Sashe 57
Triplets Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana kwance jikin Abba ta jiyo wayar ta na ringing a bedroom na ta, da gudu ta miƙe ta haye sama ta nufi bedroom ɗin, wayar na gab da katsewa ta shigo, hannun ta har rawa yake wajen yin picking call ɗin tare da manna wayar a kunnen ta cike da zumuɗi tace "Bappa ina wuni" daga ɗaya bangaren muryan Jelly ta daki dodon kunnen ta cikin kauɗi tace "Aunty Akila ni ce ba daddy ba" daɗi kamar Akila tayi ihu sai murmushi take bakin ta yaki rufuwa, ta kasa ɓoye murnar ta, cike da kaunar yan uwa ta tace "Jelly na ya kike ina kewar ki sosai yar uwata" a bangaren ita ma Jelly bakin ta ya kasa rufuwa saboda murna da farinciki ji take kamar tayi tsuntsuwa tazo ta kalli Akila, tana matikar son Akila over,
haka suka rinƙa hira Jelly na zuba mata shirme ita kuma tana biye mata, almost 1 hour suka ɗauka suna hira sai murmushin da dariya Akila keyi ji take kamar ta koma gidan su Jelly kawai da zama, sun kasa yin sallama da juna har sai da daddy ya anshe wayar suka gaisa da Akilan san nan ya katse kiran
Yana katsewa Akila ta fara ƙoƙarin neman layin su Umaisha dan su gaisa, sai dai kash a rufe tasamu layin, haka ta hakura ba dan taso ba, tana bala'i kaunar yan uwan ta sosai, rashin samun su Aafia a waya bai mata daɗi ba ko kaɗan amma haka ta hakura ba dan taso ba, ta miƙe jiki ba kwari ta fice ta koma Palo
Ko da ta dawo palon, yaya Imran da Akil duk sun tafi basu a palon sai Ammie da Abba, da suka zubawa Tv ido sosai suna kallon, yanzu sun samu saukin wayan nan dodannin dake zuwa musu kasan cewar su Imran na yawan yi musu karatun al Qur'ani mai girma a gidan, shi yasa tun ranar da suka ɓace basu sake dawowa ba, daman saboda tafiyar su Imran kano ne yasa abubuwan ke zuwa dan ba'a karatu kuma ba'a kunna kira'a, daman Abba da su Imran ke kunnawa, to shi Abba ya dawo ya samu bala'i ne shi yasa bai samu damar karatun ba, dan ita dai Hajiya Umaiya bata wani yin karatu Al Qur'ani sharholiyar ta kawai take, san nan faruwar wan nan abun yasa Hajiya Umaisha ta yi hankali sosai, ta rage wasu abubuwa yanzu duk wani hakkin miji tana kokarin ta sauke sa dan tsoron dodannin, yanzu ta dai na masifa da faɗa ta koma so silent kamar ba ita ba, daman shi kam Abba shiru shiru ne baya shiga har kan kowa abun da ke gaban sa kawai yake, haka suka koma ratuwar farincikin su kamar yadda suka saba.
*ABUJA*
Sosai a ka bawa Rimsha kulawa har sai da suka tabbatar ta dawo dai dai, daddy ya shiga damuwa over ji yake kamar zai yi kuka saboda kaunar da yake wa Rimsha gashi ta jefa kan ta cikin wahala.
Basu bar hospital ba sai da daddy ya tabbatar da tasamu lafiya sosai san nan ya ansa magungu nan ta ya wuce ya suka shiga motar sa suka bar hospital É—in, Rimsha ta samu sauki dan da kafar ta ta taka zuwa wajen motar daddy.
Suna isa gida, suka isko mum gwaggo da Jehan a Palo zaune cikin damuwa ko wani hali Rimsha ke ciki, mum na ganin su ta miƙe tana faɗin "Ya jikin nata dai?" kallon face ɗin Rimsha daddy yayi kafin yace cikin zolaya "GAR ya bamu magani ai" cool murmushi Rimsha ta saki har sai da dimple nata ya lotsa open teeth nata ya bayyana ga hakoran nata a jere tsab sai kyalli suke kamar gonar audiga, hakan ba karamin kyau ya karawa kyakkyawar face nata ba, duk da cewa ta ɗan rame saboda zazzaɓin, sleeping eyes nata sun kara haske sosai sun kara girma saboda yar ramar da tayi. Riƙo hannun ta gwaggo tayi suka haura sama dan taje ta mata wanka ta huta, wucewa daddy yayi ta nufi bedroom na shi yana faɗin "Ina son magana da ke boɗɗi" cikin sauri mun tabi bayan sa ita kuma Jehan tabi su gwaggo.
