Sashe 78
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A can Side dinsu Asma'u kuwa.
Ita da Dija da Ummi dake waya da Mommy ne, bisa gada.
Cikin sanyi Ummin ta ɗan fesar da numfashi tare da juyowa ta kalli inda Asma'u da Dija ke kwance kana a hankali tace.
“Uhmmm ke dai bari Mommyn Khausar wlh Ni kaina, tunda muka dawo kai Khausy side ɗinta na gaza bacci, gaba ɗaya ita nake tuna, abinda baka san wahalarsa, bare da yanayin ƙarancin shekaru in dai an haɗa da na Modibbo ai Khausar yarinca tunda dudu fa yanzu suka cika shekaru sha tara.”
Cikin fesar da numfashi Mommy dake zaune bakin gadon tace.
“Wallahi kuwa Ummin Jameel, gaba ɗaya na kasa rumtsawa, bare ɗazu dana kirata, kuka tai ramin tana magoya wai dan Allah in roƙeki a bar mata Asma'u, itafa bata san kowaba a garin.
Wai da nace mata ai kowa da haka yake sabawa, sai cewa tayi. Mommy kamar bakya sona, kin san haka za'ace za'abarni ni kaɗai shine baki bani Raudat”.
Cikin sanyi Ummi tace.
“Ba komai in sha Allah, wlh Aliyu bazai tozarta zaɓin Jamilu naba, koda kuwa ace baya sonta, barema wlh Mommyn Khausar iyayen Modibbo masu mutumci ne, barema kuma ai zamu bar Innayi anan".
Cikin rauni da tausayi irin na iyayen a dararen da suka san an kaɗai ta yarsu da mijin aurenta, Mommy tace.
“Kayya Ummin Jameel wani sabawa ne, Khausar tayi da Innayi”.
Cikin bada ƙarfin guiwa Ummi tace.
“In sha Allah ba komai sai al'khairi”.
A hankali Mommy tace.
“Ɗazu muna waya da Haiydar ke cemin, wai ranar Jumma'a zaku dawo ko?".
Cikin sauƙe numfashi Ummi tace.
“Eh haka dai Abban Jameel ke cemin, amman shi Abban Jameel zai ɗan zauna sabida yanzu dole shi zai tsaya yayi aikin da ya turo Aliyun yayi. Kuma yacemin sune suka shirya komai na tafiyar namu, sun hanashi kashe ko asi”.
Cikin sanyi Mommy tace.
“Wato dai ya tabbata zaku dawo ku barmin Khausar na, can ita ɗaya, Khausar da shegen tsoro ace an barta a ƙasar da bata da kowa nata, da mijin da sonta yake ba, ko ya rayuwa zata juya mata, wlh Ummin Jameel wannan abufa yana damuna, dama ace Modibbo shine yace yana sonta da bazan shiga damuwa sosaiba”.
Cikin sanyi Ummi tace.
“Wallahi kada ki damu Khausar fa, ta samu karɓu sosai a masarautar Mouley”.
“Uhmm Toh Allah ya dawo daku lafiya”.
Mommy tace kana daga nan sukayi sallama.
Sai kuma ta miƙe ta shiga Bathroom tayi al'wala kana ta fito ta fara Nafila tare da roƙawa Khausar ɗinta samun aminci da konciyar hankali.
Ummi ma nafilan ta fara
Yayinda can cikin masarautar Mouley kuwa a side ɗin Didi.
Cikin sanyi Lalla Khadijah ta kalli Aunty Afreen wacce take ƴar Didice.
Cikin sanyi tace.
“Aunty Allah dai yasa ɗankun nan, ya bar ƴar mutane ta sarara, ta samu ta huta, domin na lura shi ɗin sai a hankali”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Ina ruwanki mutum da matarsa in banda sa ido”.
Dariya tayi tare da leƙa idon Lalla Hafsat da ke cewa.
“Gsky dai kam, Allah yasa ya barta, kinfa san in bai barta ba, muma ba hutawa za muyiba da wannan tsaraɓe-tsaraɓen al'dun wannan masarautar Mouley munnan, ni har ga Allah abin kunya yake bani da takaici”.
Cikin sauƙe numfashi Afree tace.
