Sashe 84
Triplets Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana kokarin fita muryan dad ta dakatar da shi "James where are you going" a sukwane ya juyo ya kalli daddy cikin sauri yace "Please dad where is the man I brought" murmushi daddy yayi kafin ya sanar da James mutumin yana É—akin duba marasa lafiyar su, da sauri James ya nufi wajen dan alhakin kula da mutumin na rataye ne a wuyar sa.
Yaji daÉ—i sosai ganin yadda daddy ya bawa mutumin nan kulawa, har da karin ruwa daddy ya masa, sannan mutumin ya farka, kafar sa da ya karye kuma daddy ya sanya kafar cikin wata na ura na aikin su likitocin.
Karisawa cikin É—akin James yayi, ya zauna a gefen mutumin yana faÉ—in "Sorry" kallon sa mutumin yayi kafin ya É—an É—aga masa kai kawai, "What is your name?" James ya tambayi sunan mutumin, a hankali mutumin yace masa "Musharraf" jinjina kai James yayi kafin yace "are you an Arab from saudia?" GyaÉ—a masa kai mutumin yayi kafin yace "Yes" shiru James yayi kafin ya sake cewa "Are you a Muslim?" Nan ma eh mutumin yace masa "Okey how is your body now" James ya faÉ—a yana kokarin mikewa ya nufar hanyar fita "Alhadulillah" Musharraf ya faÉ—a yana bin James da ido kawai amma shi kaÉ—ai yasan azaban da yake ji.
Ficewa James yayi daga room É—in yana jin daÉ—i da mutumin bai mutu ba, a palo ya isko daddy, da fara'a ya yiwa daddy godiya, shima daddy ba karamin daÉ—i yaji ba, dama kuma ya kula da mutumin ne dan James yaji daÉ—i, yana son yaga yaran sa suna nuna masa soyayya kamar yadda yake son su amma basa hakan sai dai tsawa da faÉ—a, shi yasa yanzu yake kokarin yin duk abun da suke so dan ya jawo su jikin sa.
Wannan kenan ku koma Nigeria muga meke faruwa
💞NIGERIA💞
💞KATSINA💞
kallon Sadiq tayi idon ta a bushe, dan yanzu gaba ɗaya ta dai na jin kuka zuciyar ta ya bushe, cikin sauri tace "Sadiq ka nemomin masu sayan gidan nan" sannan ta dawo da kallon ta kan gwaggo dake ta faman kuka tace "Gwaggo bamu bukatar mu fitar da Mum waje kuɗin aiki kawai zamu nema mu wuce babban asibiti, na san dai kuɗin gidan nan zai isa ai mata aiki, daman kuɗin jirgin fita wajen shi ne mai tsada, dan haka a sayar da gidan nan a mata magani daga baya zamu san abun yi bayan ta samu lafiya" ta kai karshen maganar tare da miƙewa ta nufi cikin ɗaki.
Jim kaÉ—an ta fito sanye da abaya a jikin ta tana faÉ—in "Gwaggo ki koma hospital ni da Sadiq zamu nemo mai sayan gidan" kasa magana gwaggo tayi dan ta jinjinawa Jehan wannan shine dalilin da yasa a kace ilimi na da amfani yau gashi ilimin Jehan ya taimaka musu, dan kwata kwata bata kawo zancen sai da gida ko kuma karsu fita waje da mum ba sai gashi Jehan ta kawo musu mafita.
Jiki ba kwari gwaggo ta miƙe ta wuce hospital wajen mum, su kuma Jehan da Sadiq suka wuce nemam dillalai.
Babban tashin hankali shine duk wanda su Jehan suka kira dan ya sayi gidan idan ya fahimci kuɗi suke buƙata ruwa a jallo, sai yayiwa gidan kuɗin wulakanci, a wannan karon ba karamin tashin hankali Jehan ta shiga ba, dan abun da take tunani shine mafitar su shima yana neman ya gagara, ga mum kuma kwance rai a hannun Allah kowani lokaci daga yanzu tana iya mutuwa, dan da gaggawa ake buƙatar a mata aiki saboda ciwon yaci jikin ta sosai, dan likitan yace ciwon ya jima a zuciyar ta tun bata kai haka ba, cikin watan nan ne kuma ciwon ya kara tsanan ta saboda tashin hankali da ta shiga na rasuwar daddy da kuma ɓatan Rimsha.
Kamar zararriya haka Jehan ta dawo lokaci guda ta fita hayyacin ta rasa mada fa.
