Sashe 34
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin sauƙe numfashi Malam Arɗo yace.
“Toh Alhamdulillah gamu da gishiri da goro na tambayar mu na forko muka zo,".
Sai kuma duk suka juyo suka kalli Malam Liman sayi gyaran murya tare fuskantarsu da kyau cikin kamala da dottaku yace.
“Tunda ga yanayin yadda abin ya kasance, mu shammaci Adda Nana, domin bata da alƙibila yanzu tace ta yarda zuwa anjima zata iya cewa ta fasa, don haka mu ɗaura auren nan yanzu-yanzu ana da goron da kuka kawo in dai akwai sadaki a hannunsu tunda ga waliyan yaro ga kuma nata waliyan”.
Ya ƙare mgnar tare da yin ƙasa da murya gudun kada Hajja Nana taji mgnar.
Cikin tsanananin mamaki da farin ciki mara misaltawa Abba Jameel yasa hannunshi cikin aljihunsa jiki na rawa ya zaro sabbin kuɗin yar dubu dubu wanda ya dauko dan yin hisani. Bandir ɗaya ya ajiye a tsakiyarsu wanda har jikinsa na rawa dan farin ciki yace.
“Gashi ina nemawa Aliyu Youseep Muhammad Mouley auren Khausar bisa sadaki dubu ɗari”.
Da sauri Bappa Jimeta ya gyara zamanshi tare da cewa.
“Na bawa Aliyu Youseep Muhammad Mouley auren ƴata Fatima Usman Abubakar Leewal bisa sadaki dubu ɗari.”
Cikin tsananin jin daɗin wannan al'amari da yazo musu da sauƙin aka ɗauka Auren Khausar da Modibbo a yau Litinin a cikin rugar Jauro yaya bisa shaidu Lamiɗo, Malam Arɗo, Malam Liman, da sauran ƙananan Hajja Nana baki ɗaya.
Bayan sun gama gudanar da ɗaurin auren kamar yadda shari'ar Muslunci ta tsara.
Cike da gamsuwa haɗin da tsananin jin daɗin ɗaurin auren Baffa Jimeta yace.
“Toh ba matsala Insha Allah duk abinda ake ciki zan gayawa Hajja Nana kuma zan taushi zuciyarta”.
Sai kuma duk suka juyo suka kalli Hajja Nana dake fitowa daga cikin rumfarta tana mai cewa.
“Uhmmm ta yara kyau take bata ƙarko, ai duk abinda kuke cewa dayi ina jinku badai kun ɗaya aurenba, toh ai hikenan maji magani”.
Cikin Sauri suka kuma kalli juna, ayi mace kunne kamar na maciji duk ƙantar sauti sai taji.
Sai kuma suka maida kallonsu kam Malam Liman dake cewa.
“Toh kisanya albarka kawai”.
Kai ta gyaɗa cike da takaici tace.
“Hmmm Allah ya sanya al'khairi Allah yasa yadda muka ɗauki mgnar marigayi da mahimmanci shima Modibbo a ɗauki mgnar da gsky”.
Bata jira cewarsu ba kuma ta juya cikin ɗakin,
Ida ta zubawa Khausar da tun lokacin da taji Hajja Nana nacewa badai kun ɗaura aurenba ta daskare a zaune, yayinda Mommy mgnar ta daki zuciyarta, dan batayi zaton abin da gaggawa haka ba. Sai kuma duk suka kalli Hajja Nana dake cewa.
“Wlh kinyi asarar ƙuruciyarki da kyanki ji yadda aka ɗaura aurenki kamar na bazawara mara gata”.
Zuwa yanzu Khausar kam bazata iya fahimtar kalaman Hajja Nana ba bare ta bata amsa. Ita kanta Mommy abin ya sata tafiya dogon nazari.
A can waje kuma
Anutse Lamiɗo ya gyara zama kana yace.
“Toh Alhamdulillah dama kwanan ake batun auren Amina nanda kwana goma, tunda an auren Khausar za'a haɗa bikin ayishi lokaci ɗaya, kana akai ko wacce gidan mijinta”.
Kusan a tare duk sukace.
“Allah ya kaimu lokacin”.
Amin Ya amsa tare daci gaba da cewa.
“Insha Allah zuwa gobe ko jibi Insha Allah zan dawo in muyi magana mahaifiyar yarinya”.
Nan dai suka gaba da tsastsara duk yadda abin zai kasance.
