Sashe 81
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya kare mgnar tare da sake hannunta kana ya zauna bisa kuje.
“Suna lfy, gatama tun ɗazu take ta kuka wai in Kira mata Adda Khausy”.
Juyowa yayi ya kalli Khausar ɗin da ta matso kusa dashi tana mai miƙa mishi hannun alamun ya bata wayar, fuska ya tsuke tare da dannan mata harara.
Kana yace Mommy kuwa.
“Toh a bawa Raudat ɗin”.
Cikin kawaici Mommyn ta miƙawa Raudat ɗin waya tana amsa tace.
“Hello Adda Khausy nayi missing inki”.
“A'ah Raudat ya akayi yau bakije school ba?".
Jin hakane yasa Khausar kara matsowa gareshi cikin zumuɗi da son jin muryar Raudat ɗin dan tun shekaran jiya basuyi mgn ba, da sauri ta miƙo hannunta har tana taɓa sajenshi.
Juyowa yayi yana maiyi mata wani irin kallon mai haɗa da saƙonni masu yawa, katse kiran yayi baƙi ɗaya ya xora wayar a aljihun rigar shaddar dake jikinsa wacce iri ɗaya ne da nata.
Cikin tsuke fuska ya tsira mata ido tare da juyowa ya fuskanceta da kyau idonshi ya zira cikin nata tare da cewa.
“Na dai lura ke, in baki taɓani ba, bakya jin daɗin rayuwarki, na gama fahimtarki ban san me kikeso inyi mikiba da kike shigemin rayuwa da jiki, gaba ɗaya in kin gannin jikinki rawa yake, ji kike kamar kin cinyeni ɗanye dan rashin ta ido, yanzu ji yadda kike wani son kamani ban san uwar me kikeso inyi miki ba”.
Ya ƙare mgnar cikin ƙarfin hali.
Ita kam Khausar cikin mmki da tsoron lamarin shi ta buɗe baki tare da cewa.
“Ni dai Allah ya sani ba abinda ya dameni da kai, kawai wayata zaka bani, toh ma ni me ruwana da kai”.
Ta ƙare mgnar tana tura baki.
Da hannunshi yasa ya kamo hannunta tare da matsewa har saida tayi ƙara kana yace.
“A hakan dai kikace kina sona! Ga yadda kike kallona kamar ki haɗiyeni ni ban masan me sajena ya tsare mikiba".
Da sauri ta kwaɓe fuska tare da yin ƙasa da kanta tace.
“Toh ni ai wayata nake kalla".
Ta ƙare maganar tana tura baki.
Shi kuma cikin tsareta da ido yace.
“Jiya da dare ba biyoni kikayi ba”.
Sai kuma ya miƙe tsaye tare da motsowa kusa da ita cikin wata irin sassautacciyar muryansa can ƙasan maƙoshi yace..
“Ni kikeyiwa haka ko? Zanyi maganinki zan miki abin da kike son inyi mikin, tunda na lura a hannu kike”. Ita batama fahimci mgnar ba sai dai jujjuya ido da tayi cikin shaƙar ƙamshin jikinsa tace.
“Ni dai ka bani wayata”. Tsuke fuska yayi tare da matse jikinsa baga ɗaya kana cikin danne yanayin da yake ciki yace.
“Bazan badawa”.
Sai kuma yayi mata kallon sama da ƙasa kai ya jinjina ganin mayafin jikinta ya ɗan rufe mata ƙirji, juyawa yayi kana ya ɗan zagaya bayanta tare da cewa.
“Mu tafi Didi na kiranki". Zuwa yanzu tasan waye Didi tasan nasabarta da kuma kimarta, haka yasa cikin nitsuwa tayi gaba batare da tacemai ko ƙalaba, bayanta yabi, tare da sauƙe ganinsa kan ƙugunta dake juyawa kai kace kamar da gayya takeyi.
Kiciniyar buɗewa kofar ta fara, shi kuwa ido kawai ya zuba mata, kusan one minute tana kiciniyar, gani, ta gazane ta juyo ta kalleshi tare ɗan tura baki tace.
“Na kasa buɗewa”. Kallon gefen ido yayi mata kana yace.
“Uhmmm dama ke me kika iya banda rawan kai”.