Zaune bakin gado ta isko sa yayi shiru kamar mai tunani wani abun, "lafiya daddyn Jehan?" Mum ta tambaya dai dai lokacin da take zama a gefen sa, dogon numfashi yaja tare da sauke wa a hankali ya ɗan juyo suna fiskantar juna "Wallahi ba lafiya ba" zaro ido waje mum tayi tana faɗin "Meke faruwa to?" Riko hannun ta daddy yayi ya fara magana cike da damuwa "kwana ki na ta tafiya zaɓe na ta kara gabatowa ni kuma sai kara samun baraza nake daga abokan ha mayya, baraza ta ko ina nake samu abun ya fara affecting ɗina na fara karaya, dan wasu ma ban san daga ina suke min barazanar ba, ina tsoron kada na jefa rayuwar ku a cikin haɗari bana son abun da zai taɓa min ku bana son tashin hankali ku, ina ganin zan hakura da siyasar nan kawai" cikin sauri mum tace "A'a barkama ni ban yarda da ka hakura da siyasa ba, kasan cewar adalin mutun irin ka mai gaskiya a siyasa babban nasara ne ga yan kasa, kana da tausayi kuma zaka taimakawa talakawa, na sani siyasa babban haɗari ne dan ba kowa yake son cigaba al'umma ba, amma jajirtattun mutane ire iren ka masu son tai makon talakawa bai kamata ku rinƙa karaya kuna sarewa haka ba, kama ta yayi ku rinƙa karawa kan ku kwarin gwiwa, na san cewa rayuwa a matsayin mai gaskiya yafi komai wahala a duniyar da muke ciki yanzu, dan dayawa daga cikin mutane sun ajiye gaskiya sun bi karya da ha inci a guje suna son kamawa su runguma, wasu ma har sun kama sun runguma ɗin sun yar da gaskiya, kayi rayuwa ba tare da cutar da wani ko tauye hakkin wasu ba yafi komai wahala a duniyar yanzu, babu mai tai makon ɗan uwan sa, jama'a da dama sun manta lahira sun rungumi duniya hannu bibbiyu, jama'a da dama sun manta cewa wanda ka bayar shi zaka tarar a lahira wanda kuma kaci a nan duniya zaka barshi, dan Allah barkama ka karawa kan ka karfin gwiwa wajen ganin ka tsaya tsayin daka ka ceto mana kasar mu, muna bukatar adalin shugaba irin ka, kasar mu na bukatar jajirtattun maza irin ka, aikin Allah na da wahala, ba'a shiga aljanna a na kwance a gado, duk wanda Allah keso da Rahma to sai ya jarrabe shi da wani abun, to ka ɗauka duk wan nan barazana da abokan hamayya suke maka jarabawa ce daga Allah, kuma ka dage ka ci jarabawar, san nan ka zauna da kowa zuciya ɗaya" duk wan nan hiran da suke cikin harshen turanci suke yin sa,
dogon numfashi yaja tare da sauke nauyayyar ajiyar zuciya kafin yace "Kin san me?" Girgiza masa kai tayi alamar a'a "Meeting da naje ɗazun sai da nayi dana sanin shiga ta siyasa, saboda a fillin Allah wasu daga cikin manya ke min baraza a kan na janye tun yanzu abun ya tsorata ni, shi yasa nake tsoron kar na jefa rayuwar ku cikin haɗari" kwanciya mum tayi a jikin sa cikin sigar soyayya ta fara magana "Barkama ka sani fa kafin mutun yaji daɗi sai ya sha wahala, musamman ma mutun mai zuciyar gaskiya irin naka to fa sai ka daure ka kawar da kan ka daga kan wasu abubuwan idan ba haka ba bazaka taɓa cin ma nasara ba, a zamanin yanzun nan duk wanda yace zai fito fili ya nuna cewa shi gaskiya yake so tofa makiya ba zasu taɓa bari ya kai labari ba sai ya dage da kai wa Allah kukan sa, yanzu dai ka manta da komai ka ci-gaba da gwagwarmayan ka kana addu'a muma zamu taya ka, In Sha Allah ba dai ɗan adam ba, sai Allah ya cika maka burin ka na ganin ka taimaki talakawa kuma