“Idan dai har ya kasance kamar kakanshi mahaifinmu to, babu shakka zai gyara muku masarautarku duk randa ya hau karagar mulki zai rabaku da duk wasu bauɗaɗɗun al'adu ya fuskantar daku addini, kamar yadda Sheykh Jabeer yayi gyara masarautar Joɗa”.
Cikin sauke numfashi Lalla Hafsat tace.
“Allah yasa haka”. Da Amin suka amsa, kana ita sukaci gaba hirarsu.
A can Side ɗin Khausar kuwa, cikin wahalallan baccin da takeyi a takure wanda ya jaza mata nauyin ƙirjine, ta ɗan mirgina sabida takuranda taji, cikin akasi tayi ƙasa rib kasan cewar a bakin gadon take.
Cikin wani irin raɗaɗin da ya game guiwowinta da suka sauƙa gib kan tayis ɗin ne, ta buɗe idanunta da sauri sai kuma ta sake rufesu da ƙarfi, tare da faɗin.
“Innalillahi wa innalillahi raji'un”.
Sabida ganin duhun daya mamaye ganinta, cikin gigita haɗi da kiɗima, ta miƙe tsaye tare da fara laluɓe-laluɓe tana kuma faɗin.
“Na shiga uku, innalillahi ba kowa ne a nan, wayyo Allah Ummi”.
Ta ƙarasa kiran Ummin da ƙarfi.
Sai kuma tayi saurin juyawa jin yadda ta buge kanta da jikin gini.
Kuka mai cike da tsoro ta saki tare da ci gaba da lalubawa, jin hannunta jikin labulena yasa tayi saurin yaye labulen, wanda na window ne, buɗe labulen da ta ɗanyi ne yasa ta ɗan samu hasken dake cikin correct ya ɗan haska ɗakin, da sauri ta juya ciki tana laluba ta inda wutan yake, amman ina bata ganoba sai dai tayi kamari da ƙofar fita, haka yasa ta fita da sauri, yayinda laffayar jikinta ke ja da ƙasa sabida ya warware.
Shi kuwa Modibbo tun farkawarta yaji muryarta, da motsinta, sai dai bashi da dama ko iko da ingin motsawa.
Sai karkarwar da jikinsa keyi daya ƙara tsananta. Hannunsa duka biyu ne, dafe da mararsa yayinda lips inshi suke rawa tamkar wanda aka cilla cikin dusar ƙanƙara, sabida rawar da ya tsananta har haƙoransa na dukan juna suna bada sautin gat-gat-gatt.
Ita kuwa Khausar da sassarfa ta fito falon, tana mai dannawa Ummi kira.
Dai-dai lokacin da ta iso tsakiyar falon kusa dashi laffayar ta zame tayi ƙasa ya harɗe sawunta da sauri ta daga ƙafarta da nufin ta zare samu ta cikin akasi kuma tayi tuntube da Modibbo dake kwance tsakiyar falon.
Luu ta tafi ta faɗa kanshi, ba zato ba tsammani ta jita bisa ruwan cikin mutum.
Ihu ta kurma da ƙarfi, wanda har saida Ummi dake Nafila ta jita, cikin sauri ta rumtse idanunta dan a zatonta, Modibbo ne ya rutsa Khausar ɗin a fili tace.
“Kai yaran zamani ka barta ta huta mana ko na mako ɗaya ne, ka bita a hankali”.
Ta kare mgnar cikin yin ƙasa da murya da kuma ci gaba da tasbihinta.
Shi kuwa Modibbo cikin tsakin gigitan yanayin da yake ciki ya jawota jikinshi tare da ruggume ta da masifan karfi.
Yah Salam wani irin karkarwa Khausar ta farayi kamar wacce za'a zarewa rai da ƙarfi ta daddage da nufin kurma wani ihun, sai kuma ta zazzaro idanunta waje, jin yasa tafin Hannunshi na dama ya rufe bakin nata.
Jin yadda take karkarwa da fesar da numfashi kamar mai shirin shiɗewane yasashi ɗan buɗe mata bakin.
Cikin sassayan murya ya buɗe baki murya na karkarwa yace.
“Meyasa baki da nitsuwa ne? Ki nitsumana!”.
Cike da razani tasa hannunta ta ɗan riƙe hannunsa tare da cewa.