Wasu pin number dake jikin ɗan ƙofar ya danna wanda shima Ibraahim ne ya nuna masa.
Da hannun yayi mata alamun su tafi.
A hankali suka fito kana yaja ƙofar ya rufe, jujjuya kai tayi don so take ta gane ta inane inda su Ummi suke amman ta gaza ganewa kasancewar idonta a rufe suka fito, kuma ma ƙofofin wurin sunyi yawa.
A hankali ta fara taka steps din suna sauƙa ga mamakinta sai taga basu ɓullo cikin falon nanba, sai ganinta da tayi cikin corridor nan mai faɗi, kusan a jere suke tafiya yayinda suke baza wani irin fitinennen ƙamshi kamar furannin.
Da sauri tayi ƙasa da kanta lokacin da taga sun ɓullo cikin wani ƙasaitaccen falo, wanda tayi arba da Rahama dake tsaye, da sauri Rahama ta nufeta tare da buɗe mata hannun.
A hankali ta ware hannunta suka ruggume juna.
Didi kuwa murmushi ta saki tare da miƙewa, ruggume su tayi duka biyu tana mai cewa.
“A onmi jam nɓingel am". Kin tashi lafiya ɗiyata”.
Cikin mmkin yadda akayi Didi da yaranta kab da yawa da cikin mutanen makusantansu suka iya fllanci ras ta ɗan kalli fuskar Didi tare da cewa.
“Jam Alhamdulillah Didi noi Chomri".
Lfy lau Alhamdulillah Didi ya gajiya.
Murmushi Didi tayi tare da kallon Modibbo da ya zuba musu ido ko keftawa bayayi.
Sai kuma ta juyo cikin falon jin su Lalla Khadijah suna dariya tare da cewa.
“Didi kalli Ibarahim yadda ya wani zumbura baki, wai sun kwace mishi fada”.
Cikin dariya tace.
“Yoh ai bashi kadaiba kalli Yayan nashi ma yadda ya tsaremu da ido".
Da sauri Modibbo ya kauda kanshi jin abinda Abualeey ke mishi dariya.
Saita nitsuwarsa yayi cikin yanayinsa mishkilanci ya raɓa gefensu ya wuce, biyoshi sukayi a baya.
Ita kuwa Khausar a hankali ta rusuna gaban Abualeey cikin sanyi da girmama tace.
“Barka da safiya Abba”.
Cikin kula yace.
“Barka dai Khausar ya bakunta".
Cikin yin ƙasa da kai tace.
“Alhamdullillah".
Sai kuma ta miƙe sabida kamo hannunta da Aunty Khadija tayi tare da cewa.
“Bismillah zo muje muyi breakfast”.
Kai ta gyaɗa mata kana tabi bayanta.
Yayinda suma duk saura suka bi bayansu suka nufi wani tamfatsestsen Dinning table wanda a ƙalla yake da kujeru goma sha biyu.
Sai kuma duk suka tsaya, har saida Didi da Abualeey suka iso suka zauna sannan duk suka zauna.
Didi da Abualeey suna kan karshen table ɗin a jere, sai kuma Khausar dake gefen Didi forkon layin kenan sai kuma ɗaya gefen forkon layin Modibbo ne zaune wanda ya zama yana fuskarta Khausar.
Sai Ibrahim dake gefshi yana fuskarta Rahama dake gefen Khausar, sai kuma Lalla Hafsat dake fuskantar Hakim sai kuma Lalla Khadijah, dake fuskantar Ashshe.
Ya zama kujeru uku ne babu kowa a kansu.
A hankali Lalla Khadijah ta miƙa tsaye tare da fara savin dinsu ɗaya bayan ɗaya duk da kowa da irin kalan abinda ta zuba mishi.
Abualeey masace mai haɗa da miyar daddageggen nama, sai kuma Modibbo da Ibarahim da ta zuba musu soyayyan dankali, da dege-dege da yaji naman kaza da kuma fararen tsokokin kifi sai kuma wadatacciyar albasar da take sa ɗan sauran gwaninta, sosai yajin yayi meɗeu a cikin domin Ibarahim na son yaji sosai sai kuma soyayyan kwai da yaji vegetables wani iri daddaɗan ƙamshi mai tada tsohuwar yunwa dege-dege ke gazawa, shi ta zubawa Khausar ma da Rahama, sai kuma ta sawa Ashshe da Lalla Hafsat masa da miyan ita kuma irin nasu Khausar Hakim ma Masa da miyarsun ta saka mishi.