ka raya mana kasar mu ta girma kamar sauran manya manyan kasashe na duniya In Sha Allah" ta kai karshen maganar tana riƙo hannun sa, murmushi ya saki har sai da dimple nashi ya lotsa, cike da so da kauna yace "Shi yasa nake son ki matata duk lokacin da na shiga damuwa kin san yadda zaki yi ki kwantar min da hankali, duk wata natsala ta idan na kawo miki, ba za'a fi 10mins ba kike samo mana mafita, Allah ya miki albarka ki taya ni da addu'a In Sha Allah burin mu zai cika bari naje nayi wanka yanzu na fito sai mu ci-gaba da hirar ko?" Gyaɗa masa kai tayi tana faɗin "Amin ya Allah" ta kai karshen maganar tare da tashi daga jikin sa, miƙewa yayi ya nufi toilet ita kuma ta miƙe ta wuce wajen drawer kayan sa ta ciro masa kayan sawa da duk wani abun da zai buƙata ta dawo ta ajiye masa a bakin gado san nan ta haye saman gadon ta kwanta tana tunanin rayuwa.
After some days
*KADUNA*
A yau Akil yazo yin sallama da Umaisha zai koma makaranta, sanye yake da manyan kaya wato wata dakakkiyar yadi navy blue mai bala'i kyau da tsada, É—inkin half jomfa, kayan sun masa kyau, yau ma kamar kullun tsaye yake a kofar gida bai shiga ba, ya bawa gidan baya ya kifa kai da jikin mota kamar dai kullun, ya aiki mai gadi da ya kira masa matar sa, ko da mai gadi yaje Abbi baya nan ya tafi company shi kuma Irfan ya wuce Uk tun kwana biyu da suka wuce, gidan ya rage daga Umaisha sai Aafia, koda mai gadi ya sanar da su sakon Akil sai Umaisha tace "Kaje kace masa Abbi yace ya shigo ba zan kara fita ba" tayi maganar cike da tsoron abun da Akil É—in zai mata sai dai kuma ta sawa ranta ko kashe ta zai yi bazata ki bin umarnin Abbin ta tabi na Akil É—in ba.
haka suka rinƙa hira Jelly na zuba mata shirme ita kuma tana biye mata, almost 1 hour suka ɗauka suna hira sai murmushin da dariya Akila keyi ji take kamar ta koma gidan su Jelly kawai da zama, sun kasa yin sallama da juna har sai da daddy ya anshe wayar suka gaisa da Akilan san nan ya katse kiran
Yana katsewa Akila ta fara ƙoƙarin neman layin su Umaisha dan su gaisa, sai dai kash a rufe tasamu layin, haka ta hakura ba dan taso ba, tana bala'i kaunar yan uwan ta sosai, rashin samun su Aafia a waya bai mata daɗi ba ko kaɗan amma haka ta hakura ba dan taso ba, ta miƙe jiki ba kwari ta fice ta koma Palo
Ko da ta dawo palon, yaya Imran da Akil duk sun tafi basu a palon sai Ammie da Abba, da suka zubawa Tv ido sosai suna kallon, yanzu sun samu saukin wayan nan dodannin dake zuwa musu kasan cewar su Imran na yawan yi musu karatun al Qur'ani mai girma a gidan, shi yasa tun ranar da suka ɓace basu sake dawowa ba, daman saboda tafiyar su Imran kano ne yasa abubuwan ke zuwa dan ba'a karatu kuma ba'a kunna kira'a, daman Abba da su Imran ke kunnawa, to shi Abba ya dawo ya samu bala'i ne shi yasa bai samu damar karatun ba, dan ita dai Hajiya Umaiya bata wani yin karatu Al Qur'ani sharholiyar ta kawai take, san nan faruwar wan nan abun yasa Hajiya Umaisha ta yi hankali sosai, ta rage wasu abubuwa yanzu duk wani hakkin miji tana kokarin ta sauke sa dan tsoron dodannin, yanzu ta dai na masifa da faɗa ta koma so silent kamar ba ita ba, daman shi kam Abba shiru shiru ne baya shiga har kan kowa abun da ke gaban sa kawai yake, haka suka koma ratuwar farincikin su kamar yadda suka saba.
