← Book details Triplets Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 126

Sashe 26

Triplets Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Ɗan sanda na parking a parking space na school ɗin ya fito ya buɗewa daddy da gwaggo suka fito nan take manya manyan alhazawan dake tsaye a wajen suna jiran fitowar daddy suka kariso cikin murna da fara'a suka fara bashi hannu a kan su gaisa, kasan cewar shine babban bako a wajen hakan yasa director makarantar da sauran malamai suka kariso wajen da sauri dan tarban sa, cikin girmamawa director ya miƙawa daddy hannu yana faɗin "Barka da zuwa gaskiya munji daɗi da amsa gayyatar mu da kayi muna alfahari da hakan" murmushi daddy ya saki har sai da dimple na shi ta lotsa yace "Ai dole nazo ko dan siha ta" ya kai karshen maganar tare da shafa kan Rimsha cool murmushi ta saki har sai da dimple nata ya lotsa siririn open teeth dake tsakanin fafaren hakoran ta ya bayyana hakoranta fafare tas da su kamar gonan audiga, manya manyan Alhazawan dake wajen dukkan su Rimsha ta matikar burge su sosai. Malamar su Rimsha ce ta ƙaraso ta gaida daddy cikin girmamawa ta kama hannun Rimsha tana faɗin "let's go and get ready" a hankali ta lumshe sleeping eyes nata ta sake buɗe wa kafin tace "Bye daddy see you in the Hall" ta kai ƙarshe maganar tana yi masa bye bye da hannunta shima bye bye ɗin ya mata ita dai Jehan tun saukowar su ba ta jira kowa ba ta wuce wajen friends nata,
Director ne yace "sir please let's go in"
Kallon Gwaggo daddy yayi yace "Anty A'isha muje Koh"

a tare suka ranƙaya zuwa cikin katafaren hall ɗin dake cikin School ɗin a nan za'ayi taron ƴan jarida sunzo ɗaukar new gidan TV kala kala gaba ɗaya student na ciki kowa na zaune saman kujera an kawata hall ɗin sosai da kalar makarantar Dark blue da light blue an rubuta Sunan Makarantar da ballons dark blue da light blue idan nace zan tsaya zayyana muku haɗuwar da hall ɗin nan yayi to zamu kwana mu wuni bamu kammala ba kawai ku kawata shi a ran ku, hall ne mai girman gaske an cike sa da kujeru da student suka zazzauna, ta gaba kuma inda aka tanadar na ɗaliban da sukayi graduation ɗine, daga saman staircase wani ya opposite ɗin students ɗin, a ka shirya wasu haɗaɗu kujeru masu kyau sun kawatu iya kawatuwa ga wata doguwar table a gaban kujerun an jera drinks a sama da ruwan faro masu sanyi wadda daga ka gani kasan wajen baki na musamman ne daga tsakiyar kuren a kwai wata haɗaɗiyar kujera golden color an mata kwalliya sosai kamar kujerar sarauta daga gani kasan mutun na musamman a ka tana dawa,

manya manyan alhazawa da sarakuna ne zazzaune saman sauran kujerun da a ka jera layi sai wan nan ɗayan mai kama dana sarakuna shi da na kusa da shi ne babu kowa a kai, saman sa daddyn su Jehan yaje ya zauna ita kuma gwaggo ta zauna a kujerar kusa da na shi, nan take student suka miƙe suka fara kwasan gaisuwa daddy na amsa musu da fara'a a face na sa, duk school nan ba wanda bai san shi ba sai dai in new comer amma student ɗin school ɗin sun san shi dan mutun ne shi mai fara'a da kyauta gashi da son yara duk kuɗin da yake da shi, shi da kan sa yake kawo su Jehan school kuma ya dawo ya ɗauke su dan gani yake kamar idan ya bari driver ya kai su ba zai kula masa da su sosai ba, shi yasa ko abu suke so yake ɗaukan su suje shopping tare da shi komai aikin da yake zai ajiye yazo yayi attended nasu, yana bala'i kaunar su sosai,