Da kyar suka samu wani ya sai gidan 2 million haka suka sallama masa ya zuba musu kuÉ—in a account É—in mum, haka Jehan taje ta ciro 1.5m misalin karfe 5 na yamma, duk wannan yawon da suke tare da Sadiq suke, haka suka shiga a daidaita sahu suka kama hanyar asibiti dan taje ta É—auki mum su wuce babban hospital, tana rungume da jakar kuÉ—in tana tunanin halin da suke ciki.
A kan hanyar su ta zuwa asibitin ne suka samu accident da wata mota, cikin kwata Jehan ta faÉ—a yayin da shi kuma Sadiq ya faÉ—i can gefen titi, saboda juyin da a daidaita sahun tayi da su, shi ne ta watsar da su, kan kace me jama'a sun taru sai salati suke yayin da shima mai motar da sukayi accident É—in da shi ya sume sakamakon buga kan sa da glass É—in marfin motar da yayi.
Allah ya kiyaye Jehan da Sadiq basu ji ciwo sosai ba, a sukwane Jehan ta miƙe bata damu da kwatar dake jikin taba, ita dai kawai burin ta mum ɗin ta tafita daga haɗari ta samu lafiya.
Kai tsaye bakin hanya ta koma tana neman wani mai a daidaita sahu dan su wuce asibiti, ta ruÉ—e ta manta da jakar kuÉ—in ma, haka Sadiq yazo ya same ta, suka É—an kara gaba da in da sukayi accident É—in suka samu wani abun hawan, zasu hau kenan Sadiq yace mata "Jehan ina kuÉ—in kuma" a sukwane ta juyo, tana faÉ—in "Yana cikin wannan abun da muka hau É—in" a guje Sadiq ya juya ya koma, da sauri ta bi bayan sa.
Ko da suka zo wajen babu jakar, tsab suka duba cikin mashin É—in duk da cewa mashin É—in ma ya faÉ—i dan sai da sukayi juyi biyu kafin mashin É—in ya faÉ—i.
Tsab suka duba cikim mashin ɗin babu komai, a razane Sadiq ya ɗago yana tambayar jama'ar dake wajen, kowa yace masa bai gani ba, mutuwar tsaye Jehan tayi ta kasa motsawa, ta rasa me zatayi, daman ta ciro kuɗin ne a nata tunani dan tana zuwa kawai su wuce babban asibiti ta biya kuɗi kawai a yiwa mum aiki ba sai sun kai gobe ba, a yau zaayiwa mum komai shi yasa tayi sauri ta ciro kuɗin dan kar banki su rufe, gashi a daren nan take son ayiwa mum aiki kuma banki basa aiki da daddare bare tace zata bar kuɗin a bank har sai an buƙata, a takaice dai bata son ɓata lokacin shi yasa ta ciro kuɗin, yanzu gashi wanda ya fisu iya ajiyar kuɗin ya ɗauke,ko in ce mara imani.
Shi ma Sadiq kasa magana yayi dan yasan ba karamin wahala suka shaba, wajen neman kuÉ—in nan, jiki ba kwari ya kariso wajen da Jehan É—in ke tsaye, a hankali yace "Ya Zamuyi" shiru Jehan ta masa dan bata da bakin magana, ganin haka yasa ya riko hannun ta suka hau abin hawan da suka tare suka nufi asibiti, cike da tashin hankali da fargaban abun da zasu gayawa gwaggo.
wannan shi ne ba É—aya kanin biyu, ba gida kuma ba kuÉ—i sannan ba yiwa mum aiki, tashin sense, muje zuwa yanzu wasan zai fara, karki bari a baki labari.
👹Daular mutuwa👹
Rimsha bata sake fita ba tun ranar da abun nan ya faru tsakanin ta da duna, yau kwana biyu kenan.
Yauma kamar kullun suna zaune cikin ɗakin su, sunyi jugum jugum, ita Rimsha sai faman kokarin ɗaure dark black curly hair ta take, gashin nata na da tsantsi sosai yaki ɗauruwa, ita kuma bata son barin sa a sake haka saboda ƙuran dake ɗakin nasu. Cikin sauri Ayla tace "La Meesha muje mu gaishe da baba, kwana biyu ban je ba" juyo da dara daran sleeping eyes nata Rimsha tayi kan Ayla kafin tace "waye kuma baba?" Miƙe wa Ayla tayi tana faɗin "Zo muje ki gan shi" miƙa wa Ayla hannu Rimsha tayi, Ayla tajata ta miƙe tana faɗin "Meesha kin fini quality fa" shiru Rimsha ta mata ba tayi magana ba, mukowa Ayla hannu itama kausar tayi, Ayla ta kama, ta miƙar da ita.
