Sashe 53
Triplets Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sallama mai gadi ya shigo palon, Abbi da Irfan har suna haÉ—a baki wajen amsa masa sallamar tasa "Lafiya mai gadi" cewar Irfan, cikin girmamawa mai gadi yace "Wani bako ne yazo yace na kira masa matar sa, shine na tambaye sa waye yace bai sani ba idan naje kawai nace a na kiran matar Akil tasan kan ta" tashin sense kallon su Aafia Abbi yayi kafin yace "Yau she ku kayi aure ban sani ba? Dan ku kaÉ—ai ne mata a gidan nan" Jinjina kai Irfan yayi kafin yace da mai gadi "Je kace ya shigo" da sauri mai gadi ya wuce ya koma bakin gate, shi kuma Akil ya dawo da kallon sa kan Abbi cikin nitsuwa ta fara yiwa Abbi bayanin abun da ke faruwa ta sigar da zai fahimter, shiru Abbi ya É—an yi kafin ya É—ago yana kokarin yin magana mai gadi ya dawo bakin sa É—auke da sallama.
"Ina yake?" Irfan ya tambayi mai gadi, Mai gadi yace "Oga yace wai in ce muku idan shiga gidan yake son yi ai ba sai an masa iso ba, ba sai an bashi izini ba yasan hanyar shigowar dan haka bai da niya kawai in ce matar sa tazo yanzun nan ya bata 2mins" shiru Irfan ya ɗan yi na yan seconni kafin yace "Shike nan jeka abun ka, ke kuma Umaisha ta shi kije" Abbi zai yi magana Irfan yayi saurin cewa "Dan Allah Abbi kayi hakuri na yau kawai zan ga gudun ruwan sane" shiru Abbi yayi bai yi magana ba, miƙewa Umaisha tayi jiki a mace cike da jin kunya ta haye sama.
Jim kaɗan ta fito sanye da yar karamar gyale a jikin ta tazo ta wuce su Abbi kunya kamar ta shige cikin kasa haka ta nufi waje, ba karya da Abbi yaji Akil na son Umaisha yaji daɗi sosai ko ba komai zasu kara dankon zumunci, amma sai dai yana tausayawa Umaisha ɗin dan yasan zama surukar hajiya Umaiya ba karamin abu bane sai wanda ya shirya dan masifaffiyar mace ce lamba ɗaya, sai dai duk masifar ta sai ka taɓo ta san nan kuma idan tana son ka zaka ji daɗi dan tana da kyau ta over ga wadda tayi niya, kuma tana da kirki ga wadda take so.
Baki É—auke da sallama Umaisha ta isa wajen sa, yana tsaye jikin motar sa ya bawa gidan nasu baya ya Kifa kan sa a jikin motar kamar mai tunanin wani abu, yau sanye yake cikin dakakkiyar shadda milk color mai bala'i tsada É—inkin ta zauna a jikin sa sosai, half jomfa a ka masa yasha hula kamar ustaz,
jin sallamar ta yasa ya juyo cikin nitsuwa, kallo ɗaya ya mata ya ɗaure fuska sosai kamar bai san Menene dariya ba, a kule yace cikin tsawa "Ki koma kije ki sanya hijabi!! Kuma idan kika kuskura na sake ganin ki ba hijabi sai ranki ya ɓaci!!" Ya karisa maganar kamar zai wanka mata mari saboda haushi, murya na rawa tace "Kayi hakuri yaya Akil bani da hijabi ne shi yasa, duk wanda yaya Irfan ya saya mana na kyautar da yaya Irfan ya koma Zaria lokacin" a fusace ya ɗaga hannu har zai mareta sai kuma ya fasa cikin fushi yace "Shiga mota muje" cike da tsoro tace "Ina zamuje?" Shiru ya mata kamar bai ji me tace ba, ganin haka yasa tace "To bari na faɗa wa su Abbi sai nazo mu tafi...bata kai karshen maganar ba taji saukan mari a kumatun ta, rai a matukar ɓace yace "A matsayin kanwa na mareki ba mata ba, ke har kin isa nace muje kice min ina zamuje, san nan kuma daga yau idan nace kiyi abu kika ce min bari ki tambayo wani Allah sai ran ki ta ɓaci, dan ba wanda zaki tambaya ida zakiyi abu sai nine, nine mijin ki ke mallaki nane, ni kaɗai nake da iko da ke, ba wanda ya isa ya nuna min abun da zan yi a kan ki, dan ke ɗin mata tace!!" Ya kai karshen maganar tare da ciro handkerchief daga aljihun sa ya miƙa mata a kan ta goge hawaye, a hankali ta sanya hannu tana hawaye zata ansa handkerchief ɗin, ganin tana abu a hankali zata ɓata masa lokaci ne yasa, ya sanya hannun sa da kan sa ya goge mata hawayen yana faɗin "A matsayin kan wa nake miki hakan" bayan ya goge mata hawayen da kan sa ya buɗe mata motar ta shiga gidan gaba san nan shima ya zagaya ta ɗayan gefen ya shiga ya tada motar suka bar wajen.
