin ka samu jikina, 2000f cfa (jaka biyu) kad'ai ka bani zan iya kwana tare da kai, saboda ni k'aramar karuwa ce da aka cewa *je ki kya gani*, abinci kawai nake nema da zan ciyar da kaina da kuma 'yata, tunda muma halitta ce ba zamu iya rayuwa babu abinci ba, amma kai ka tsaya sai wahalar da kanka kane kana b'ata min lokacin da rera min wani banzan wak'anka wai kana so na, mtssss."
Tunda ta fara magana ya saki baki yana kallon nata k'aramin bakin, har k'asan zuciyarshi tana birgeshi, yana son kallon kyakyawar fuskarta mai d'auke da tsagu har hud'u, wanda kowane kunci ya samu bibbiyu, amma ta kasa fahimtarshi har yanzu, wani murmushi yayi mai kama da ciwo yace "Yanzu akan jaka biyu kad'ai Maryama kike wofantar da kanki ga mazan da basu san ciwon kansu ba? Maryama akan kud'in da ba zasu iya siya miki ko zanin atamfa ba kike kwanciya da duk d'a namijin daya miki magana? Maryama taya zaki illatar da kanki da gangan alhalin kinsan ba kya da kud'in warakar matsalarki ba?"
Hannayenshi yasa aljihu ya lalaba ya fito da duka kud'in dake cikin ak'alla sun ba jaka d'ari biyu baya ya janyo hannunta ya damk'a mata kud'in a hannu kamar zaiyi kuka yace "Karb'i wannan kiyi duk buk'atunki iya na yau kawai, ni kuma na miki alk'awari kowace safiya zan kawo miki adadin wannan kud'in dan biyan buk'atar ki kawai data 'yarki, amma ki min alk'awarin babu ke babu sake kula wani namijin, ki bani tabbacin zaki kula min da kanki za kuma tsare min mutumcinki, dan Allah Maryama."
A hankali ta raba hannunta da nashi ta sakar masa kud'in a hannunsa tana kallon cikin idonshi tace " Bana buk'atar taimako daga wajen kowa, zanyi aiki da jikina wajen samo mana halak d'in da zamu ci, amma bana son kud'in ka, kad'an d'in da nake samu sunfi min masu yawan da zasu fito a hannun kowane d'a namiji."
"D'a namiji! D'a namiji! Maryama kullum maganarki kenan d'a namiji, wai wace irin ta'sa namiji yayi miki haka da har kika mana kud'in goro haka? Ki fad'a min ni kuma zan tsaya tsayin daka wajen ganin na goge waccen bak'in fantin da waccen mutumin yayi mana, sannan ki bar tunanin halak kike ci ke da yarki, kud'i ne da kika samu ta hanyar sab'awa ubangiji."
Kallon idonshi tayi wanda suka cicciko da hawaye tayi wani murmushi tace "Ba zaka tab'a iya goge wannan bak'in fantin ba, kamar yanda ba zaka iya dawo min da mahaifina dana rasa ba a dalilin wautar d'a namiji irinka, haka kuma ba zaka tab'a sawa mahaifiyata ta kalli idona ba bare harta min magana irin ta uwa da d'iya, dan haka dan Allah Junaid ka rabu dani nayi rayuwata, ka barni na k'arasa k'azamar rayuwa ta a haka ba tare daka tuna min da baya ba, ina farin ciki da hakan."
Murmushi ya mata yace "Magana kawai kikayi akan baya, amma gashi har na iya hango triste (damuwa) d'in da kike ciki, Maryama tu es en colère (kina cikin hushi), kamar fansa ce kike son d'auka ko kuma dai hushi ne ke sakaki abinda kikeyi."
Cikin k'ok'arin b'oye damuwarta tace "Laise moi en paix (ka bani lafiya)."
Wucewa tayi yabi bayanta da kallo, Iklima ce ta zo wucewa ta gabanshi ya bata kud'in nan yace "Dan Allah Iklima ki rik'e wannan kud'in kuyi wani anfanin dashi, sannan ki sanar da Maryama irin son da nake mata, wallahi ko misk'ala zarra bana da niyyar cutar da ita, aurenta nake so nayi, yau d'in nan har nayi magana da magabata na, kuma na samu amincewar kowa, ita kad'ai ta rage min na samu ta ta amincewar, na rok'e ki Iklima ki taimaka min na shawo kanta."