“Waye ne kai ɗin?”.
Cikin fuzgo maganar a hankali yace.
“Nine”.
“Kai waye ɗin?”.
Cikin Lumshe ido yace.
“Mijinki ne Aliyu”.
Wani irin dogon numfashi taja mai gwaraye da tsoro da kuma sassauci murya a sarƙafe tace.
“Moddibbooooo”. Cikin wani irin sabon ruɗanin da muryarta da ɗumin jikinta ya jefa shi ne yace mata.
“Uhhhhhhhmmmmmm”.
Cikin sauri ta janye jikinta daga gareshi ya koma gefe kana murya a sarƙafe tace.
“Dan Allah ka tashi ka maidani wurinsu Ummin”.
Hannunshi yasa ya lalubo wayarta da ya kife bisa kujera, cikin sanyi ya danna hasken fuskar wayar, wanda haka yasa Khausar sakin sassayyan numfashi.
Shi kuwa cikin karkarwar da jikinsa keyi ya yunƙara da kyar ya miƙe zaune, tare da kunna tocin wayar kana ya ajiye, tare da zuba mata fitunannun idanunsa da suka sirance.
Da sauri tace.
“Dan Allah kayi haƙuri ka tashi ka kaini”.
Cikin sanyin murya dake can ƙasan maƙosjinsa yace.
“Ce miki akayi ni ɗan rakiyarki ne, ko ɗan aikenki”.
Da sauri ta turo baki tare da cewa.
“Toh Wlh ni dai bazan kwana a nan ba, cikin duhu”.
Da hannunshi na hagu yayi mata alamun ga hanya ai ki tafi mana.
Hannunshi na dama kuma Al'kebbar jikinsa ya gyara tare da rufe cinyoyinsa.
Ita kuwa cikin sanyi tace.
“Ai tsoro nakeji fita ni ɗaya”.
Kanshi ya sunkuyar ba tare da yace mata kimaiba sabida ganinta cikin shigar tayi masifar zaburar dashi.
Ita kuwa Khausar can gefe ta koma ta tsaya tana tura baki tare da mgna ƙasa-ƙasa.
“Wallahi babu inda su Ummi zasu tafi su barni a nan ƙafarsu ƙafata”.
Sai kuma tayi shiru jin, an kwaɗa kiran sallan forko a matsallacin Masarautar, sassayan numfashi ta fesar tare da cewa.
“Alhamdulillah”.
Shi kuwa Modibbo cikin ɓoye yanayin da yake ciki ya yunƙura ya miƙe tsaye tare da ɗaukar wayar tata, kana ya nufi hanyar fita da sauri tace.
“Ka bani wayata”.
Ba tare da ya juyo ya kalleta ba yace.
“Kina da ƙarfi ai kizo ki ƙwata”. Ya ida maganar tare da ficewa.
Yana shiga bedroom ɗinshi kai tsaye bathroom ya wuce, ruwan mai ɗan zafi ya sakarwa kansa daga bisani yayi al'wala kana ya fito tare da kmtsawa cikin wata tattausar jallabiya baƙa mai ɗan karen taushi, turare ya fesa, kana ya fara nafila.
Ita kuwa Khausar yana fita, ta kunna watan falon da sauri, kana ta shiga Bathroom dake falon tayi al'wala, laffayan ta naɗa a jikinta sannan ta fara nafila bisa Carpet din, jin an kira assalatune yasa tayi rak'atsinil fajir, kana rai ta tasbihi.
Shi kuwa Modibbo jin anyi assalatune yasa ya miƙe tare da ƙara fesa turaren ya fice zuwa masalaccin.
Jin an yada iƙamane kuma yasa Khausar miƙe itama takabbarta.
Bisa jagorancin Modibbo akayi salkan.
Koda aka idar da salla Modibbo bai tashiba hakama Ibraahim da Abualeey da kuma da yawa cikin manyan fada wasu karatun qura'an sukeyi wasu tasbihi.
Saida lokacin fitowar rana yayi kana suka riƙa yin nafila raka'a bibbiyu kamar yadda Manzon Allah ya kwaɗaitar damu, hadisi ne sahihi cewa duk wanda yayi sallan asuba, yaci gaba da zama'a wurin har rana ta fito kana yayi nafila raka'a biyu toh yaba da ladan aikin hajji.
