Sashe 9
Badak'ala Complète Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri colonel ya kalli agogon dake d'akin yace "Eh to, kuma kaga fa da sauran minti talatin da wani abu, kana ganin zamu iya isa *Gidan roumji* nan da wannan lokacin?"
"Sosai ma, kai dai kawai kuyi harama, duk wanda yasan zaije ya kimtsa da wuri mu d'auki hanya, zan kira Labaran na fad'a mishi shi ma nasan zaije."
"Shikenan." Yana fad'a ya kashe wayar ya shiga neman wata lambar, ana d'auka ya bayar da umarnin motocin d'azu su dawo zai fita shi da iyalinshi, yana gamawa ya shiga wanka cikin k'ank'anin lokaci ya fito ya shirya cikin bla (bleue) d'in shadda amma kanshi ba hula, wayarshi ya figa ya fito ya nufi d'akin Alhaji, ba wani b'ata lokaci ya fad'a mishi abinda ke faruwa tare da cewa su fito yanzu zasu d'auki hanya, lieutenant ma na shigowa wanka ya zarce kai tsaye ya shirya da gaggawa, Alhaji da kanshi ne ya samu Hajia a d'aki yace ta saka gyalenta zasu fita, tayi tambayar ina? Amma bai bata amsa ba, da haka ta fara gunguni tana saka tsadadden gyalenta ta d'auki takalmi masu shegen kyau da jakarsu ta saka, waya a d'aya hannu sai mouchoir (handkiciep) a hannu na goge k'ura da datti, haka ta fito cikin takon izza da k'asaita suka nufi k'ofa, a farfajiyar gidan suka samu mata da yara, lieutenant ne ya kalli matan yace "Mu zafi tafi gidan roumji sai Allah ya mana dawowa, akwai yiwuwar mu kwana acan, dan haka ku kula da gidan da yaran."
Zeinabu ce ta kalli mijinta tace "Wani abun ne ya faru yallab'ai?"
D'an juyawa yayi ya kalli Hajia da sai wani yamutsar fuska take ya kuma kalleta yace "Ba komai, zamu kiraku idan mun isa can, kuma gobe zan turo a d'auke ku."
Muryar Hajia ce ta katse shi tace "Wai meye ya faru a gidan roumjin? Ko dai wani abu ya samu Fatime ne?"
Lieutenant ne yace "Ba komai Hajia, idan munje sai muji meke faruwa."
Cikin had'e fuska tace "Ku tabbatar ba wahalar banza zaku sani nayi ba, dan na tsani na kwashi jiki na je k'azamin wuri kuma ba da wani dalili ba."
Kafin wani yace wani abu Labaran ya shigo a hargitse da sallama, kamar wanda yayi gudu yace "Wai har kun shirya? To zamu iya tafiya kenan?"
Cikin tafiya kamar ta saurayin doki Ammar ya shigo saboda kawu Labaran ya fad'a mishi komai, lieutenant ne ya kalli Ammar fuska ba walwala yace "Ka kira sauran yan uwanka ku same mu acan, ba wai kowa yayi tafiyarshi ba nake nufi, ku tabbatar kanku a had'e kuka tafi, kai kuma ka wuce ka canza wannan kayan na jikinka, kar wanda ya kuskura ya zo mana da shigar turawa a wurin jama'a."
Kamar wanda ciwon kai ya dameshi haka ya juya ya nufi b'angaren su ko magana babu, su kuma suna jin tsayawar motoci suka fito, colonel da kanshi ya bud'ewa su Alhaji suka shiga motarshi mazaunin baya, shi kuma wani soja ya bud'e mishi ya zauna gaba, motar soji ce gaba saita colonel sai kuma wata motar ta soji a baya, sai motar Labaran wacce lieutenant ke ciki suka d'auki hanya, tunda suka samu titi suka bud'e wuta ake gudu sosai saboda suna so su isa da wuri, a lokacin ne Alhaji ya kalli Hajia ya fara da bata hak'uri da kuma tausarta kan haka Allah ya so, nan ya fad'a mata k'anwar ta ce ta rasu, dafe k'irji tayi tace "Fatime, ta rasu?"
Kallon titi tayi tace "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, Fatime lokaci yayi, shikenan yer uwata ta tafi ta barni."
Jimami ta dinga yi amma dai babu kuka ko alamun razana a tare da ita, da haka kuma cikin ikon Allah sai gasu gidan roumji cikin minti ashirin da bakwai, ko da suka iso anata shirya shiryen kawar da ita, nan Hajia ta shiga cikin ciki mazan kuma suka shigar da mitocisu cikin layin masu rakiyarta gidanta na gaskiya.