Da sauri duk suka juyo jin muryar Dr Jameel da Zakariyya da kusan a tare suka shiga.
Bisa kujeru dake gefen Lalla Khadijah suka zauna bayan sun gama hausawa.
Suna ta zuba musu abincin.
Bismillahi suka kana duk suka fara ci.
Yayinda Khausar kuwa ke riƙe da fork din tana ɗan jujjuyawa tana ganin yadda miyar taji nama da kifi.
Da sauri Didi ta kalleta tare da cewa.
“Bismillah ɗiyata kici abinci”.
Murmushi ta ɗanyi tare da cewa.
“Toh”. Sai kuma ta ƙare mgnar tare da kallon Modibbo dayi loman forko, da sauri ya lumsh idanunsa, yana maijin ɗan-ɗanon abincin mai gamsarwa na ratsa mishi harce, sai dai kuma wani irin gigitaccen yajin da yaji yana gama gaba ɗaya jijiyoyin bakinshi manya da kananan. Allah ya sani shi dai yana masifar tsoron yaji.
Rahama ce ta kalleshi cikin murmushi tace.
“Yah Aleey yayi daɗiko nice nayi mana girkin da kaina”.
Cikin danne azabebben yajin dake gab da gigitashi yace.
“Yes kinci a baki tukuici”.
Sai kuma ya ɗan kalli Ibarahim dake cewa.
“Wow masha Allah ai ɗaɗi kam sosai ma, wannan girki ko yau aka aurar da ke ai bamu da haufi”.
Kai Khausar ta ɗan sunkuyar tare da soka dankali ɗaya ta haɗa da kifin kadan tasa a baki.
Wani irin zar taji yawun bakinta ya tsinke Allah ya sani tana da masifar cin yaji, shiyasa taji abinci yayi mata yadda takeso, sai dai duk da haka yajin ya fitini harshenta.
A hankali ta kalli Lalla Hafsat da kuma Lalla Khadijah dake cin abinci cike da kwanciyar hankali alamun suma manyan askarawa ne a cin yaji.
Sai kuma ta kalli Dr Jameel ta ɗan kalli Abualeey tare da jan plate gabansa ya fara cin masa da miyar Abualeey da aka sa mishi.
A hankali ta dawo da kallonta kan Modibbo da ya kai hannunsa kanshi yana ɗan shafawa tare da yin ƙasa da hannunsa har zuwa ƙeyarsa.
A hankali ta kuma kai loma na biyu wanda zuwa lokacin Ibrahim dasu Kalla Khadijah har sun kusa cin kaso ɗaya bisa ukun na abinci da ke kan plate dinsu.
Shi kuwa Modibbo cikin sanyi ya kai loma ta huɗu wanda tuni idanunsa sun cika da hawaye sabida azabar yaji daya fitini bakinsa.
A hankali ta tsaida idanunta kanshi tana mai tuno wasu kalaman Yah Jameel a ranar da sukayi rabuwar ƙarshe a cikin Shopping mall da suka shiga, a lokacin da yaga ta ɗauki robar dakekken yaji yace mata.
“Na lura kina son Yaji matuƙa, MJ ɗina kuma yana masifar tsoron yaji, kuma muddin yaga mutun yana son a yaba masa kan girkinsa to baya taɓa kushewa, kuma duk rintsi sai yaci dan shi mutum ne da baya son gwatsale mutum.
Shiyasa ko yaya bazai faɗaba, gwara ki sani dan kada kije kiyi ta zabga mishi yaji ki kashe min aminina.
Domin ko yaya bazai faɗa mikiba sai dai idan yaji ya gigita shi, zakiga, zaita shafa kanshi musamman ƙeyarsa kuma idanunshi zasu cika da hawaye, baza kuma su zuboba haka kuma zakiga duk sanyi zai fara zufa toh da zan kinga haka ki sani yajine ya gigitashi”.
Tuno hakanne yasa dawo da hankalinta kanshi ai kuwa zufan yakeyi duk da masifeffen sanyi da AC ke busa musu.