Kai tsaye *ABC supermarket* suka nufa, yana tuki yana zuba mata kashe di da dokokin irin kayan da zata rinƙa sawa, gaba ɗaya yayin cancel ɗin gyale a cikin kayan ta, haka riga da wando yace kar ta sake sawa sai tazo gidan sa, san nan attachment da eyelashes duk ya hana yayi cancel, hijabi har kasa ya yarje mata tarinƙan sawa idan zata je school, dokoki kala kala iri iri ya kafa mata, tare da kashe din idan ta karya masa doka ɗaya zatayi bayani sai ranta ya ɓaci, ita kuwa cikin ranta cewa take "zan dai na duk abun da ka hana amma wlh ban da sa gyale, sai na sa in dai gyale ne sai dai ka kashe ni" shiru yayi bai sake magana ba har suka isa super market ɗin
cike da bada umarni yace "Ki zauna a nan karki yarda ki leka waje" ya kai karshen maganar tare da ficewa daga Motar ya nufi cikin super market É—in, sai tsaki take ja, a kule tace "Sai an sa gyale mugu kawai"
Haka tayi ta surutan ta ita kaɗai, har ya dawo hannun sa rike da ledoji manya manya guda biyu, ba tare da ya mata magana ba ya ajiye a gidan bayan motar san nan ya shiga gidan gaba, ya tada motar kai tsaye suka wuce *kasuwar barci* a nan yaje da kan sa ya zaɓa mata manya manyan hijabai wadda yana da tabbacin zasu kai mata har kasa, dan a wan nan karon ma a mota ya barta ya hana ta fita, hijabi 12 ya saya mata manya manya har kasa san nan ya sayawa Aafia ma 12 ya wuce ya dawo mota, yana zama wayar sa ta fara kara, guntun tsaki yaja tare da ɗauko wayar ya duba, a nutse yayi picking call ɗin yana faɗin "Sorry Abla na manta ne amma bari na sa miki yanzu, sai yaushe zaki zo ne?" Daga ɗayan ɓangaren Abla tace "Yaya Akil wai ina yaya Imran ne? Sai kiran sa nake amma baya ɗagawa" kallon face ɗin Umaisha yayi ta cikin mirror motar kafin yace "Abla ni bana gida na fita da Auntyn ku amma idan na dawo zan duba miki me yasa baya ɗaukan kiran, amma dai koma me kin dai san ba da gan gan yaki ɗauka bako?" Da sauri Abla tace "Yaya Akil Auntyn mu kuma? Jinjina kai yayi yana faɗin "Eh Auntyn ku" cikin zumuɗi tace "Dan Allah yaya Akil ka bata waya mu gaisa" "Me zaki faɗa mata?" Shagwaɓa murya tayi kafin tace "Kai yaya Akil gaisawa kawai zamuyi" girgiza kai yayi yana faɗin "A'a ai na sanki ne da iya yi" "Kai yaya ba wani iyayi Allah" sanya wayar yayi a hand-free san nan ya miƙa wa Umaisha, jikin ta har kerma yake wajen ansar wayar tana faɗin "Assalamu alaikum" da murna Abla tace "Waalaikumussalam Auntyn mu ina wuni?" Kallon sa ta kasan ido Umaisha tayi kafin tace "Lafiya lou Aunty Abla yasu mama?" kunna motar sa yayi ya ɗauki hanya yana sauraron hirar tasu