Da mamaki ta kalleshi tace "Kana nufin ka sanar a gidanku zaka aure ta?"
Cike da tabbatarwa yace "Na sanar mana."
"Kuma sun amince ka ce?"
"Sosai ma, wallahi da gaske nake Iklima."
Ajiyar zuciya ta sauke tace "Kuma ka fad'a musu irin matar da kake son aure?"
"Na fad'a musu Iklima, amma ban fad'a musu tana da 'ya ba, abu mai mahimmanci su san wacece zan aura."
Zata wuce yace "Kud'in fa?"
Juyowa tayi tace "Ka barshi kawai mun gode, idan na karb'a zamu samu matsala da Mari ne."
Wucewa tayi shi kam yabi bayansu da addu'ar shiriya, cikin sanyin jiki kamar kullum ya shiga motarshi ya kamo hanyar gida dan babu abinda zai tsinta a wajen.
➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️
Su Hamna yan mata sune a falon sama tare da yara ta kunna wak'a a wayarta sai rawa take yaran na biyarta a baya, Amna na zaune tana kallonsu tana dariya, sai Umminsu Ammar da ita ma take kallonsu tana dariyar tare da mahaifiyar Junaid, a gefe ma k'anwar Junaid ce *Jamila* duk da ba ita ke bi mishi ba, amma ita ce daidai su ma'ana warin haihuwa, dan yayarta *Umaima* bata cika son hayaniya ba itama, tana da tsatsauran ra'ayi, ita d'in ce wacce suka zama k'awaye da ita suna ta kallonsu, wannan hayaniyar ce tasa Ammar daya dawo falon ya zauna yana danna wayarshi yayi tsaki yafi dubu, in dai yace yaje yanzu dan yayi musu magana Ummi za tace ai zai takura ma yaranta ne, kuma yana da tabbacin in yaje sai ranshi ya sake b'aci saboda *kankana* *(sunan daya sakawa Hamna kenan saboda soyayyarta da kankana*😂), su kam basu san tsiyar da yake ba sai rawarsu suke kwasa, wannan dum-dum d'in da wajen ke amsawa yasa yake jin kamar benen zai fad'o mishi a kai, wani wawan tsaki ya sake ja yace "Wannan yarinyar wallahi saina karya mata k'afa ta yanda gobe ba zata iya rawar ba ma, ayi yarinya kamar dujal ne ya haifeta, mtssss."
Wasu lambobi ya danna saiga lambar Amna ta bayyana a wayar tashi, kira ya aika mata da shi ta d'auka cikr da nutsuwa da fad'uwar gaba dan ita har ga Allah tana tsoronshi, duk da akwai banbanci tsakanin Hamna da Amna mai yawa, domin kuwa Hamna na da tsoron k'ananun dabbobi irun su k'adangare, kyankyaso, tsaka dacdai sauransu, Amna kuma bata tsoron wannan halittu kamar yanda take tsoron Ammar, Hamna kuma bata da zuciya da sanin ciwon kai, dan duk maganar da zaka fad'a mata komai zafinta saira karkad'e tace ko a kwalar rigarta, shiyasa duk maganganun da Ammar ke fad'a mata bata jin zafi, sai dai kuma akwai yab'a magana ita ma, dan tsoron da Amna ke masa ita bata mishi, idan taga ta shiga hannunshi kad'ai take tsorata da razana, sab'anin Amna kuma da magana ke mata mugun zafi, tana da zuciya da hushi, a tak'aice ma dai ita masifaffiyar amma fa ga wanda ya tab'a ta, idan kuma ka ganta zaka d'auka ko hannu ka saka mata a baki ba zata ciza ba, amma idan tana fad'a ko tayi zuciya to babu kyau, cikin sanyin murya ta amsa da "Na'am yaya Ammar."
Sai kace a gabanshi take saboda yanda ya wani sake had'e rai murya k'asan mak'oshi yace "Ki fad'awa yarinyar nan ta kashe mana kid'an nan, idan kuma na samesu a nan ran uban kowa saiya b'ace."