Bayan sun gama kwasan gaisuwa ne suka koma suka zauna.
Mike director ya ɗauko ya sanya a saitin bakin sa ya fara magana cikin harshen turanci "Ina mai farincikin zuwan wan nan rana mai albarka Jehan Nawazudden Salman kizo ki buɗe mana taro da Addu'a" shiru hall ɗin yayi, gaba ɗaya manya manyan bakin da suka halakci taron sun zubawa Jehan ido wadda ta taso tana tafiya a nitse, a hankali ta tattaka saman staircase ɗin ta hauro sama taje ta tsaya kusa da director, miƙa mata mike ɗin director yayi ta ansa cikin kyakkyawa turancin ta da zazzakar voice nata mai sanyi da daɗi ta fara da yi musu sallama san nan ta fara jero addu'a "We take refuge with Allah, The Supreme and with His Noble Face, and His eternal authority from the accursed devil In the name of Allah, and prayers and peace be upon the Messenger of Allah O Allah, open the gates of Your mercy for us Amin" ta kai karshen Addu'ar tare da rufewa da Ayatul kursiyyu, sosai jama'a suka yi ta kabbara ciki hadda daddy da gwaggo sosai daddy yaji daɗi, ji yayi kamar ya zuba ruwa a kasa ya sha,

bayan Jehan ta sauka ta koma mazaunin ta ne director yace a shigo da É—aliban da sukayi graduation É—in, a cikin layin suka shigo cikin tsarin suna sanye Cikin graduation gown kalar uniform É—in makarantar daga bayansu kuma malaman sune kowa fuskarsa cikin annashiwa da tsantsar farin ciki, kai tsaye inda aka tanadar domin su suka karasa sannan sukayi Anthem É—in makarantar aka basu iznin zama
Director ne fara kiran graduates É—in É—aya bayan É—aya sukazo su gabatar da kan su san nan suyi jawabi tare da nuna farincikin su sai suyi karatun al Qur'ani mai girma,

ba laifi yaran sun iya kira'a daddy ya kosa a kira Rimsha É—in sa haka ita ma gwaggo ta kosa taji karatun Rimsha, duk yarinyar da tazo a kace ta karanta Al Qur'ani mai girma bata wuce karanta sura daga nasi zuwa amma ko sabbi,

Rimsha itace yarinya ta goma da a ka kira cikin nitsuwa ta taso tana tafiya a nitse ta hauro saman wajen ta ansa mike ɗin da zazzakar voice nata ta fara da bilmillah san nan ta karanta suratul fatiha daddy yaji ba daɗi a tunanin sa a suratul fatiha zata tsaya sai yaji ta sake wata Bismillah ta fara karanta Suratul Baƙara,
shiru hall É—in yayi ba abun da ke tashi sai zazzakar voice É—in Rimsha dake tashi, gaba É—aya kowa ya nitsu tsit suna sauraron baiwar da Allah ya mata farincikin a wajen daddy da gwaggo ba'a magana,

hawaye Rimsha ta fara yi tana karatu ko da tazo In da Allah ke magana a kan itaciyar da ya hana Annabi Adam ci Annabi Adam yaci ta sanadiyar haka Allah ya fito da shi daga aljanna, sau uku tana mai mai ta ayoyin san nan ta ci gaba tana karatu tana kuka, tun muryan ta na fita sosai har ya fara sarkewa saboda kuka da take idan ta tuna girman Allah ta tuna mutuwa kwanciyar kabari gadar siraÉ—i hisabi sai ta kara fashe wa da kuka shi kan sa daddy sai da kwalla ta cika masa ido duk wani mai imani a wajen sai da idon sa ta kawo kwalla dan kukan da Rimsha ke yi tana rero kira'ar nan, masu saurin kuka kam ma tuni sun fara rera nasu kukan cikin harda Jehan,
Chapter 26 · 0% Book details