“Suna lfy, gatama tun ɗazu take ta kuka wai in Kira mata Adda Khausy”.
Juyowa yayi ya kalli Khausar ɗin da ta matso kusa dashi tana mai miƙa mishi hannun alamun ya bata wayar, fuska ya tsuke tare da dannan mata harara.
Kana yace Mommy kuwa.
“Toh a bawa Raudat ɗin”.
Cikin kawaici Mommyn ta miƙawa Raudat ɗin waya tana amsa tace.
“Hello Adda Khausy nayi missing inki”.
“A'ah Raudat ya akayi yau bakije school ba?".
Jin hakane yasa Khausar kara matsowa gareshi cikin zumuɗi da son jin muryar Raudat ɗin dan tun shekaran jiya basuyi mgn ba, da sauri ta miƙo hannunta har tana taɓa sajenshi.
Juyowa yayi yana maiyi mata wani irin kallon mai haɗa da saƙonni masu yawa, katse kiran yayi baƙi ɗaya ya xora wayar a aljihun rigar shaddar dake jikinsa wacce iri ɗaya ne da nata.
Cikin tsuke fuska ya tsira mata ido tare da juyowa ya fuskanceta da kyau idonshi ya zira cikin nata tare da cewa.
“Na dai lura ke, in baki taɓani ba, bakya jin daɗin rayuwarki, na gama fahimtarki ban san me kikeso inyi mikiba da kike shigemin rayuwa da jiki, gaba ɗaya in kin gannin jikinki rawa yake, ji kike kamar kin cinyeni ɗanye dan rashin ta ido, yanzu ji yadda kike wani son kamani ban san uwar me kikeso inyi miki ba”.
Ya ƙare mgnar cikin ƙarfin hali.
Ita kam Khausar cikin mmki da tsoron lamarin shi ta buɗe baki tare da cewa.
“Ni dai Allah ya sani ba abinda ya dameni da kai, kawai wayata zaka bani, toh ma ni me ruwana da kai”.
Ta ƙare mgnar tana tura baki.
Da hannunshi yasa ya kamo hannunta tare da matsewa har saida tayi ƙara kana yace.
“A hakan dai kikace kina sona! Ga yadda kike kallona kamar ki haɗiyeni ni ban masan me sajena ya tsare mikiba".
Da sauri ta kwaɓe fuska tare da yin ƙasa da kanta tace.
“Toh ni ai wayata nake kalla".
Ta ƙare maganar tana tura baki.
Shi kuma cikin tsareta da ido yace.
“Jiya da dare ba biyoni kikayi ba”.
Sai kuma ya miƙe tsaye tare da motsowa kusa da ita cikin wata irin sassautacciyar muryansa can ƙasan maƙoshi yace..
“Ni kikeyiwa haka ko? Zanyi maganinki zan miki abin da kike son inyi mikin, tunda na lura a hannu kike”. Ita batama fahimci mgnar ba sai dai jujjuya ido da tayi cikin shaƙar ƙamshin jikinsa tace.
“Ni dai ka bani wayata”. Tsuke fuska yayi tare da matse jikinsa baga ɗaya kana cikin danne yanayin da yake ciki yace.
“Bazan badawa”.
Sai kuma yayi mata kallon sama da ƙasa kai ya jinjina ganin mayafin jikinta ya ɗan rufe mata ƙirji, juyawa yayi kana ya ɗan zagaya bayanta tare da cewa.
“Mu tafi Didi na kiranki". Zuwa yanzu tasan waye Didi tasan nasabarta da kuma kimarta, haka yasa cikin nitsuwa tayi gaba batare da tacemai ko ƙalaba, bayanta yabi, tare da sauƙe ganinsa kan ƙugunta dake juyawa kai kace kamar da gayya takeyi.
Kiciniyar buɗewa kofar ta fara, shi kuwa ido kawai ya zuba mata, kusan one minute tana kiciniyar, gani, ta gazane ta juyo ta kalleshi tare ɗan tura baki tace.
“Na kasa buɗewa”. Kallon gefen ido yayi mata kana yace.
“Uhmmm dama ke me kika iya banda rawan kai”.