Ita da Dija da Ummi dake waya da Mommy ne, bisa gada.
Cikin sanyi Ummin ta ɗan fesar da numfashi tare da juyowa ta kalli inda Asma'u da Dija ke kwance kana a hankali tace.
“Uhmmm ke dai bari Mommyn Khausar wlh Ni kaina, tunda muka dawo kai Khausy side ɗinta na gaza bacci, gaba ɗaya ita nake tuna, abinda baka san wahalarsa, bare da yanayin ƙarancin shekaru in dai an haɗa da na Modibbo ai Khausar yarinca tunda dudu fa yanzu suka cika shekaru sha tara.”
Cikin fesar da numfashi Mommy dake zaune bakin gadon tace.
“Wallahi kuwa Ummin Jameel, gaba ɗaya na kasa rumtsawa, bare ɗazu dana kirata, kuka tai ramin tana magoya wai dan Allah in roƙeki a bar mata Asma'u, itafa bata san kowaba a garin.
Wai da nace mata ai kowa da haka yake sabawa, sai cewa tayi. Mommy kamar bakya sona, kin san haka za'ace za'abarni ni kaɗai shine baki bani Raudat”.
Cikin sanyi Ummi tace.
“Ba komai in sha Allah, wlh Aliyu bazai tozarta zaɓin Jamilu naba, koda kuwa ace baya sonta, barema wlh Mommyn Khausar iyayen Modibbo masu mutumci ne, barema kuma ai zamu bar Innayi anan".
Cikin rauni da tausayi irin na iyayen a dararen da suka san an kaɗai ta yarsu da mijin aurenta, Mommy tace.
“Kayya Ummin Jameel wani sabawa ne, Khausar tayi da Innayi”.
Cikin bada ƙarfin guiwa Ummi tace.
“In sha Allah ba komai sai al'khairi”.
A hankali Mommy tace.
“Ɗazu muna waya da Haiydar ke cemin, wai ranar Jumma'a zaku dawo ko?".
Cikin sauƙe numfashi Ummi tace.
“Eh haka dai Abban Jameel ke cemin, amman shi Abban Jameel zai ɗan zauna sabida yanzu dole shi zai tsaya yayi aikin da ya turo Aliyun yayi. Kuma yacemin sune suka shirya komai na tafiyar namu, sun hanashi kashe ko asi”.
Cikin sanyi Mommy tace.
“Wato dai ya tabbata zaku dawo ku barmin Khausar na, can ita ɗaya, Khausar da shegen tsoro ace an barta a ƙasar da bata da kowa nata, da mijin da sonta yake ba, ko ya rayuwa zata juya mata, wlh Ummin Jameel wannan abufa yana damuna, dama ace Modibbo shine yace yana sonta da bazan shiga damuwa sosaiba”.
Cikin sanyi Ummi tace.
“Wallahi kada ki damu Khausar fa, ta samu karɓu sosai a masarautar Mouley”.
“Uhmm Toh Allah ya dawo daku lafiya”.
Mommy tace kana daga nan sukayi sallama.
Sai kuma ta miƙe ta shiga Bathroom tayi al'wala kana ta fito ta fara Nafila tare da roƙawa Khausar ɗinta samun aminci da konciyar hankali.
Ummi ma nafilan ta fara
Yayinda can cikin masarautar Mouley kuwa a side ɗin Didi.
Cikin sanyi Lalla Khadijah ta kalli Aunty Afreen wacce take ƴar Didice.
Cikin sanyi tace.
“Aunty Allah dai yasa ɗankun nan, ya bar ƴar mutane ta sarara, ta samu ta huta, domin na lura shi ɗin sai a hankali”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Ina ruwanki mutum da matarsa in banda sa ido”.
Dariya tayi tare da leƙa idon Lalla Hafsat da ke cewa.
“Gsky dai kam, Allah yasa ya barta, kinfa san in bai barta ba, muma ba hutawa za muyiba da wannan tsaraɓe-tsaraɓen al'dun wannan masarautar Mouley munnan, ni har ga Allah abin kunya yake bani da takaici”.
Cikin sauƙe numfashi Afree tace.