*ABUJA*
Sosai a ka bawa Rimsha kulawa har sai da suka tabbatar ta dawo dai dai, daddy ya shiga damuwa over ji yake kamar zai yi kuka saboda kaunar da yake wa Rimsha gashi ta jefa kan ta cikin wahala.
Basu bar hospital ba sai da daddy ya tabbatar da tasamu lafiya sosai san nan ya ansa magungu nan ta ya wuce ya suka shiga motar sa suka bar hospital É—in, Rimsha ta samu sauki dan da kafar ta ta taka zuwa wajen motar daddy.
Suna isa gida, suka isko mum gwaggo da Jehan a Palo zaune cikin damuwa ko wani hali Rimsha ke ciki, mum na ganin su ta miƙe tana faɗin "Ya jikin nata dai?" kallon face ɗin Rimsha daddy yayi kafin yace cikin zolaya "GAR ya bamu magani ai" cool murmushi Rimsha ta saki har sai da dimple nata ya lotsa open teeth nata ya bayyana ga hakoran nata a jere tsab sai kyalli suke kamar gonar audiga, hakan ba karamin kyau ya karawa kyakkyawar face nata ba, duk da cewa ta ɗan rame saboda zazzaɓin, sleeping eyes nata sun kara haske sosai sun kara girma saboda yar ramar da tayi. Riƙo hannun ta gwaggo tayi suka haura sama dan taje ta mata wanka ta huta, wucewa daddy yayi ta nufi bedroom na shi yana faɗin "Ina son magana da ke boɗɗi" cikin sauri mun tabi bayan sa ita kuma Jehan tabi su gwaggo.
Zaune bakin gado ta isko sa yayi shiru kamar mai tunani wani abun, "lafiya daddyn Jehan?" Mum ta tambaya dai dai lokacin da take zama a gefen sa, dogon numfashi yaja tare da sauke wa a hankali ya ɗan juyo suna fiskantar juna "Wallahi ba lafiya ba" zaro ido waje mum tayi tana faɗin "Meke faruwa to?" Riko hannun ta daddy yayi ya fara magana cike da damuwa "kwana ki na ta tafiya zaɓe na ta kara gabatowa ni kuma sai kara samun baraza nake daga abokan ha mayya, baraza ta ko ina nake samu abun ya fara affecting ɗina na fara karaya, dan wasu ma ban san daga ina suke min barazanar ba, ina tsoron kada na jefa rayuwar ku a cikin haɗari bana son abun da zai taɓa min ku bana son tashin hankali ku, ina ganin zan hakura da siyasar nan kawai" cikin sauri mum tace "A'a barkama ni ban yarda da ka hakura da siyasa ba, kasan cewar adalin mutun irin ka mai gaskiya a siyasa babban nasara ne ga yan kasa, kana da tausayi kuma zaka taimakawa talakawa, na sani siyasa babban haɗari ne dan ba kowa yake son cigaba al'umma ba, amma jajirtattun mutane ire iren ka masu son tai makon talakawa bai kamata ku rinƙa karaya kuna sarewa haka ba, kama ta yayi ku rinƙa karawa kan ku kwarin gwiwa, na san cewa rayuwa a matsayin mai gaskiya yafi komai wahala a duniyar da muke ciki yanzu, dan dayawa daga cikin mutane sun ajiye gaskiya sun bi karya da ha inci a guje suna son kamawa su runguma, wasu ma har sun kama sun runguma ɗin sun yar da gaskiya, kayi rayuwa ba tare da cutar da wani ko tauye hakkin wasu ba yafi komai wahala a duniyar yanzu, babu mai tai makon ɗan uwan sa, jama'a da dama sun manta lahira sun rungumi duniya hannu bibbiyu, jama'a da dama sun manta cewa wanda ka bayar shi zaka tarar a lahira wanda kuma kaci a nan duniya zaka barshi, dan Allah barkama ka karawa kan ka karfin gwiwa wajen ganin ka tsaya tsayin daka ka ceto mana kasar mu, muna bukatar adalin shugaba irin ka, kasar mu na bukatar jajirtattun maza irin ka, aikin Allah na da wahala, ba'a shiga aljanna a na kwance a gado, duk wanda Allah keso da Rahma to sai ya jarrabe shi da wani abun, to ka ɗauka duk wan nan barazana da abokan hamayya suke maka jarabawa ce daga Allah, kuma ka dage ka ci jarabawar, san nan ka zauna da kowa zuciya ɗaya" duk wan nan hiran da suke cikin harshen turanci suke yin sa,