Ko da Hajia ta shiga gidan bata gaisa da kowa dake waje ba tayi cikin d'aki cikin jagorar autar margayiya duk da kana ganinta zaka san tasha kuka, tana shiga d'akin ganin mutane ga zahi yasa ta wani had'e fuska tasa jelar gyalenta ta fara firfita, autar Fatimen ce tace "Hajia ku shigo nan ciki."
Bayanta ta bi har suka shiga d'akin margayiya, kan gado ta zauna inda autar ta juyo mata da pankar dake aiki, juyawa tayi zata fita Hajia tace " *Sayyada*."
Juyowa tayi ta amsa da "Na'am Hajia."
Cikin gatsina fuska tace "Ki bud'e min tagar nan." Ta fad'a tana nuna mata tagar dake gefe da yatsa, da sauri ta bud'e mata sannan ta juya ta fita, kafin ta shigo kuma mutanen da suka shigo gaishe da Hajia da yi mata ta'aziya basu da adadi, duk da ita bata kula su ba amma dayake a dangin kaf babu wanda Allah ya hore ma abun duniya da matsayi da iko kamar ita, shiyasa suke girmamata suma a dolensu, har yaran margayiya su ne da kansu suka shigo akayi wa juna jaje, suma mazan suna dawowa daga bisa suka shigo aka k'ara jajantawa da bawa juna hak'uri, saida mutanen suka tsagaita Sayyada ta shigo da karap (jug) mai kyau da kofi ta zubawa Hajia gumbar da aka had'a mai sanyi, tana mik'a mata ta girgiza kai tace "Um um bana sha."
Duk da ba gari d'aya suke ba amma Sayyada tasan ta farin sani, dan haka bata damu ba ta juya zata fita da shi sai kuma tace "Kinga, idan kin fita..." Sai kuma ta kalli wayarta tace "Jeki ma ya isa."
Fita tayi inda ita kuma ta d'auki wayarta ta dannawa colonel waya dake zaune k'ofar gida, yana ganin lambar Hajia saida gabanshi ya fad'i saboda tunanin abinda za tace masa yayi, cikin sauri ya d'auka ya aza saman kunne tare da fad'in "Assalama alaikum Hajia."
Cike da iko da nuna ita ce gaba dashi tace "Ruwa mai sanyi da lemun da kasan ina sha nake so, ba kuma wani nake buk'atar ka aika ba, kai da kanka zaka je ka samo sannan ka kawo min, ina d'akin Fatime."
Tana gama fad'a ta datse kiran, d'auke wayar yayi a kunne ya kalli lieutenant dake kusanshi mutane na ta kallonsu abun birgewa saboda ganinsu iri d'aya sak, yunkurawa yayi zai tashi lieutenant yace "Ina zuwa kuma? Lafiya dai ko?"
Cikin rad'a yace mishi "Zanje aiken Hajia, yanzu zan dawo."
Kallonshi yayi da kyau yace "Amma ga yaranka nan ka basu mana."
Had'e fuska ya sakeyi ya wuce bai kula shi ba, yaranshi dake gefe suna ganin haka suka matso suna sara mishi, ko kulasu baiyi ba ya saka takalmi zai fara tafiya ya ji suna take masa baya, juyowa yayi rai b'ace yace "Meye kuma na bi na, ku jira ni na dawo to, wannan ba aikin général bane ko aikin k'asa zanje yi, uwata ce ta aike ni, ko dole sai kunga me zanje yi."
Yana fad'a ya wuce kamar zai tashi sama musamman abinka ga tafiyar mai k'arfi, su kam da bayar da hak'uri suka bi bayanshi suna jinjina girma girma ne, duk girmanka da tsiyarka uwa ko uba ko mata sai su juyaka, kai idan ma ka zama lusari har 'ya'yan daka haifa sai su juyaka yanda suke so, da k'yar ya isa shagon daya samu duk abinda take so, da kuma yasan cewa tana son yaour sosai sai kawai ya siyo ita ma, dan k'aramin aikinta ne saiya kawo tace kuma tana son ta, haka colonel ya kinkimo bak'ar ledarshi a hannu ya taho da ita, sabo da kuma sanin kan aiki yasa d'aya daga cikin yaranshi suna ganinshi yayi saurin mik'ewa zai nufi wajenshi, wasu jajayen idanu colonel ya zaro mishi hakan yasa ya k'ame wuri d'aya, cikin gidan ya haura ya shiga ya wuce d'akin, yana zuwa ya sameta zaune ita kad'ai a d'aki kamar mayya, ita ba zata iya shiga mutane ba saboda k'yank'yamin su take tana ganin ta wuce ajinsu, durk'usawa yayi akan tafukan k'afafun shi ya fara bud'e ledar yace "Hajia ruwan zan baku?"
