Sashe 27
Triplets Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
da kyar Rimsha ta iya kai karshen suratul bakara tana kokarin durkushewa kasa a wajen daddy da ya kasa hakuri ya taso da sauri yazo ya rungume ta yana faɗin "It's okey my siha" cikin kuka tace "Daddy me mutun zaiyi a dunuyyar nan da ya wuce bautan Allah daddy mutuwa gaskiya ce kwanciyar kabari gaskiya ce gadar siraɗi gaskiya ce hisabi gaskiya ce haka zalika wuta da aljanna gaskiya ce daddy, duk wani rai sai ya ɗanɗani zafin mutuwa daddy, duk lokacin da na kalli kwayar idon ɗan Adam daddy ina kara jin tsoron Allah da ganin girman Allah a rayuwata dan idon ɗan adam ma kawai ya isa yasa bawa mai hankali ya kara jin tsoro Allah, duk lokacin da na tuna da mutuwa hisabi kwanciyar kabari gadar siraɗi wutar jahannama daddy ina shiga tashin hankali sai in ji gaba ɗaya duniya ta fitamin a rai na daddy, me ya rage bawa yake so bayan yayi bautar Allah dan ya samu ya tsira ranar gobe kiyama, daddy ban taɓa kwaciya barci na sawa rai na zan farka a duniya ba, ban taɓa lissafin me zai faru gobe na ba kullu lissafi na iya yau nake dan bana sawa rai na zan kai goben mutuwa gaskiya ce kuma tana ɗauka duk lokacin da kwanan mutun ya kare ba ruwan ta da abun da kake ko in da kake zata ɗauke kane kawai, daddy duk wani musulmi kamata yayi ya sawa ransa iya yau kaɗai garesa ba zai kai gobe ba dan ya samu damar aikata aikin Allah, daddy duk lokacin da na samu dama har tsawon kwana na ya kai nayi sallar issha, ji nake tamkar an sauke min wani katon dutse a kai na dan kullun ina cikin fargabar kada na mutu gab da wata sallar ko azahar ko la'asar kuma a ce ban samu damar yin wan nan sallar ba" ganin maganar da Rimsha take babban magana ne yasa director ya kawo mata mike ɗin sai tin bakin ta dan kowa yaji maganar nata, sosai hall ɗin gaba ɗaya suka ɗauka da kuka babban magana miƙewa manya manyan sarakuna irin su sarkin Zazzau Sarkin kano Gombe Bauci da dai sauransu suka yi, ba karamin tashin hankali magangun Rimsha ta jefasu ba yariya yar karama kamar wan nan amma tana da karfin imani har haka shi kan shi daddy yayi shocked da jin maganar Rimsha yasan dai tafi Jehan ilimin addini dan ita kullun tana tare da mum tana koya mata karatun addini ban da Jehan da a iya islamiyya kawai take ɗauka bai taɓa tunanin girman ilimin Rimsha ya kai haka ba, ba wanda bai yi mamaki da jinjinawa Rimsha ba ta girgiza gaba ɗaya hall ɗin ta karawa mutane da dama imani a ran su dayawa daga cikin wayan da suka halakci wajen sun kudurci niyar gyara ɗabiun su marasa kyau ta dalilin maganganun Rimsha, sosai suka shiga tashin hankali duk wanda ya manta da lahira yau sai da Rimsha ta tuna masa wani ma ji yayi kamar yaje ya sadakar da dukiyar sa dukka ya koma ga Allah yayi ta ibada,
da gudu Jehan ta miƙe ta hauro saman wajen ta rungumi Rimsha tana kuka tana faɗin "Kinyi gaskiya yar uwata duk abun da kika faɗa gaskiya ne amma jama'a da dama sun shagala da duniya sun manta da mutuwa da kwantatciyar kabari sun manta duhun kabari da siraɗi da hisabi idan ka dace ka shiga aljanna idan baka dace ba ka wuce wutar jahannama bayan ka gama ansan azabar kabari dana siraɗi ga tsayuwa kafin hisabi tsayuwar shekara ɗai ɗai har shekara dubu saba'in ga kuma rana a dai dai sai tin kan ku babu dare babu inuwa sai wan da yayi aikin Allah ne kaɗai zai shiga inuwar al'arshin Ubangiji Innalillahi wa inna ilaihir rajiun Allah mun tuba mun tuba ya Allah" sosai jama'a suka ciro wayoyin su suka rinƙa yi musu video ciki har da director.