dogon numfashi yaja tare da sauke nauyayyar ajiyar zuciya kafin yace "Kin san me?" Girgiza masa kai tayi alamar a'a "Meeting da naje ɗazun sai da nayi dana sanin shiga ta siyasa, saboda a fillin Allah wasu daga cikin manya ke min baraza a kan na janye tun yanzu abun ya tsorata ni, shi yasa nake tsoron kar na jefa rayuwar ku cikin haɗari" kwanciya mum tayi a jikin sa cikin sigar soyayya ta fara magana "Barkama ka sani fa kafin mutun yaji daɗi sai ya sha wahala, musamman ma mutun mai zuciyar gaskiya irin naka to fa sai ka daure ka kawar da kan ka daga kan wasu abubuwan idan ba haka ba bazaka taɓa cin ma nasara ba, a zamanin yanzun nan duk wanda yace zai fito fili ya nuna cewa shi gaskiya yake so tofa makiya ba zasu taɓa bari ya kai labari ba sai ya dage da kai wa Allah kukan sa, yanzu dai ka manta da komai ka ci-gaba da gwagwarmayan ka kana addu'a muma zamu taya ka, In Sha Allah ba dai ɗan adam ba, sai Allah ya cika maka burin ka na ganin ka taimaki talakawa kuma ka raya mana kasar mu ta girma kamar sauran manya manyan kasashe na duniya In Sha Allah" ta kai karshen maganar tana riƙo hannun sa, murmushi ya saki har sai da dimple nashi ya lotsa, cike da so da kauna yace "Shi yasa nake son ki matata duk lokacin da na shiga damuwa kin san yadda zaki yi ki kwantar min da hankali, duk wata natsala ta idan na kawo miki, ba za'a fi 10mins ba kike samo mana mafita, Allah ya miki albarka ki taya ni da addu'a In Sha Allah burin mu zai cika bari naje nayi wanka yanzu na fito sai mu ci-gaba da hirar ko?" Gyaɗa masa kai tayi tana faɗin "Amin ya Allah" ta kai karshen maganar tare da tashi daga jikin sa, miƙewa yayi ya nufi toilet ita kuma ta miƙe ta wuce wajen drawer kayan sa ta ciro masa kayan sawa da duk wani abun da zai buƙata ta dawo ta ajiye masa a bakin gado san nan ta haye saman gadon ta kwanta tana tunanin rayuwa.
After some days
*KADUNA*
A yau Akil yazo yin sallama da Umaisha zai koma makaranta, sanye yake da manyan kaya wato wata dakakkiyar yadi navy blue mai bala'i kyau da tsada, É—inkin half jomfa, kayan sun masa kyau, yau ma kamar kullun tsaye yake a kofar gida bai shiga ba, ya bawa gidan baya ya kifa kai da jikin mota kamar dai kullun, ya aiki mai gadi da ya kira masa matar sa, ko da mai gadi yaje Abbi baya nan ya tafi company shi kuma Irfan ya wuce Uk tun kwana biyu da suka wuce, gidan ya rage daga Umaisha sai Aafia, koda mai gadi ya sanar da su sakon Akil sai Umaisha tace "Kaje kace masa Abbi yace ya shigo ba zan kara fita ba" tayi maganar cike da tsoron abun da Akil É—in zai mata sai dai kuma ta sawa ranta ko kashe ta zai yi bazata ki bin umarnin Abbin ta tabi na Akil É—in ba.