Yana fad'a ya kashe kiran tare da ci gaba da abinda yake, Amna kuma kallon wayar tayi kafin ta kalli Hamna tace "To shakira ya isa haka ko tunda *boss* yace a kashe wak'ar nan, da alama kuna damunsa ne."
Kallonta Hamna tayi masha Allah kam kyakyawa ne ajin farko, suna da diri da k'ira gwanin ban sha'awa, amma duk da haka Hamna tafi haske sosai da tsayi kad'an, tab'e baki tayi tace "Shine ya kiraki kenan?"
Da ido kawai ta mata alamar eh, ci gaba tayi da rawarta tace "Ki kira ki fad'a masa bai isa ya katse mana jin dad'in mu ba, dan haka yanzu muka fara."
Iklima dake amsa wayar Junaid shi kuma a daidai lokacin ya k'araso k'ofar gidan, cikin rashin sani tace "Mari ai tun rana rabona da ita dana barota gida, izuwa yanzu kuma nasan ta yada zango a wani wurin."
Daga inda yake ya hango fitowarta sai Maryama dake bayanta, daga cikin wayar yayi murmushi yace "...
*Allah ka mana kyakyawan k'arshe.*👏
18/05/2020 à 13:46 - Ummulkhairi: 👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*BADAK'ALA*
👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨👩❤️👨
*Labarin Gaske*
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _BA SO BANE_
*3* _D'AUKAR FANSA_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_
*6* _JIHADI_
*7* _ITACE K'ADDARARMU_
*8* _K'ANGIN RAYUWA_
*9* _MAATA_
*10* _KAWUNA NE_
*11* _KALLON KITSE_
*12* _AURE_
*13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._
*14* _BADAK'ALA..._
*SADAUKARWA GA*
👨👩👧👦 _*AHALI NA*_👨👩👧👦
_Bismillahir rahamanir rahim_
_2_
Daga cikin wayar yayi murmushi yace "Karki damu ma naga hasken idaniyar tawa."
Da sauri ta d'auke wayar daga kunne ta juya hagu bata ganshi, tana juyawa dama ta hangoshi yana fitowa daga motar, a hankali ta fara takawa wajen shi sai Maryama dake biye da ita a baya wacce bata san meke faruwa ba, saida taga Iklima ta tsaya wajenshi kad'ai ta fahimci mayenta ne ya sake dawowa, tsaki tayi ta tafi a harzuk'e zata wucesu kamar bata gansu ba ma, da sauri ya tare gabanta da gudu gudu, kallon juna sukayi kafin tace "Malam matsa min a hanya ko."
Kai ya girgiza duk yayi kalar tausayi yace "Ba zan iya ba Maryama."
Tab'e baki tayi tace "To saika zauna kayi gadin wurin ko, ai shi zaka iya na sani dan kamar kaine ka yankewa wahala cibiya lokacin da ta zo duniya."
Murmushi yayi dan kalaman da suka fi wannan ma ya jisu a bakinta, zata rab'a ta wuceshi ya sake tare gabanta yace "Dan Allah Maryama ki saurare ni, wai me ya sa har yanzu idonki sun kasa gane miki masoyinki na gaskiya ne? Maryama me ya sa ba zaki yarda da soyayyar da nake miki ba?"
Da k'arfi tace "Saboda duk maza halinku d'aya ne, kana son samun soyayyata ne saboda kawai kana son jikina, kuma na fad'a maka ni yanzu a ruwa nake, karuwa ce ni, ba buk'atar saika yaudareni kafin ka samu jikina, 2000f cfa (jaka biyu) kad'ai ka bani zan iya kwana tare da kai, saboda ni k'aramar karuwa ce da aka cewa *je ki kya gani*, abinci kawai nake nema da zan ciyar da kaina da kuma 'yata, tunda muma halitta ce ba zamu iya rayuwa babu abinci ba, amma kai ka tsaya sai wahalar da kanka kane kana b'ata min lokacin da rera min wani banzan wak'anka wai kana so na, mtssss."