A tare suka jera suka fita a É—akin, suna fita suka hango Mustapha a bakin kofar É—akin sa yana É—aure takalmin sa da igiya, da yar fara'ar su suka karisa wajen sa, suka gaida shi, shima da fara'a ya amsa musu tare da tambayar ina zasu je, Ayla ce ta sanar da shi wajen baba zasu je "to kuje nima ina zuwa bari na É—an gama aiki na" to suka amsa masa da shi kafin su wuce su shiga É—aya daga cikin É—akunan dake wajen, yanzu sosai Mustapha ke sake musu fuska suyi hira, tun ranar da Rimsha ta masa magana, shi kenan sai suka zama É—aya.
Kusa da wani tsohon mutumi suka je suka zauna, tsoho ne sosai, ya manyan ta, gashi fari tas kamar bature ga dogon hanci da dara daran ido, duk da tsufa da wahala da yake ciki, hakan ba zai hana kaga kyan saba, ga gashin kan nan nasa da ya zama farin saboda tsufa kwance luf mai tsantsi har goshin sa, Rimsha ta sha mamakin ganin mutumin nan, ji take kamar ta san shi, lokaci guda taji kaunar tsohon ya shiga ranta.
Ayla ce ta fara gaishe sa, ya amsa cike da kulawa yana tambayar ta kwana biyu ina ta shiga ta dai na zuwa wajen sa suyi hira, nan take bashi labarin su Rimsha, sosai ya jajan ta musu, kafin suma su gaishe shi ya amsa, sai kallon shi Rimsha keyi tana tunanin ina ta san wannan fuskar, amma ina ta kasa tunawa, amma dai koma me tabbas tasan wannan fuskar.
Suna zaune suna hira har Mustapha shima yazo nan suka ci-gaba da hiran su, baba na basu labarai suna dariya, a nan wata yarinya tazo ta same su, suka ci-gaba da hira..
Share fisabilillah ðŸ‘
To masu karatu sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai🤪
💞Star Lady💞
💞TRIPLET'S💞
💞STAR LADY💞
*GargarÉ—i*
_Ban amince wani ko wata yayi amfani da wani sashe na book ɗin nan ba ta kowace siga, ko akaranta mun shi a youtube batare da an nemi izini awurina ba, ko a haɗamun document, ko amin Edit, Idan kunne yaji jiki ya tsira ko da Allah nabar mutun zaibi mun haƙƙina_
WhatsApp me for more information 09162620621
Episode 26
Yaji daÉ—i sosai ganin yadda daddy ya bawa mutumin nan kulawa, har da karin ruwa daddy ya masa, sannan mutumin ya farka, kafar sa da ya karye kuma daddy ya sanya kafar cikin wata na ura na aikin su likitocin.
Karisawa cikin É—akin James yayi, ya zauna a gefen mutumin yana faÉ—in "Sorry" kallon sa mutumin yayi kafin ya É—an É—aga masa kai kawai, "What is your name?" James ya tambayi sunan mutumin, a hankali mutumin yace masa "Musharraf" jinjina kai James yayi kafin yace "are you an Arab from saudia?" GyaÉ—a masa kai mutumin yayi kafin yace "Yes" shiru James yayi kafin ya sake cewa "Are you a Muslim?" Nan ma eh mutumin yace masa "Okey how is your body now" James ya faÉ—a yana kokarin mikewa ya nufar hanyar fita "Alhadulillah" Musharraf ya faÉ—a yana bin James da ido kawai amma shi kaÉ—ai yasan azaban da yake ji.
Ficewa James yayi daga room É—in yana jin daÉ—i da mutumin bai mutu ba, a palo ya isko daddy, da fara'a ya yiwa daddy godiya, shima daddy ba karamin daÉ—i yaji ba, dama kuma ya kula da mutumin ne dan James yaji daÉ—i, yana son yaga yaran sa suna nuna masa soyayya kamar yadda yake son su amma basa hakan sai dai tsawa da faÉ—a, shi yasa yanzu yake kokarin yin duk abun da suke so dan ya jawo su jikin sa.
Wannan kenan ku koma Nigeria muga meke faruwa
💞NIGERIA💞
💞KATSINA💞
kallon Sadiq tayi idon ta a bushe, dan yanzu gaba ɗaya ta dai na jin kuka zuciyar ta ya bushe, cikin sauri tace "Sadiq ka nemomin masu sayan gidan nan" sannan ta dawo da kallon ta kan gwaggo dake ta faman kuka tace "Gwaggo bamu bukatar mu fitar da Mum waje kuɗin aiki kawai zamu nema mu wuce babban asibiti, na san dai kuɗin gidan nan zai isa ai mata aiki, daman kuɗin jirgin fita wajen shi ne mai tsada, dan haka a sayar da gidan nan a mata magani daga baya zamu san abun yi bayan ta samu lafiya" ta kai karshen maganar tare da miƙewa ta nufi cikin ɗaki.