Da kyar daddy ya iya rarrashin Rimsha sai da tayi shiru san nan ya riƙo hannun ta suka miƙe ya dubi director yace "Mu zamu wuce gida ba zamu iya jira a gama taro ba dan jikin siha ya fara zafi saboda kukan da tayi" ya kai karshen maganar tare da kallon gwaggo dake zaune saman nata kujerar tana goge kwallan dake idon ta yace "Aunty A'isha muje ko?" Da kyar gwaggo ta iya miƙewa dan gaba ɗaya Rimsha ta kashe mata jiki, gaba ɗaya manya manyan baki da sarakunan dake wajen suka miƙe dan raka su daddy zuwa wajen mota, sunyi sunyi a kan daddy ya bari suyi hoto da Rimsha amma yaki haka suka hakura ba dan sun so ba suka bar su Rimsha suka tafi ba tare da sun yi hoton ba, da haka taron ya watse dan dukkan su sun kasa gudanar da komai jikin su ya mutu da har da kayan kiɗa suka kawo amma jin zancen Rimsha yasa suka manta da wani kayan kiɗa da suka kawo, kowa ya wuce gida taro ya watse
💞💞💞💞💞💞💞💞
KANO
Zaune jelly take saman mirror chair daddy na tsaye a kan ta yana ɗaure mata gashin kan ta da roba irin na kitson yara kasan cewar gashin nata yayi tsantsi sosai baya kitsowa sai dai a ɗadɗaure mata shi da roba, sai murmushi take fararen hakwaranta masu kyau suna jere kanana da su sai kyalli suke, shi ma daddy sai murmushi yake yace "My baby kinyi kyau over" kara murmushi tayi sosai a wan nan karon har fararen hakoran ta suka kara bayyana sosai "Daddy amma dai yaya Imran zai zo school na mu ko?" Tayi maganar cikin shagwaɓa "Eh my baby yace min zai zo In Sha Allah" tana kokarin sake yin magana daddy yace "Sauko na gama kuma surutun nan ya isa dan 07:00 am tayi yanzu taso na sanya miki uniform dan karmuyi late" make masa kafaɗa tayi cikin shagwaɓa tace "Daddy kai fa ka ɗaurani saman chair ɗin yanzu kuma kace na sauko da kai na ni ban iya ba" girgiza kai kawai yayi ya sanya hannu ya ɗagota cak suka nufi wajen gado dan bai son biye mata idan ya biye mata ba zasu wuce school da wuri ba,
saman gado ya É—aura ta san nan ya wuce ya É—auko mata uniform nata riga fari da wando blue sai É—an hijabi fari ya dawo ya sanya mata sharp sharp san nan ya É—auko perfume ya feshe ta da shi nan take ta fara zuba kamshi wuce wa yayi ya É—auki suit nasa da zai sanya ya shige toilet,
tana zaune har ya fito shirye cikin bakin suit da ya ɗauka ya dube ta yace "Let's go my baby" shiru ta masa kamar bata ji me yace ba, sake mai mai ta maganar yayi dai dai lokacin da yake ɗauko jakar computer sa nan ma sake masa shiru tayi kamar bata san da mutun a ɗakin ba, da sauri ya juyo dan yaga wai ko barci tayi ne ganin idon ta kar a kan sa ta turo baki kamar biro ne yasa ya dafe kan sa da hannun sa yana faɗin "Yanzu kuma menene? haba my baby zamu makarafa" kukan shagwaɓa ta sa masa tana faɗin "Ni daddy yanzu ka dai na sona baka ɗauka na sai kace na tafi da kafata" "Haba my baby yanzu fa 11 years kike da shi gaskiya kin min katuwa ba zan iya ɗaukan ki ba" sauka kasa tayi daga saman gadon ta kwanta a kasa ta fara birgima tana masa kuka girgiza kai yayi ya ratiyo jakar computer sa ya kariso wajen tare da sanya hannu ya ɗauke ta cak kamar yar baby suka nufi waje, ganin ya ɗauke ta yasa tayi shiru kamar an kashe gen.
Ko da suka fito palo su Zuwaira sun kammala shirya musu breakfast ga kuma basket na school É—in Jelly sun shirya mata abincin ta a ciki roban cool Yoghurt ne mai É—an girma da snacks a cikin wata kyakkyawar transparent roba sai pepper chicken a cikin foodflask, daddy bai tsaya yin breakfast ba dan time ya tafi basket na lunch nata kawai ya É—auka mata suka nufi waje lokacin 7:45 am yayi.