Sai Misalin ƙarfe biyar suka bar Jauro yaya ahanya sukayi sallar maghariba sai gab Isha'i suka isa gida.
Kasancewar ranan girkin Hajiya Bunayya ne yasa kai tsaye Mommy ta wuce Sashen ta tare da Khausar wacce take tafiya tamkar kazar da ƙwai ya fashewa, domin jin kanta take tamkar wacce aka rufe da ɗanyen fatan rago, wasu abubuwa na musamman ne ke yawo a jiki da zuciyarta ita kanta ta rasa yanayin da take ciki, kawai dai ta tsinci kanta da rayuwa da Modibbo a cikin zuciyata tun lokacin da taji wai an ɗaura aurensu.
Suna shiga kai tsaye ɗalibta ta wuce, duk da tsalle da Raudat keyi na ganinta ta gaza yi mata mgn.
Sai Mommy ce data ruggume Raudat ɗin.
Ita kuwa Khausar a hankali ta faɗa bisa gafonta, tare da rumtse idanunta da karfi.
Sai kuma ta buɗesu ganin fuskar Modibbo a ranar da sukayi robuwar ƙarshe jujjuya idonta tayi kamar yadda tayi mishi a lokacin, sai kuma ta lumshesu jin wasu tafasassun hawaye dake kwaranyo mata ba ƙaƙƙautawa.
Kamar a Film haka yanayin da suke rayuwa dashi a makaranta ya fara dawo mata, one by one, har zuwa ranar da suka kasance a mota, haka nan taji wani murmushin da batasan manufarsaba ya kumce mata, wanda kuma ya korowa hawayen da bata san ya kubce mata da kukaba.
Sai kuma ta saki sassayyan kuka jin Mommy ta zauna kusa da ita tana mai cewa.
“Toh kuma kukan me kikeyi Fatima”.
Ta ƙare mgnar da kiran asalin sunanta wanda bata cika kiranta da shiba.
Ita kuwa Khausar cikin ci gaba da sassayan kukan tace.
“Mommy kinaji fa wai sun ɗaura auren”.
Jawota jikinta Mommy da hawaye zubomata tayi tare da ɗaura kanta bisa cinyarta tana mai danne kukanta tace.
“Ba komai Mamana kiyi shiru, ai ba yau za'a tafi da keba ki share hawayenki, addu'arta bazata bari ki muzantaba a gidan aurenki”.
Ta ƙare mgnar tana share mata hawaye, daga nan taci gaba tausarta da kwantar mata da hankali dan ta lura gaba ɗaya ta ɗimauce abin ya daki zuciyarta ya kauda nitsuwarta.
Washegari Da safe Kai tsaye Bedroom din Mommy Lamiɗo ya shiga tare da yi mata bayanin duk yanda sukayi a Jauro yaya bayan sun dawo Sallar La'asar da batun auren da suka dauran.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe cikin sanyi ta ɗago kai tare da kallon Lamiɗo kana tace.
“Toh yanzu har an ɗaura Auren kuma ba jan lokacin asan yaron yana sonta, sannan kuma ace za ayi bikin cikin ƙankanin lokaci haka?”.
Ta ƙare mgnar cije da rauni.
Jinjina kai Abba yayi yana kallon yanayinta yace.
“Toh me za ajira Aysha ai abune na wasiyya kuma akwai damar yi sannan Already Khausar ta gama Secondary kawai tayi Aurenta tunda Alh Bashir yace a Marocco zasu zauna kinga shida kanshi yace zai kaita wurin mijinta”.
Kallonsa kawai Mommy keyi sabida tama rasa abincewa.
Ahankali Abba ya cigaba da cewa.
“Saboda ya lura yaron bayan son zaman nan sannan yana so yabar masa ragamar Company ahannunsa kinga idan sunje can sai ta cigaba da karatunta acan tunda dama yanayin makarantar su akwai cikekkiyar larabci kinga zata iya karatu a can, ta kuma yi zaman aurenta cikin aminci”.
Sunkuyar da kai Mommy tayi tana wasa da yatsun hannunta yayinda tausayin yarta yasa hawaye cika mata idanu A hankali tace.
“Kuma ba wanda ta sani a canfa, ya zatayi”.
Abba ya cigaba da cewa.
“Kada ki damu, ɗan naji Abban Jameel yace in Malam Ahmad ya yarda da rakiyar Ummin Jameel da Asma'u zasuje, ga kuma Hajia Bunayyah itama zan biya mata su kaita tare”.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe kana tace.