Sai murmushi Umaisha ke yi, Abla tace "Auntyn mu waye baban ki? Yar gidan sarki ne ke ko yar governor? Dan nasan yaya Akil ba zai zaɓo mana yar gidan kananan mutane ba" nan take face ɗin Umaisha ta sauya ta dai na murmushi jiki a mace tace "Ni ba...bata karisa ba ya ansa wayar cikin faɗa yace "Abla abun da zaki tambaye ta kenan? Wan nan tambayar ni zaki yiwa ai ba ita ba" murya na rawa Abla tace "Kayi hakuri yaya Akil" tsawa ya daka mata "Abla kullun ina faɗa miki ki ɗauki duniya da sauki ki dai na jin zancen Ammie a kunnan ki baki ji ko? Kullun sai na faɗa miki ki dai na cewa kina kyamar talakawa amma baki ji ko kaɗan ko? Ya miki kyau to ba yar kowa bace yar talakawa ce, kuma a haka nace nake so ko akoi wadda ya isa ya hanani auren zaɓin rai na ne?" Murya har sarkewa yake tace "Kayi hakuri yaya Akil tuba nake" dogon tsaki yaja tare da katse kiran, shiru Umaisha tayi tana tunani "Ashe daman yaya Akil yana da hankali, ashe kawai zafin rai gare sa ba wai rashin hankali ba Allah sarki, Allah ya sassauta masa zafin kan nan da zuciyar nan tasa"
shiru sukayi dukkan su, ba wanda ya sake magana har suka isa kofar gida, ya kashe motar sa ya fito ya É—auka mata ledojin dan yasan ba zata iya É—auka ba
suna shiga harabar gida a nan suka isko Abbi da Irfan da Aafia, suna tsaye cirko cirko saboda da sukaji Umaisha shiru bata dawo ba shi sukazo su leka ko tana wajen ganin bata nan shine suka tsaya suna tattaunawa ta ina Irfan zai je neman ta
"Ina yake?" Irfan ya tambayi mai gadi, Mai gadi yace "Oga yace wai in ce muku idan shiga gidan yake son yi ai ba sai an masa iso ba, ba sai an bashi izini ba yasan hanyar shigowar dan haka bai da niya kawai in ce matar sa tazo yanzun nan ya bata 2mins" shiru Irfan ya ɗan yi na yan seconni kafin yace "Shike nan jeka abun ka, ke kuma Umaisha ta shi kije" Abbi zai yi magana Irfan yayi saurin cewa "Dan Allah Abbi kayi hakuri na yau kawai zan ga gudun ruwan sane" shiru Abbi yayi bai yi magana ba, miƙewa Umaisha tayi jiki a mace cike da jin kunya ta haye sama.
Jim kaɗan ta fito sanye da yar karamar gyale a jikin ta tazo ta wuce su Abbi kunya kamar ta shige cikin kasa haka ta nufi waje, ba karya da Abbi yaji Akil na son Umaisha yaji daɗi sosai ko ba komai zasu kara dankon zumunci, amma sai dai yana tausayawa Umaisha ɗin dan yasan zama surukar hajiya Umaiya ba karamin abu bane sai wanda ya shirya dan masifaffiyar mace ce lamba ɗaya, sai dai duk masifar ta sai ka taɓo ta san nan kuma idan tana son ka zaka ji daɗi dan tana da kyau ta over ga wadda tayi niya, kuma tana da kirki ga wadda take so.