“Idan dai har ya kasance kamar kakanshi mahaifinmu to, babu shakka zai gyara muku masarautarku duk randa ya hau karagar mulki zai rabaku da duk wasu bauɗaɗɗun al'adu ya fuskantar daku addini, kamar yadda Sheykh Jabeer yayi gyara masarautar Joɗa”.
Cikin sauke numfashi Lalla Hafsat tace.
“Allah yasa haka”. Da Amin suka amsa, kana ita sukaci gaba hirarsu.
A can Side ɗin Khausar kuwa, cikin wahalallan baccin da takeyi a takure wanda ya jaza mata nauyin ƙirjine, ta ɗan mirgina sabida takuranda taji, cikin akasi tayi ƙasa rib kasan cewar a bakin gadon take.
Cikin wani irin raɗaɗin da ya game guiwowinta da suka sauƙa gib kan tayis ɗin ne, ta buɗe idanunta da sauri sai kuma ta sake rufesu da ƙarfi, tare da faɗin.
“Innalillahi wa innalillahi raji'un”.
Sabida ganin duhun daya mamaye ganinta, cikin gigita haɗi da kiɗima, ta miƙe tsaye tare da fara laluɓe-laluɓe tana kuma faɗin.
“Na shiga uku, innalillahi ba kowa ne a nan, wayyo Allah Ummi”.
Ta ƙarasa kiran Ummin da ƙarfi.
Sai kuma tayi saurin juyawa jin yadda ta buge kanta da jikin gini.
Kuka mai cike da tsoro ta saki tare da ci gaba da lalubawa, jin hannunta jikin labulena yasa tayi saurin yaye labulen, wanda na window ne, buɗe labulen da ta ɗanyi ne yasa ta ɗan samu hasken dake cikin correct ya ɗan haska ɗakin, da sauri ta juya ciki tana laluba ta inda wutan yake, amman ina bata ganoba sai dai tayi kamari da ƙofar fita, haka yasa ta fita da sauri, yayinda laffayar jikinta ke ja da ƙasa sabida ya warware.
Shi kuwa Modibbo tun farkawarta yaji muryarta, da motsinta, sai dai bashi da dama ko iko da ingin motsawa.
Sai karkarwar da jikinsa keyi daya ƙara tsananta. Hannunsa duka biyu ne, dafe da mararsa yayinda lips inshi suke rawa tamkar wanda aka cilla cikin dusar ƙanƙara, sabida rawar da ya tsananta har haƙoransa na dukan juna suna bada sautin gat-gat-gatt.
Ita kuwa Khausar da sassarfa ta fito falon, tana mai dannawa Ummi kira.
Dai-dai lokacin da ta iso tsakiyar falon kusa dashi laffayar ta zame tayi ƙasa ya harɗe sawunta da sauri ta daga ƙafarta da nufin ta zare samu ta cikin akasi kuma tayi tuntube da Modibbo dake kwance tsakiyar falon.
Luu ta tafi ta faɗa kanshi, ba zato ba tsammani ta jita bisa ruwan cikin mutum.
Ihu ta kurma da ƙarfi, wanda har saida Ummi dake Nafila ta jita, cikin sauri ta rumtse idanunta dan a zatonta, Modibbo ne ya rutsa Khausar ɗin a fili tace.
“Kai yaran zamani ka barta ta huta mana ko na mako ɗaya ne, ka bita a hankali”.
Ta kare mgnar cikin yin ƙasa da murya da kuma ci gaba da tasbihinta.
Shi kuwa Modibbo cikin tsakin gigitan yanayin da yake ciki ya jawota jikinshi tare da ruggume ta da masifan karfi.
Yah Salam wani irin karkarwa Khausar ta farayi kamar wacce za'a zarewa rai da ƙarfi ta daddage da nufin kurma wani ihun, sai kuma ta zazzaro idanunta waje, jin yasa tafin Hannunshi na dama ya rufe bakin nata.
Jin yadda take karkarwa da fesar da numfashi kamar mai shirin shiɗewane yasashi ɗan buɗe mata bakin.
Cikin sassayan murya ya buɗe baki murya na karkarwa yace.
“Meyasa baki da nitsuwa ne? Ki nitsumana!”.
Cike da razani tasa hannunta ta ɗan riƙe hannunsa tare da cewa.
“Waye ne kai ɗin?”.