Tunda ta fara magana ya saki baki yana kallon nata k'aramin bakin, har k'asan zuciyarshi tana birgeshi, yana son kallon kyakyawar fuskarta mai d'auke da tsagu har hud'u, wanda kowane kunci ya samu bibbiyu, amma ta kasa fahimtarshi har yanzu, wani murmushi yayi mai kama da ciwo yace "Yanzu akan jaka biyu kad'ai Maryama kike wofantar da kanki ga mazan da basu san ciwon kansu ba? Maryama akan kud'in da ba zasu iya siya miki ko zanin atamfa ba kike kwanciya da duk d'a namijin daya miki magana? Maryama taya zaki illatar da kanki da gangan alhalin kinsan ba kya da kud'in warakar matsalarki ba?"
Hannayenshi yasa aljihu ya lalaba ya fito da duka kud'in dake cikin ak'alla sun ba jaka d'ari biyu baya ya janyo hannunta ya damk'a mata kud'in a hannu kamar zaiyi kuka yace "Karb'i wannan kiyi duk buk'atunki iya na yau kawai, ni kuma na miki alk'awari kowace safiya zan kawo miki adadin wannan kud'in dan biyan buk'atar ki kawai data 'yarki, amma ki min alk'awarin babu ke babu sake kula wani namijin, ki bani tabbacin zaki kula min da kanki za kuma tsare min mutumcinki, dan Allah Maryama."
A hankali ta raba hannunta da nashi ta sakar masa kud'in a hannunsa tana kallon cikin idonshi tace " Bana buk'atar taimako daga wajen kowa, zanyi aiki da jikina wajen samo mana halak d'in da zamu ci, amma bana son kud'in ka, kad'an d'in da nake samu sunfi min masu yawan da zasu fito a hannun kowane d'a namiji."
"D'a namiji! D'a namiji! Maryama kullum maganarki kenan d'a namiji, wai wace irin ta'sa namiji yayi miki haka da har kika mana kud'in goro haka? Ki fad'a min ni kuma zan tsaya tsayin daka wajen ganin na goge waccen bak'in fantin da waccen mutumin yayi mana, sannan ki bar tunanin halak kike ci ke da yarki, kud'i ne da kika samu ta hanyar sab'awa ubangiji."
Kallon idonshi tayi wanda suka cicciko da hawaye tayi wani murmushi tace "Ba zaka tab'a iya goge wannan bak'in fantin ba, kamar yanda ba zaka iya dawo min da mahaifina dana rasa ba a dalilin wautar d'a namiji irinka, haka kuma ba zaka tab'a sawa mahaifiyata ta kalli idona ba bare harta min magana irin ta uwa da d'iya, dan haka dan Allah Junaid ka rabu dani nayi rayuwata, ka barni na k'arasa k'azamar rayuwa ta a haka ba tare daka tuna min da baya ba, ina farin ciki da hakan."
Murmushi ya mata yace "Magana kawai kikayi akan baya, amma gashi har na iya hango triste (damuwa) d'in da kike ciki, Maryama tu es en colère (kina cikin hushi), kamar fansa ce kike son d'auka ko kuma dai hushi ne ke sakaki abinda kikeyi."
Cikin k'ok'arin b'oye damuwarta tace "Laise moi en paix (ka bani lafiya)."
Wucewa tayi yabi bayanta da kallo, Iklima ce ta zo wucewa ta gabanshi ya bata kud'in nan yace "Dan Allah Iklima ki rik'e wannan kud'in kuyi wani anfanin dashi, sannan ki sanar da Maryama irin son da nake mata, wallahi ko misk'ala zarra bana da niyyar cutar da ita, aurenta nake so nayi, yau d'in nan har nayi magana da magabata na, kuma na samu amincewar kowa, ita kad'ai ta rage min na samu ta ta amincewar, na rok'e ki Iklima ki taimaka min na shawo kanta."
Da mamaki ta kalleshi tace "Kana nufin ka sanar a gidanku zaka aure ta?"
Cike da tabbatarwa yace "Na sanar mana."
"Kuma sun amince ka ce?"
"Sosai ma, wallahi da gaske nake Iklima."
Ajiyar zuciya ta sauke tace "Kuma ka fad'a musu irin matar da kake son aure?"
"Na fad'a musu Iklima, amma ban fad'a musu tana da 'ya ba, abu mai mahimmanci su san wacece zan aura."
Zata wuce yace "Kud'in fa?"