Baki É—auke da sallama Umaisha ta isa wajen sa, yana tsaye jikin motar sa ya bawa gidan nasu baya ya Kifa kan sa a jikin motar kamar mai tunanin wani abu, yau sanye yake cikin dakakkiyar shadda milk color mai bala'i tsada É—inkin ta zauna a jikin sa sosai, half jomfa a ka masa yasha hula kamar ustaz,
jin sallamar ta yasa ya juyo cikin nitsuwa, kallo ɗaya ya mata ya ɗaure fuska sosai kamar bai san Menene dariya ba, a kule yace cikin tsawa "Ki koma kije ki sanya hijabi!! Kuma idan kika kuskura na sake ganin ki ba hijabi sai ranki ya ɓaci!!" Ya karisa maganar kamar zai wanka mata mari saboda haushi, murya na rawa tace "Kayi hakuri yaya Akil bani da hijabi ne shi yasa, duk wanda yaya Irfan ya saya mana na kyautar da yaya Irfan ya koma Zaria lokacin" a fusace ya ɗaga hannu har zai mareta sai kuma ya fasa cikin fushi yace "Shiga mota muje" cike da tsoro tace "Ina zamuje?" Shiru ya mata kamar bai ji me tace ba, ganin haka yasa tace "To bari na faɗa wa su Abbi sai nazo mu tafi...bata kai karshen maganar ba taji saukan mari a kumatun ta, rai a matukar ɓace yace "A matsayin kanwa na mareki ba mata ba, ke har kin isa nace muje kice min ina zamuje, san nan kuma daga yau idan nace kiyi abu kika ce min bari ki tambayo wani Allah sai ran ki ta ɓaci, dan ba wanda zaki tambaya ida zakiyi abu sai nine, nine mijin ki ke mallaki nane, ni kaɗai nake da iko da ke, ba wanda ya isa ya nuna min abun da zan yi a kan ki, dan ke ɗin mata tace!!" Ya kai karshen maganar tare da ciro handkerchief daga aljihun sa ya miƙa mata a kan ta goge hawaye, a hankali ta sanya hannu tana hawaye zata ansa handkerchief ɗin, ganin tana abu a hankali zata ɓata masa lokaci ne yasa, ya sanya hannun sa da kan sa ya goge mata hawayen yana faɗin "A matsayin kan wa nake miki hakan" bayan ya goge mata hawayen da kan sa ya buɗe mata motar ta shiga gidan gaba san nan shima ya zagaya ta ɗayan gefen ya shiga ya tada motar suka bar wajen.
Kai tsaye *ABC supermarket* suka nufa, yana tuki yana zuba mata kashe di da dokokin irin kayan da zata rinƙa sawa, gaba ɗaya yayin cancel ɗin gyale a cikin kayan ta, haka riga da wando yace kar ta sake sawa sai tazo gidan sa, san nan attachment da eyelashes duk ya hana yayi cancel, hijabi har kasa ya yarje mata tarinƙan sawa idan zata je school, dokoki kala kala iri iri ya kafa mata, tare da kashe din idan ta karya masa doka ɗaya zatayi bayani sai ranta ya ɓaci, ita kuwa cikin ranta cewa take "zan dai na duk abun da ka hana amma wlh ban da sa gyale, sai na sa in dai gyale ne sai dai ka kashe ni" shiru yayi bai sake magana ba har suka isa super market ɗin
cike da bada umarni yace "Ki zauna a nan karki yarda ki leka waje" ya kai karshen maganar tare da ficewa daga Motar ya nufi cikin super market É—in, sai tsaki take ja, a kule tace "Sai an sa gyale mugu kawai"