Jim kaÉ—an ta fito sanye da abaya a jikin ta tana faÉ—in "Gwaggo ki koma hospital ni da Sadiq zamu nemo mai sayan gidan" kasa magana gwaggo tayi dan ta jinjinawa Jehan wannan shine dalilin da yasa a kace ilimi na da amfani yau gashi ilimin Jehan ya taimaka musu, dan kwata kwata bata kawo zancen sai da gida ko kuma karsu fita waje da mum ba sai gashi Jehan ta kawo musu mafita.
Jiki ba kwari gwaggo ta miƙe ta wuce hospital wajen mum, su kuma Jehan da Sadiq suka wuce nemam dillalai.
Babban tashin hankali shine duk wanda su Jehan suka kira dan ya sayi gidan idan ya fahimci kuɗi suke buƙata ruwa a jallo, sai yayiwa gidan kuɗin wulakanci, a wannan karon ba karamin tashin hankali Jehan ta shiga ba, dan abun da take tunani shine mafitar su shima yana neman ya gagara, ga mum kuma kwance rai a hannun Allah kowani lokaci daga yanzu tana iya mutuwa, dan da gaggawa ake buƙatar a mata aiki saboda ciwon yaci jikin ta sosai, dan likitan yace ciwon ya jima a zuciyar ta tun bata kai haka ba, cikin watan nan ne kuma ciwon ya kara tsanan ta saboda tashin hankali da ta shiga na rasuwar daddy da kuma ɓatan Rimsha.
Kamar zararriya haka Jehan ta dawo lokaci guda ta fita hayyacin ta rasa mada fa.
Da kyar suka samu wani ya sai gidan 2 million haka suka sallama masa ya zuba musu kuÉ—in a account É—in mum, haka Jehan taje ta ciro 1.5m misalin karfe 5 na yamma, duk wannan yawon da suke tare da Sadiq suke, haka suka shiga a daidaita sahu suka kama hanyar asibiti dan taje ta É—auki mum su wuce babban hospital, tana rungume da jakar kuÉ—in tana tunanin halin da suke ciki.
A kan hanyar su ta zuwa asibitin ne suka samu accident da wata mota, cikin kwata Jehan ta faÉ—a yayin da shi kuma Sadiq ya faÉ—i can gefen titi, saboda juyin da a daidaita sahun tayi da su, shi ne ta watsar da su, kan kace me jama'a sun taru sai salati suke yayin da shima mai motar da sukayi accident É—in da shi ya sume sakamakon buga kan sa da glass É—in marfin motar da yayi.
Allah ya kiyaye Jehan da Sadiq basu ji ciwo sosai ba, a sukwane Jehan ta miƙe bata damu da kwatar dake jikin taba, ita dai kawai burin ta mum ɗin ta tafita daga haɗari ta samu lafiya.
Kai tsaye bakin hanya ta koma tana neman wani mai a daidaita sahu dan su wuce asibiti, ta ruÉ—e ta manta da jakar kuÉ—in ma, haka Sadiq yazo ya same ta, suka É—an kara gaba da in da sukayi accident É—in suka samu wani abun hawan, zasu hau kenan Sadiq yace mata "Jehan ina kuÉ—in kuma" a sukwane ta juyo, tana faÉ—in "Yana cikin wannan abun da muka hau É—in" a guje Sadiq ya juya ya koma, da sauri ta bi bayan sa.
Ko da suka zo wajen babu jakar, tsab suka duba cikin mashin É—in duk da cewa mashin É—in ma ya faÉ—i dan sai da sukayi juyi biyu kafin mashin É—in ya faÉ—i.
Tsab suka duba cikim mashin ɗin babu komai, a razane Sadiq ya ɗago yana tambayar jama'ar dake wajen, kowa yace masa bai gani ba, mutuwar tsaye Jehan tayi ta kasa motsawa, ta rasa me zatayi, daman ta ciro kuɗin ne a nata tunani dan tana zuwa kawai su wuce babban asibiti ta biya kuɗi kawai a yiwa mum aiki ba sai sun kai gobe ba, a yau zaayiwa mum komai shi yasa tayi sauri ta ciro kuɗin dan kar banki su rufe, gashi a daren nan take son ayiwa mum aiki kuma banki basa aiki da daddare bare tace zata bar kuɗin a bank har sai an buƙata, a takaice dai bata son ɓata lokacin shi yasa ta ciro kuɗin, yanzu gashi wanda ya fisu iya ajiyar kuɗin ya ɗauke,ko in ce mara imani.