Juyowa tayi tace "Ka barshi kawai mun gode, idan na karb'a zamu samu matsala da Mari ne."
Wucewa tayi shi kam yabi bayansu da addu'ar shiriya, cikin sanyin jiki kamar kullum ya shiga motarshi ya kamo hanyar gida dan babu abinda zai tsinta a wajen.
➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️
Su Hamna yan mata sune a falon sama tare da yara ta kunna wak'a a wayarta sai rawa take yaran na biyarta a baya, Amna na zaune tana kallonsu tana dariya, sai Umminsu Ammar da ita ma take kallonsu tana dariyar tare da mahaifiyar Junaid, a gefe ma k'anwar Junaid ce *Jamila* duk da ba ita ke bi mishi ba, amma ita ce daidai su ma'ana warin haihuwa, dan yayarta *Umaima* bata cika son hayaniya ba itama, tana da tsatsauran ra'ayi, ita d'in ce wacce suka zama k'awaye da ita suna ta kallonsu, wannan hayaniyar ce tasa Ammar daya dawo falon ya zauna yana danna wayarshi yayi tsaki yafi dubu, in dai yace yaje yanzu dan yayi musu magana Ummi za tace ai zai takura ma yaranta ne, kuma yana da tabbacin in yaje sai ranshi ya sake b'aci saboda *kankana* *(sunan daya sakawa Hamna kenan saboda soyayyarta da kankana*😂), su kam basu san tsiyar da yake ba sai rawarsu suke kwasa, wannan dum-dum d'in da wajen ke amsawa yasa yake jin kamar benen zai fad'o mishi a kai, wani wawan tsaki ya sake ja yace "Wannan yarinyar wallahi saina karya mata k'afa ta yanda gobe ba zata iya rawar ba ma, ayi yarinya kamar dujal ne ya haifeta, mtssss."
Wasu lambobi ya danna saiga lambar Amna ta bayyana a wayar tashi, kira ya aika mata da shi ta d'auka cikr da nutsuwa da fad'uwar gaba dan ita har ga Allah tana tsoronshi, duk da akwai banbanci tsakanin Hamna da Amna mai yawa, domin kuwa Hamna na da tsoron k'ananun dabbobi irun su k'adangare, kyankyaso, tsaka dacdai sauransu, Amna kuma bata tsoron wannan halittu kamar yanda take tsoron Ammar, Hamna kuma bata da zuciya da sanin ciwon kai, dan duk maganar da zaka fad'a mata komai zafinta saira karkad'e tace ko a kwalar rigarta, shiyasa duk maganganun da Ammar ke fad'a mata bata jin zafi, sai dai kuma akwai yab'a magana ita ma, dan tsoron da Amna ke masa ita bata mishi, idan taga ta shiga hannunshi kad'ai take tsorata da razana, sab'anin Amna kuma da magana ke mata mugun zafi, tana da zuciya da hushi, a tak'aice ma dai ita masifaffiyar amma fa ga wanda ya tab'a ta, idan kuma ka ganta zaka d'auka ko hannu ka saka mata a baki ba zata ciza ba, amma idan tana fad'a ko tayi zuciya to babu kyau, cikin sanyin murya ta amsa da "Na'am yaya Ammar."
Sai kace a gabanshi take saboda yanda ya wani sake had'e rai murya k'asan mak'oshi yace "Ki fad'awa yarinyar nan ta kashe mana kid'an nan, idan kuma na samesu a nan ran uban kowa saiya b'ace."
Yana fad'a ya kashe kiran tare da ci gaba da abinda yake, Amna kuma kallon wayar tayi kafin ta kalli Hamna tace "To shakira ya isa haka ko tunda *boss* yace a kashe wak'ar nan, da alama kuna damunsa ne."
Kallonta Hamna tayi masha Allah kam kyakyawa ne ajin farko, suna da diri da k'ira gwanin ban sha'awa, amma duk da haka Hamna tafi haske sosai da tsayi kad'an, tab'e baki tayi tace "Shine ya kiraki kenan?"
Da ido kawai ta mata alamar eh, ci gaba tayi da rawarta tace "Ki kira ki fad'a masa bai isa ya katse mana jin dad'in mu ba, dan haka yanzu muka fara."