Haka tayi ta surutan ta ita kaɗai, har ya dawo hannun sa rike da ledoji manya manya guda biyu, ba tare da ya mata magana ba ya ajiye a gidan bayan motar san nan ya shiga gidan gaba, ya tada motar kai tsaye suka wuce *kasuwar barci* a nan yaje da kan sa ya zaɓa mata manya manyan hijabai wadda yana da tabbacin zasu kai mata har kasa, dan a wan nan karon ma a mota ya barta ya hana ta fita, hijabi 12 ya saya mata manya manya har kasa san nan ya sayawa Aafia ma 12 ya wuce ya dawo mota, yana zama wayar sa ta fara kara, guntun tsaki yaja tare da ɗauko wayar ya duba, a nutse yayi picking call ɗin yana faɗin "Sorry Abla na manta ne amma bari na sa miki yanzu, sai yaushe zaki zo ne?" Daga ɗayan ɓangaren Abla tace "Yaya Akil wai ina yaya Imran ne? Sai kiran sa nake amma baya ɗagawa" kallon face ɗin Umaisha yayi ta cikin mirror motar kafin yace "Abla ni bana gida na fita da Auntyn ku amma idan na dawo zan duba miki me yasa baya ɗaukan kiran, amma dai koma me kin dai san ba da gan gan yaki ɗauka bako?" Da sauri Abla tace "Yaya Akil Auntyn mu kuma? Jinjina kai yayi yana faɗin "Eh Auntyn ku" cikin zumuɗi tace "Dan Allah yaya Akil ka bata waya mu gaisa" "Me zaki faɗa mata?" Shagwaɓa murya tayi kafin tace "Kai yaya Akil gaisawa kawai zamuyi" girgiza kai yayi yana faɗin "A'a ai na sanki ne da iya yi" "Kai yaya ba wani iyayi Allah" sanya wayar yayi a hand-free san nan ya miƙa wa Umaisha, jikin ta har kerma yake wajen ansar wayar tana faɗin "Assalamu alaikum" da murna Abla tace "Waalaikumussalam Auntyn mu ina wuni?" Kallon sa ta kasan ido Umaisha tayi kafin tace "Lafiya lou Aunty Abla yasu mama?" kunna motar sa yayi ya ɗauki hanya yana sauraron hirar tasu
Sai murmushi Umaisha ke yi, Abla tace "Auntyn mu waye baban ki? Yar gidan sarki ne ke ko yar governor? Dan nasan yaya Akil ba zai zaɓo mana yar gidan kananan mutane ba" nan take face ɗin Umaisha ta sauya ta dai na murmushi jiki a mace tace "Ni ba...bata karisa ba ya ansa wayar cikin faɗa yace "Abla abun da zaki tambaye ta kenan? Wan nan tambayar ni zaki yiwa ai ba ita ba" murya na rawa Abla tace "Kayi hakuri yaya Akil" tsawa ya daka mata "Abla kullun ina faɗa miki ki ɗauki duniya da sauki ki dai na jin zancen Ammie a kunnan ki baki ji ko? Kullun sai na faɗa miki ki dai na cewa kina kyamar talakawa amma baki ji ko kaɗan ko? Ya miki kyau to ba yar kowa bace yar talakawa ce, kuma a haka nace nake so ko akoi wadda ya isa ya hanani auren zaɓin rai na ne?" Murya har sarkewa yake tace "Kayi hakuri yaya Akil tuba nake" dogon tsaki yaja tare da katse kiran, shiru Umaisha tayi tana tunani "Ashe daman yaya Akil yana da hankali, ashe kawai zafin rai gare sa ba wai rashin hankali ba Allah sarki, Allah ya sassauta masa zafin kan nan da zuciyar nan tasa"
shiru sukayi dukkan su, ba wanda ya sake magana har suka isa kofar gida, ya kashe motar sa ya fito ya É—auka mata ledojin dan yasan ba zata iya É—auka ba
suna shiga harabar gida a nan suka isko Abbi da Irfan da Aafia, suna tsaye cirko cirko saboda da sukaji Umaisha shiru bata dawo ba shi sukazo su leka ko tana wajen ganin bata nan shine suka tsaya suna tattaunawa ta ina Irfan zai je neman ta