Wasu pin number dake jikin ɗan ƙofar ya danna wanda shima Ibraahim ne ya nuna masa.
Da hannun yayi mata alamun su tafi.
A hankali suka fito kana yaja ƙofar ya rufe, jujjuya kai tayi don so take ta gane ta inane inda su Ummi suke amman ta gaza ganewa kasancewar idonta a rufe suka fito, kuma ma ƙofofin wurin sunyi yawa.
A hankali ta fara taka steps din suna sauƙa ga mamakinta sai taga basu ɓullo cikin falon nanba, sai ganinta da tayi cikin corridor nan mai faɗi, kusan a jere suke tafiya yayinda suke baza wani irin fitinennen ƙamshi kamar furannin.
Da sauri tayi ƙasa da kanta lokacin da taga sun ɓullo cikin wani ƙasaitaccen falo, wanda tayi arba da Rahama dake tsaye, da sauri Rahama ta nufeta tare da buɗe mata hannun.
A hankali ta ware hannunta suka ruggume juna.
Didi kuwa murmushi ta saki tare da miƙewa, ruggume su tayi duka biyu tana mai cewa.
“A onmi jam nɓingel am". Kin tashi lafiya ɗiyata”.
Cikin mmkin yadda akayi Didi da yaranta kab da yawa da cikin mutanen makusantansu suka iya fllanci ras ta ɗan kalli fuskar Didi tare da cewa.
“Jam Alhamdulillah Didi noi Chomri".
Lfy lau Alhamdulillah Didi ya gajiya.
Murmushi Didi tayi tare da kallon Modibbo da ya zuba musu ido ko keftawa bayayi.
Sai kuma ta juyo cikin falon jin su Lalla Khadijah suna dariya tare da cewa.
“Didi kalli Ibarahim yadda ya wani zumbura baki, wai sun kwace mishi fada”.
Cikin dariya tace.
“Yoh ai bashi kadaiba kalli Yayan nashi ma yadda ya tsaremu da ido".
Da sauri Modibbo ya kauda kanshi jin abinda Abualeey ke mishi dariya.
Saita nitsuwarsa yayi cikin yanayinsa mishkilanci ya raɓa gefensu ya wuce, biyoshi sukayi a baya.
Ita kuwa Khausar a hankali ta rusuna gaban Abualeey cikin sanyi da girmama tace.
“Barka da safiya Abba”.
Cikin kula yace.
“Barka dai Khausar ya bakunta".
Cikin yin ƙasa da kai tace.
“Alhamdullillah".
Sai kuma ta miƙe sabida kamo hannunta da Aunty Khadija tayi tare da cewa.
“Bismillah zo muje muyi breakfast”.
Kai ta gyaɗa mata kana tabi bayanta.
Yayinda suma duk saura suka bi bayansu suka nufi wani tamfatsestsen Dinning table wanda a ƙalla yake da kujeru goma sha biyu.
Sai kuma duk suka tsaya, har saida Didi da Abualeey suka iso suka zauna sannan duk suka zauna.
Didi da Abualeey suna kan karshen table ɗin a jere, sai kuma Khausar dake gefen Didi forkon layin kenan sai kuma ɗaya gefen forkon layin Modibbo ne zaune wanda ya zama yana fuskarta Khausar.
Sai Ibrahim dake gefshi yana fuskarta Rahama dake gefen Khausar, sai kuma Lalla Hafsat dake fuskantar Hakim sai kuma Lalla Khadijah, dake fuskantar Ashshe.
Ya zama kujeru uku ne babu kowa a kansu.
A hankali Lalla Khadijah ta miƙa tsaye tare da fara savin dinsu ɗaya bayan ɗaya duk da kowa da irin kalan abinda ta zuba mishi.
Abualeey masace mai haɗa da miyar daddageggen nama, sai kuma Modibbo da Ibarahim da ta zuba musu soyayyan dankali, da dege-dege da yaji naman kaza da kuma fararen tsokokin kifi sai kuma wadatacciyar albasar da take sa ɗan sauran gwaninta, sosai yajin yayi meɗeu a cikin domin Ibarahim na son yaji sosai sai kuma soyayyan kwai da yaji vegetables wani iri daddaɗan ƙamshi mai tada tsohuwar yunwa dege-dege ke gazawa, shi ta zubawa Khausar ma da Rahama, sai kuma ta sawa Ashshe da Lalla Hafsat masa da miyan ita kuma irin nasu Khausar Hakim ma Masa da miyarsun ta saka mishi.