Cikin fuzgo maganar a hankali yace.
“Nine”.
“Kai waye ɗin?”.
Cikin Lumshe ido yace.
“Mijinki ne Aliyu”.
Wani irin dogon numfashi taja mai gwaraye da tsoro da kuma sassauci murya a sarƙafe tace.
“Moddibbooooo”. Cikin wani irin sabon ruɗanin da muryarta da ɗumin jikinta ya jefa shi ne yace mata.
“Uhhhhhhhmmmmmm”.
Cikin sauri ta janye jikinta daga gareshi ya koma gefe kana murya a sarƙafe tace.
“Dan Allah ka tashi ka maidani wurinsu Ummin”.
Hannunshi yasa ya lalubo wayarta da ya kife bisa kujera, cikin sanyi ya danna hasken fuskar wayar, wanda haka yasa Khausar sakin sassayyan numfashi.
Shi kuwa cikin karkarwar da jikinsa keyi ya yunƙara da kyar ya miƙe zaune, tare da kunna tocin wayar kana ya ajiye, tare da zuba mata fitunannun idanunsa da suka sirance.
Da sauri tace.
“Dan Allah kayi haƙuri ka tashi ka kaini”.
Cikin sanyin murya dake can ƙasan maƙosjinsa yace.
“Ce miki akayi ni ɗan rakiyarki ne, ko ɗan aikenki”.
Da sauri ta turo baki tare da cewa.
“Toh Wlh ni dai bazan kwana a nan ba, cikin duhu”.
Da hannunshi na hagu yayi mata alamun ga hanya ai ki tafi mana.
Hannunshi na dama kuma Al'kebbar jikinsa ya gyara tare da rufe cinyoyinsa.
Ita kuwa cikin sanyi tace.
“Ai tsoro nakeji fita ni ɗaya”.
Kanshi ya sunkuyar ba tare da yace mata kimaiba sabida ganinta cikin shigar tayi masifar zaburar dashi.
Ita kuwa Khausar can gefe ta koma ta tsaya tana tura baki tare da mgna ƙasa-ƙasa.
“Wallahi babu inda su Ummi zasu tafi su barni a nan ƙafarsu ƙafata”.
Sai kuma tayi shiru jin, an kwaɗa kiran sallan forko a matsallacin Masarautar, sassayan numfashi ta fesar tare da cewa.
“Alhamdulillah”.
Shi kuwa Modibbo cikin ɓoye yanayin da yake ciki ya yunƙura ya miƙe tsaye tare da ɗaukar wayar tata, kana ya nufi hanyar fita da sauri tace.
“Ka bani wayata”.
Ba tare da ya juyo ya kalleta ba yace.
“Kina da ƙarfi ai kizo ki ƙwata”. Ya ida maganar tare da ficewa.
Yana shiga bedroom ɗinshi kai tsaye bathroom ya wuce, ruwan mai ɗan zafi ya sakarwa kansa daga bisani yayi al'wala kana ya fito tare da kmtsawa cikin wata tattausar jallabiya baƙa mai ɗan karen taushi, turare ya fesa, kana ya fara nafila.
Ita kuwa Khausar yana fita, ta kunna watan falon da sauri, kana ta shiga Bathroom dake falon tayi al'wala, laffayan ta naɗa a jikinta sannan ta fara nafila bisa Carpet din, jin an kira assalatune yasa tayi rak'atsinil fajir, kana rai ta tasbihi.
Shi kuwa Modibbo jin anyi assalatune yasa ya miƙe tare da ƙara fesa turaren ya fice zuwa masalaccin.
Jin an yada iƙamane kuma yasa Khausar miƙe itama takabbarta.
Bisa jagorancin Modibbo akayi salkan.
Koda aka idar da salla Modibbo bai tashiba hakama Ibraahim da Abualeey da kuma da yawa cikin manyan fada wasu karatun qura'an sukeyi wasu tasbihi.
Saida lokacin fitowar rana yayi kana suka riƙa yin nafila raka'a bibbiyu kamar yadda Manzon Allah ya kwaɗaitar damu, hadisi ne sahihi cewa duk wanda yayi sallan asuba, yaci gaba da zama'a wurin har rana ta fito kana yayi nafila raka'a biyu toh yaba da ladan aikin hajji.