Ba tare data kalleshi ba tace "Umm."
Bud'awa yayi ya bud'e murfin robar ya mik'a mata, karb'a tayi tasa abin goge gogen nan na hannunta ta goge bakin robar sannan tasha, gefe ya aje mata sauran yace "Ga sauran nan Hajia ko zaku buk'ata."
Wani kallo ta masa tace "Hussein yanzu dayawa ka siyo saboda kar anjima nace ina so ka sake wahala? Tafiyar ce ka ke jin wahalarta ko me?"
K'asa yayi da kanshi yace "Ba ko d'aya Hajia, na dai siyo ne ko zaku iya buk'atar su a kowane lokaci."
Cikin b'acin rai tace "To bana so Hussein, ka d'auka ka fitar min da su yanzun nan, idan buk'atar ta tashi zan sake nemanka."
D'aukar ledar yayi yace "Shikenan Hajia, Allah ya huci zuciyarki."
Har ya kusa kaiwa k'ofa tace "Ka ban lemu d'aya."
A hankali ya bud'a ledar ya fito da kwalin lemu ya sunkuya ya aje mata k'asa gefenta, yana d'agowa suka had'a ido ta mishi wani kallo tace "Cewa nayi fa ka bani, shine zaka aje k'asa."
"Yi hak'uri." Ya fad'a yana sake d'auka ya bata ga hannun, amma sai cewa tayi "Aje kawai zan d'auka." Ajewa yayi ya juya ya fita yana addu'a a ranshi Allah ya k'ara musu hak'urin zama da mahaifiyarta su, dan iyaye irin mahaifiyarsu wuyar sha'ani ne da su ba kad'an ba.
Lieutenant ne ya kira Gambo ya sanar da shi, nan fa aka bi duk 'ya'yan margayiya ana bashi yana musu ta'aziya, kafin daga bisani ya sake cewa a mik'a ta'aziyarshi ga kowa dake wuri dan ba lallai ya samu lokaci ya zo ba tunda ya riga da ya bar garin.
*Bayan tafiyarsu*
"Sosai ma, kai dai kawai kuyi harama, duk wanda yasan zaije ya kimtsa da wuri mu d'auki hanya, zan kira Labaran na fad'a mishi shi ma nasan zaije."
"Shikenan." Yana fad'a ya kashe wayar ya shiga neman wata lambar, ana d'auka ya bayar da umarnin motocin d'azu su dawo zai fita shi da iyalinshi, yana gamawa ya shiga wanka cikin k'ank'anin lokaci ya fito ya shirya cikin bla (bleue) d'in shadda amma kanshi ba hula, wayarshi ya figa ya fito ya nufi d'akin Alhaji, ba wani b'ata lokaci ya fad'a mishi abinda ke faruwa tare da cewa su fito yanzu zasu d'auki hanya, lieutenant ma na shigowa wanka ya zarce kai tsaye ya shirya da gaggawa, Alhaji da kanshi ne ya samu Hajia a d'aki yace ta saka gyalenta zasu fita, tayi tambayar ina? Amma bai bata amsa ba, da haka ta fara gunguni tana saka tsadadden gyalenta ta d'auki takalmi masu shegen kyau da jakarsu ta saka, waya a d'aya hannu sai mouchoir (handkiciep) a hannu na goge k'ura da datti, haka ta fito cikin takon izza da k'asaita suka nufi k'ofa, a farfajiyar gidan suka samu mata da yara, lieutenant ne ya kalli matan yace "Mu zafi tafi gidan roumji sai Allah ya mana dawowa, akwai yiwuwar mu kwana acan, dan haka ku kula da gidan da yaran."
Zeinabu ce ta kalli mijinta tace "Wani abun ne ya faru yallab'ai?"
D'an juyawa yayi ya kalli Hajia da sai wani yamutsar fuska take ya kuma kalleta yace "Ba komai, zamu kiraku idan mun isa can, kuma gobe zan turo a d'auke ku."
Muryar Hajia ce ta katse shi tace "Wai meye ya faru a gidan roumjin? Ko dai wani abu ya samu Fatime ne?"
Lieutenant ne yace "Ba komai Hajia, idan munje sai muji meke faruwa."