Suna fita harabar gidan wata dankareriyar mota kirar Mercedes-Benz ta danno hanci cikin gidan ihu jelly ta fasa mai rikita ƙwaƙwalwa tana faɗin "Daddy ka sauƙe Ni" ba musu ya sauƙe ta da gudu ta nufi motar zata runguma ba ruwan ta da tafi motar yake, saura kaɗan yabi ta kan ta dan irin shigar da tayiwa motar, a sukwane mamallakin motar ya taka birki, ba karamin tsorata daddy yayi ba ganin saura kaɗan motar ya take ta, ita ko, ko a jikin ta bata ma san me tayi ba da gudu ta karisa wajen marfin motar tana faɗin "Yaya Imran nayi kewar ka" gently a ka buɗe kofar motar a hankali ya zuro kyawawan kafafun sa dake sanye cikin cover shoe baƙi waje kafin ya fito gaba ɗaya, cikakken namiji ne chocolate color yana da dogon hanci da dara daran idon ga kyakkyawan saje kwance a face na shi kaman sa ɗaya da daddyn Jelly sai dai shi chocolate color ne sosai, yana sanye cikin dakakkiyar shadda fara tas da hula baki sai cover baki a kafar sa kyakkyawa ne a jin farko, da sauri Jelly ta faɗa jikin sa tare da sakin kukan shagwaɓa, ɗagata sama yayi yana faɗin "Rabin rai na nima ai nayi kewar ki yanzu dai a dai na min kukan haka ya isa kin san ban son kukan ki ko?" kwantar da kan ta tayi saman kafaɗar sa tana yar dariya kamar ba ita ke kuka yanzu ba, wucewa Imran yayi ɗauke da ita a jikin sa ya nufi daddy dake tsaye sai murmushi yake bakin sa yaki rufuwa yana bala'i kaunar Imran sosai,
da gudu Jehan ta miƙe ta hauro saman wajen ta rungumi Rimsha tana kuka tana faɗin "Kinyi gaskiya yar uwata duk abun da kika faɗa gaskiya ne amma jama'a da dama sun shagala da duniya sun manta da mutuwa da kwantatciyar kabari sun manta duhun kabari da siraɗi da hisabi idan ka dace ka shiga aljanna idan baka dace ba ka wuce wutar jahannama bayan ka gama ansan azabar kabari dana siraɗi ga tsayuwa kafin hisabi tsayuwar shekara ɗai ɗai har shekara dubu saba'in ga kuma rana a dai dai sai tin kan ku babu dare babu inuwa sai wan da yayi aikin Allah ne kaɗai zai shiga inuwar al'arshin Ubangiji Innalillahi wa inna ilaihir rajiun Allah mun tuba mun tuba ya Allah" sosai jama'a suka ciro wayoyin su suka rinƙa yi musu video ciki har da director.
Da kyar daddy ya iya rarrashin Rimsha sai da tayi shiru san nan ya riƙo hannun ta suka miƙe ya dubi director yace "Mu zamu wuce gida ba zamu iya jira a gama taro ba dan jikin siha ya fara zafi saboda kukan da tayi" ya kai karshen maganar tare da kallon gwaggo dake zaune saman nata kujerar tana goge kwallan dake idon ta yace "Aunty A'isha muje ko?" Da kyar gwaggo ta iya miƙewa dan gaba ɗaya Rimsha ta kashe mata jiki, gaba ɗaya manya manyan baki da sarakunan dake wajen suka miƙe dan raka su daddy zuwa wajen mota, sunyi sunyi a kan daddy ya bari suyi hoto da Rimsha amma yaki haka suka hakura ba dan sun so ba suka bar su Rimsha suka tafi ba tare da sun yi hoton ba, da haka taron ya watse dan dukkan su sun kasa gudanar da komai jikin su ya mutu da har da kayan kiɗa suka kawo amma jin zancen Rimsha yasa suka manta da wani kayan kiɗa da suka kawo, kowa ya wuce gida taro ya watse
💞💞💞💞💞💞💞💞
KANO