Shi ma Sadiq kasa magana yayi dan yasan ba karamin wahala suka shaba, wajen neman kuÉ—in nan, jiki ba kwari ya kariso wajen da Jehan É—in ke tsaye, a hankali yace "Ya Zamuyi" shiru Jehan ta masa dan bata da bakin magana, ganin haka yasa ya riko hannun ta suka hau abin hawan da suka tare suka nufi asibiti, cike da tashin hankali da fargaban abun da zasu gayawa gwaggo.
wannan shi ne ba É—aya kanin biyu, ba gida kuma ba kuÉ—i sannan ba yiwa mum aiki, tashin sense, muje zuwa yanzu wasan zai fara, karki bari a baki labari.
👹Daular mutuwa👹
Rimsha bata sake fita ba tun ranar da abun nan ya faru tsakanin ta da duna, yau kwana biyu kenan.
Yauma kamar kullun suna zaune cikin ɗakin su, sunyi jugum jugum, ita Rimsha sai faman kokarin ɗaure dark black curly hair ta take, gashin nata na da tsantsi sosai yaki ɗauruwa, ita kuma bata son barin sa a sake haka saboda ƙuran dake ɗakin nasu. Cikin sauri Ayla tace "La Meesha muje mu gaishe da baba, kwana biyu ban je ba" juyo da dara daran sleeping eyes nata Rimsha tayi kan Ayla kafin tace "waye kuma baba?" Miƙe wa Ayla tayi tana faɗin "Zo muje ki gan shi" miƙa wa Ayla hannu Rimsha tayi, Ayla tajata ta miƙe tana faɗin "Meesha kin fini quality fa" shiru Rimsha ta mata ba tayi magana ba, mukowa Ayla hannu itama kausar tayi, Ayla ta kama, ta miƙar da ita.
A tare suka jera suka fita a É—akin, suna fita suka hango Mustapha a bakin kofar É—akin sa yana É—aure takalmin sa da igiya, da yar fara'ar su suka karisa wajen sa, suka gaida shi, shima da fara'a ya amsa musu tare da tambayar ina zasu je, Ayla ce ta sanar da shi wajen baba zasu je "to kuje nima ina zuwa bari na É—an gama aiki na" to suka amsa masa da shi kafin su wuce su shiga É—aya daga cikin É—akunan dake wajen, yanzu sosai Mustapha ke sake musu fuska suyi hira, tun ranar da Rimsha ta masa magana, shi kenan sai suka zama É—aya.
Kusa da wani tsohon mutumi suka je suka zauna, tsoho ne sosai, ya manyan ta, gashi fari tas kamar bature ga dogon hanci da dara daran ido, duk da tsufa da wahala da yake ciki, hakan ba zai hana kaga kyan saba, ga gashin kan nan nasa da ya zama farin saboda tsufa kwance luf mai tsantsi har goshin sa, Rimsha ta sha mamakin ganin mutumin nan, ji take kamar ta san shi, lokaci guda taji kaunar tsohon ya shiga ranta.
Ayla ce ta fara gaishe sa, ya amsa cike da kulawa yana tambayar ta kwana biyu ina ta shiga ta dai na zuwa wajen sa suyi hira, nan take bashi labarin su Rimsha, sosai ya jajan ta musu, kafin suma su gaishe shi ya amsa, sai kallon shi Rimsha keyi tana tunanin ina ta san wannan fuskar, amma ina ta kasa tunawa, amma dai koma me tabbas tasan wannan fuskar.
Suna zaune suna hira har Mustapha shima yazo nan suka ci-gaba da hiran su, baba na basu labarai suna dariya, a nan wata yarinya tazo ta same su, suka ci-gaba da hira..
Share fisabilillah ðŸ‘
To masu karatu sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai🤪
💞Star Lady💞
💞TRIPLET'S💞
💞STAR LADY💞
*GargarÉ—i*
_Ban amince wani ko wata yayi amfani da wani sashe na book ɗin nan ba ta kowace siga, ko akaranta mun shi a youtube batare da an nemi izini awurina ba, ko a haɗamun document, ko amin Edit, Idan kunne yaji jiki ya tsira ko da Allah nabar mutun zaibi mun haƙƙina_
WhatsApp me for more information 09162620621
Episode 26