Cikin had'e fuska tace "Ku tabbatar ba wahalar banza zaku sani nayi ba, dan na tsani na kwashi jiki na je k'azamin wuri kuma ba da wani dalili ba."
Kafin wani yace wani abu Labaran ya shigo a hargitse da sallama, kamar wanda yayi gudu yace "Wai har kun shirya? To zamu iya tafiya kenan?"
Cikin tafiya kamar ta saurayin doki Ammar ya shigo saboda kawu Labaran ya fad'a mishi komai, lieutenant ne ya kalli Ammar fuska ba walwala yace "Ka kira sauran yan uwanka ku same mu acan, ba wai kowa yayi tafiyarshi ba nake nufi, ku tabbatar kanku a had'e kuka tafi, kai kuma ka wuce ka canza wannan kayan na jikinka, kar wanda ya kuskura ya zo mana da shigar turawa a wurin jama'a."
Kamar wanda ciwon kai ya dameshi haka ya juya ya nufi b'angaren su ko magana babu, su kuma suna jin tsayawar motoci suka fito, colonel da kanshi ya bud'ewa su Alhaji suka shiga motarshi mazaunin baya, shi kuma wani soja ya bud'e mishi ya zauna gaba, motar soji ce gaba saita colonel sai kuma wata motar ta soji a baya, sai motar Labaran wacce lieutenant ke ciki suka d'auki hanya, tunda suka samu titi suka bud'e wuta ake gudu sosai saboda suna so su isa da wuri, a lokacin ne Alhaji ya kalli Hajia ya fara da bata hak'uri da kuma tausarta kan haka Allah ya so, nan ya fad'a mata k'anwar ta ce ta rasu, dafe k'irji tayi tace "Fatime, ta rasu?"
Kallon titi tayi tace "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, Fatime lokaci yayi, shikenan yer uwata ta tafi ta barni."
Jimami ta dinga yi amma dai babu kuka ko alamun razana a tare da ita, da haka kuma cikin ikon Allah sai gasu gidan roumji cikin minti ashirin da bakwai, ko da suka iso anata shirya shiryen kawar da ita, nan Hajia ta shiga cikin ciki mazan kuma suka shigar da mitocisu cikin layin masu rakiyarta gidanta na gaskiya.
Ko da Hajia ta shiga gidan bata gaisa da kowa dake waje ba tayi cikin d'aki cikin jagorar autar margayiya duk da kana ganinta zaka san tasha kuka, tana shiga d'akin ganin mutane ga zahi yasa ta wani had'e fuska tasa jelar gyalenta ta fara firfita, autar Fatimen ce tace "Hajia ku shigo nan ciki."
Bayanta ta bi har suka shiga d'akin margayiya, kan gado ta zauna inda autar ta juyo mata da pankar dake aiki, juyawa tayi zata fita Hajia tace " *Sayyada*."
Juyowa tayi ta amsa da "Na'am Hajia."
Cikin gatsina fuska tace "Ki bud'e min tagar nan." Ta fad'a tana nuna mata tagar dake gefe da yatsa, da sauri ta bud'e mata sannan ta juya ta fita, kafin ta shigo kuma mutanen da suka shigo gaishe da Hajia da yi mata ta'aziya basu da adadi, duk da ita bata kula su ba amma dayake a dangin kaf babu wanda Allah ya hore ma abun duniya da matsayi da iko kamar ita, shiyasa suke girmamata suma a dolensu, har yaran margayiya su ne da kansu suka shigo akayi wa juna jaje, suma mazan suna dawowa daga bisa suka shigo aka k'ara jajantawa da bawa juna hak'uri, saida mutanen suka tsagaita Sayyada ta shigo da karap (jug) mai kyau da kofi ta zubawa Hajia gumbar da aka had'a mai sanyi, tana mik'a mata ta girgiza kai tace "Um um bana sha."
Duk da ba gari d'aya suke ba amma Sayyada tasan ta farin sani, dan haka bata damu ba ta juya zata fita da shi sai kuma tace "Kinga, idan kin fita..." Sai kuma ta kalli wayarta tace "Jeki ma ya isa."
Fita tayi inda ita kuma ta d'auki wayarta ta dannawa colonel waya dake zaune k'ofar gida, yana ganin lambar Hajia saida gabanshi ya fad'i saboda tunanin abinda za tace masa yayi, cikin sauri ya d'auka ya aza saman kunne tare da fad'in "Assalama alaikum Hajia."