Zaune jelly take saman mirror chair daddy na tsaye a kan ta yana ɗaure mata gashin kan ta da roba irin na kitson yara kasan cewar gashin nata yayi tsantsi sosai baya kitsowa sai dai a ɗadɗaure mata shi da roba, sai murmushi take fararen hakwaranta masu kyau suna jere kanana da su sai kyalli suke, shi ma daddy sai murmushi yake yace "My baby kinyi kyau over" kara murmushi tayi sosai a wan nan karon har fararen hakoran ta suka kara bayyana sosai "Daddy amma dai yaya Imran zai zo school na mu ko?" Tayi maganar cikin shagwaɓa "Eh my baby yace min zai zo In Sha Allah" tana kokarin sake yin magana daddy yace "Sauko na gama kuma surutun nan ya isa dan 07:00 am tayi yanzu taso na sanya miki uniform dan karmuyi late" make masa kafaɗa tayi cikin shagwaɓa tace "Daddy kai fa ka ɗaurani saman chair ɗin yanzu kuma kace na sauko da kai na ni ban iya ba" girgiza kai kawai yayi ya sanya hannu ya ɗagota cak suka nufi wajen gado dan bai son biye mata idan ya biye mata ba zasu wuce school da wuri ba,
saman gado ya É—aura ta san nan ya wuce ya É—auko mata uniform nata riga fari da wando blue sai É—an hijabi fari ya dawo ya sanya mata sharp sharp san nan ya É—auko perfume ya feshe ta da shi nan take ta fara zuba kamshi wuce wa yayi ya É—auki suit nasa da zai sanya ya shige toilet,
tana zaune har ya fito shirye cikin bakin suit da ya ɗauka ya dube ta yace "Let's go my baby" shiru ta masa kamar bata ji me yace ba, sake mai mai ta maganar yayi dai dai lokacin da yake ɗauko jakar computer sa nan ma sake masa shiru tayi kamar bata san da mutun a ɗakin ba, da sauri ya juyo dan yaga wai ko barci tayi ne ganin idon ta kar a kan sa ta turo baki kamar biro ne yasa ya dafe kan sa da hannun sa yana faɗin "Yanzu kuma menene? haba my baby zamu makarafa" kukan shagwaɓa ta sa masa tana faɗin "Ni daddy yanzu ka dai na sona baka ɗauka na sai kace na tafi da kafata" "Haba my baby yanzu fa 11 years kike da shi gaskiya kin min katuwa ba zan iya ɗaukan ki ba" sauka kasa tayi daga saman gadon ta kwanta a kasa ta fara birgima tana masa kuka girgiza kai yayi ya ratiyo jakar computer sa ya kariso wajen tare da sanya hannu ya ɗauke ta cak kamar yar baby suka nufi waje, ganin ya ɗauke ta yasa tayi shiru kamar an kashe gen.
Ko da suka fito palo su Zuwaira sun kammala shirya musu breakfast ga kuma basket na school É—in Jelly sun shirya mata abincin ta a ciki roban cool Yoghurt ne mai É—an girma da snacks a cikin wata kyakkyawar transparent roba sai pepper chicken a cikin foodflask, daddy bai tsaya yin breakfast ba dan time ya tafi basket na lunch nata kawai ya É—auka mata suka nufi waje lokacin 7:45 am yayi.
Suna fita harabar gidan wata dankareriyar mota kirar Mercedes-Benz ta danno hanci cikin gidan ihu jelly ta fasa mai rikita ƙwaƙwalwa tana faɗin "Daddy ka sauƙe Ni" ba musu ya sauƙe ta da gudu ta nufi motar zata runguma ba ruwan ta da tafi motar yake, saura kaɗan yabi ta kan ta dan irin shigar da tayiwa motar, a sukwane mamallakin motar ya taka birki, ba karamin tsorata daddy yayi ba ganin saura kaɗan motar ya take ta, ita ko, ko a jikin ta bata ma san me tayi ba da gudu ta karisa wajen marfin motar tana faɗin "Yaya Imran nayi kewar ka" gently a ka buɗe kofar motar a hankali ya zuro kyawawan kafafun sa dake sanye cikin cover shoe baƙi waje kafin ya fito gaba ɗaya, cikakken namiji ne chocolate color yana da dogon hanci da dara daran idon ga kyakkyawan saje kwance a face na shi kaman sa ɗaya da daddyn Jelly sai dai shi chocolate color ne sosai, yana sanye cikin dakakkiyar shadda fara tas da hula baki sai cover baki a kafar sa kyakkyawa ne a jin farko, da sauri Jelly ta faɗa jikin sa tare da sakin kukan shagwaɓa, ɗagata sama yayi yana faɗin "Rabin rai na nima ai nayi kewar ki yanzu dai a dai na min kukan haka ya isa kin san ban son kukan ki ko?" kwantar da kan ta tayi saman kafaɗar sa tana yar dariya kamar ba ita ke kuka yanzu ba, wucewa Imran yayi ɗauke da ita a jikin sa ya nufi daddy dake tsaye sai murmushi yake bakin sa yaki rufuwa yana bala'i kaunar Imran sosai,