Da sauri duk suka juyo jin muryar Dr Jameel da Zakariyya da kusan a tare suka shiga.
Bisa kujeru dake gefen Lalla Khadijah suka zauna bayan sun gama hausawa.
Suna ta zuba musu abincin.
Bismillahi suka kana duk suka fara ci.
Yayinda Khausar kuwa ke riƙe da fork din tana ɗan jujjuyawa tana ganin yadda miyar taji nama da kifi.
Da sauri Didi ta kalleta tare da cewa.
“Bismillah ɗiyata kici abinci”.
Murmushi ta ɗanyi tare da cewa.
“Toh”. Sai kuma ta ƙare mgnar tare da kallon Modibbo dayi loman forko, da sauri ya lumsh idanunsa, yana maijin ɗan-ɗanon abincin mai gamsarwa na ratsa mishi harce, sai dai kuma wani irin gigitaccen yajin da yaji yana gama gaba ɗaya jijiyoyin bakinshi manya da kananan. Allah ya sani shi dai yana masifar tsoron yaji.
Rahama ce ta kalleshi cikin murmushi tace.
“Yah Aleey yayi daɗiko nice nayi mana girkin da kaina”.
Cikin danne azabebben yajin dake gab da gigitashi yace.
“Yes kinci a baki tukuici”.
Sai kuma ya ɗan kalli Ibarahim dake cewa.
“Wow masha Allah ai ɗaɗi kam sosai ma, wannan girki ko yau aka aurar da ke ai bamu da haufi”.
Kai Khausar ta ɗan sunkuyar tare da soka dankali ɗaya ta haɗa da kifin kadan tasa a baki.
Wani irin zar taji yawun bakinta ya tsinke Allah ya sani tana da masifar cin yaji, shiyasa taji abinci yayi mata yadda takeso, sai dai duk da haka yajin ya fitini harshenta.
A hankali ta kalli Lalla Hafsat da kuma Lalla Khadijah dake cin abinci cike da kwanciyar hankali alamun suma manyan askarawa ne a cin yaji.
Sai kuma ta kalli Dr Jameel ta ɗan kalli Abualeey tare da jan plate gabansa ya fara cin masa da miyar Abualeey da aka sa mishi.
A hankali ta dawo da kallonta kan Modibbo da ya kai hannunsa kanshi yana ɗan shafawa tare da yin ƙasa da hannunsa har zuwa ƙeyarsa.
A hankali ta kuma kai loma na biyu wanda zuwa lokacin Ibrahim dasu Kalla Khadijah har sun kusa cin kaso ɗaya bisa ukun na abinci da ke kan plate dinsu.
Shi kuwa Modibbo cikin sanyi ya kai loma ta huɗu wanda tuni idanunsa sun cika da hawaye sabida azabar yaji daya fitini bakinsa.
A hankali ta tsaida idanunta kanshi tana mai tuno wasu kalaman Yah Jameel a ranar da sukayi rabuwar ƙarshe a cikin Shopping mall da suka shiga, a lokacin da yaga ta ɗauki robar dakekken yaji yace mata.
“Na lura kina son Yaji matuƙa, MJ ɗina kuma yana masifar tsoron yaji, kuma muddin yaga mutun yana son a yaba masa kan girkinsa to baya taɓa kushewa, kuma duk rintsi sai yaci dan shi mutum ne da baya son gwatsale mutum.
Shiyasa ko yaya bazai faɗaba, gwara ki sani dan kada kije kiyi ta zabga mishi yaji ki kashe min aminina.
Domin ko yaya bazai faɗa mikiba sai dai idan yaji ya gigita shi, zakiga, zaita shafa kanshi musamman ƙeyarsa kuma idanunshi zasu cika da hawaye, baza kuma su zuboba haka kuma zakiga duk sanyi zai fara zufa toh da zan kinga haka ki sani yajine ya gigitashi”.
Tuno hakanne yasa dawo da hankalinta kanshi ai kuwa zufan yakeyi duk da masifeffen sanyi da AC ke busa musu.