Cike da iko da nuna ita ce gaba dashi tace "Ruwa mai sanyi da lemun da kasan ina sha nake so, ba kuma wani nake buk'atar ka aika ba, kai da kanka zaka je ka samo sannan ka kawo min, ina d'akin Fatime."
Tana gama fad'a ta datse kiran, d'auke wayar yayi a kunne ya kalli lieutenant dake kusanshi mutane na ta kallonsu abun birgewa saboda ganinsu iri d'aya sak, yunkurawa yayi zai tashi lieutenant yace "Ina zuwa kuma? Lafiya dai ko?"
Cikin rad'a yace mishi "Zanje aiken Hajia, yanzu zan dawo."
Kallonshi yayi da kyau yace "Amma ga yaranka nan ka basu mana."
Had'e fuska ya sakeyi ya wuce bai kula shi ba, yaranshi dake gefe suna ganin haka suka matso suna sara mishi, ko kulasu baiyi ba ya saka takalmi zai fara tafiya ya ji suna take masa baya, juyowa yayi rai b'ace yace "Meye kuma na bi na, ku jira ni na dawo to, wannan ba aikin général bane ko aikin k'asa zanje yi, uwata ce ta aike ni, ko dole sai kunga me zanje yi."
Yana fad'a ya wuce kamar zai tashi sama musamman abinka ga tafiyar mai k'arfi, su kam da bayar da hak'uri suka bi bayanshi suna jinjina girma girma ne, duk girmanka da tsiyarka uwa ko uba ko mata sai su juyaka, kai idan ma ka zama lusari har 'ya'yan daka haifa sai su juyaka yanda suke so, da k'yar ya isa shagon daya samu duk abinda take so, da kuma yasan cewa tana son yaour sosai sai kawai ya siyo ita ma, dan k'aramin aikinta ne saiya kawo tace kuma tana son ta, haka colonel ya kinkimo bak'ar ledarshi a hannu ya taho da ita, sabo da kuma sanin kan aiki yasa d'aya daga cikin yaranshi suna ganinshi yayi saurin mik'ewa zai nufi wajenshi, wasu jajayen idanu colonel ya zaro mishi hakan yasa ya k'ame wuri d'aya, cikin gidan ya haura ya shiga ya wuce d'akin, yana zuwa ya sameta zaune ita kad'ai a d'aki kamar mayya, ita ba zata iya shiga mutane ba saboda k'yank'yamin su take tana ganin ta wuce ajinsu, durk'usawa yayi akan tafukan k'afafun shi ya fara bud'e ledar yace "Hajia ruwan zan baku?"
Ba tare data kalleshi ba tace "Umm."
Bud'awa yayi ya bud'e murfin robar ya mik'a mata, karb'a tayi tasa abin goge gogen nan na hannunta ta goge bakin robar sannan tasha, gefe ya aje mata sauran yace "Ga sauran nan Hajia ko zaku buk'ata."
Wani kallo ta masa tace "Hussein yanzu dayawa ka siyo saboda kar anjima nace ina so ka sake wahala? Tafiyar ce ka ke jin wahalarta ko me?"
K'asa yayi da kanshi yace "Ba ko d'aya Hajia, na dai siyo ne ko zaku iya buk'atar su a kowane lokaci."
Cikin b'acin rai tace "To bana so Hussein, ka d'auka ka fitar min da su yanzun nan, idan buk'atar ta tashi zan sake nemanka."
D'aukar ledar yayi yace "Shikenan Hajia, Allah ya huci zuciyarki."
Har ya kusa kaiwa k'ofa tace "Ka ban lemu d'aya."
A hankali ya bud'a ledar ya fito da kwalin lemu ya sunkuya ya aje mata k'asa gefenta, yana d'agowa suka had'a ido ta mishi wani kallo tace "Cewa nayi fa ka bani, shine zaka aje k'asa."
"Yi hak'uri." Ya fad'a yana sake d'auka ya bata ga hannun, amma sai cewa tayi "Aje kawai zan d'auka." Ajewa yayi ya juya ya fita yana addu'a a ranshi Allah ya k'ara musu hak'urin zama da mahaifiyarta su, dan iyaye irin mahaifiyarsu wuyar sha'ani ne da su ba kad'an ba.
Lieutenant ne ya kira Gambo ya sanar da shi, nan fa aka bi duk 'ya'yan margayiya ana bashi yana musu ta'aziya, kafin daga bisani ya sake cewa a mik'a ta'aziyarshi ga kowa dake wuri dan ba lallai ya samu lokaci ya zo ba tunda ya riga da ya bar garin.
*Bayan tafiyarsu*