“Hmmm abin ne naga kamar anyi sa da gaggawa Khausar fa yarinya ce, wlh tsoron yaronan ne fal zuciyarta jiya kwana tayi batayi bacciba”.
Murmushi Lamiɗo yayi tare da riƙe tafin hannunta acikin nasa yace.
“A ba wani yarinta aciki ai Insha Allah komai zai tafi dai-dai zakiyi alfari da Aurenta da Moddibo ke lokacin da aka aurar dake ai bakima kaita shekaruba, mijinta kuma bar tunanin tana tsoronshi a a bata sonshi ke dai ku zuba ido zakusha mamakin yadda al'amarin zai kance in dai Khausar ta ɗauke ki ai kiyi shiru kawai yaro zayi mubaya'a”.
Ya ƙare mgnar da cikin sigar wasa da son kwantar mata da hankali.
Kai ta gyaɗa kana cikin sanyi tace.
“Allah yasa”.
Amin yace tare da miƙewa ya fita.
Acan ɓangaren Ummi kuwa bayan Sallar Azahar bayan Malam Ahmad ya dawo daga gidan Abba ya zayyanewa Ummi duk yanda Abba ya faɗa masa.
Ajiyar zuciya mai nauyi Ummi ta sauƙe tare da fesar da numfashi cikin tsananin jin daɗin kana tace.
“Alhamdulillah yau dai burin Jameeluna ya cika sannan wasiyyar daya bari ta kasance kai baki daɗin wannan al'amarin”.
Jinjina kai Malam Ahmad yayi cike da farin ciki yace.
“insha Allah”.
Numfashi Ummi ta fesar kana tace.
“Toh Allah ya tabbatar mana da alkhairi ya kaimu lokacin tafiyar, shiru zanyi bazan gayawa Asma'u ba tukun sai naga yadda Khausar ɗin ta nufeta da mgnar”.
Ameen ya amsa kana ya fice.
Ahankali Asma'u ta fito daga Bedroom tare da kallon Ummi kana tace.
“Ummi wai maganar me naji kuna yi kamar batun Aure?”.
Kai Ummi ta jinjina da alamun farin ciki afuskarta tace.
“Hmmm”. Sai kuma tayi shiru, ita kuwa Asma'u cikin son tabbatar da abinda kunnuwanta suka jiyemata cike da kaɗuwa tace.
“Dan Allah Ummi ki gaya min na tuba”.
Cikin tsanananin jin dadin ɗaya kasa biya a saman fuskarta tace.
“Eh maganar Auren Moddibo mukeyi”.
Zare ido Asma'u tayi kana tace.
“Ummi Yaya Moddibo zaiyi Aurene?”.
Jinjina kai Ummi tayi tana kallonta tace.
“Eh yanayi Aure dai”.
Murmushi Asma'u tayi cike da farin ciki tace.
“Ummi Wacece matar?”.
Ummi na murmushi tace.
“Aminiyar kice matar”.
Asma'u kuwa cike da matsanancin mamaki da al'ajabi ta zare Idanunta waje kana tace.
“Khausar!?”.
Kai Ummi ta jinjina tare da faɗin.
“Tabbas kuwa da izinin Ubangiji Itace”.
Tafa hannu tayi tare da buga still da Mamaki da kuma al'ajabi tace.
_“Lahailah ha Illallahu Muhammad Rasulullahi (S.A.W)”_ Yah Moddibo da Khausar.
Kallon yanda ta zare ido da sallami Ummi tayi kana tace.
“Haƙƙun kuwa dan tuni an ɗaurama”.
Dafe kunci Asma'u tayi da matsanancin mamaki gani da kaɗuwa ɗoki da bai sake taba tace.
“Dan Allah Ummi yaushe aka fara wannan maganar?”.
Hannunta Ummi ta riƙe tare da zaunar da ita agefenta yace.
“Ki nutsu mana Asma'u me wannan kamar wanda akace an haɗa Auren mutum da Dodo!?”.
“Toh Alhamdulillah gamu da gishiri da goro na tambayar mu na forko muka zo,".
Sai kuma duk suka juyo suka kalli Malam Liman sayi gyaran murya tare fuskantarsu da kyau cikin kamala da dottaku yace.
“Tunda ga yanayin yadda abin ya kasance, mu shammaci Adda Nana, domin bata da alƙibila yanzu tace ta yarda zuwa anjima zata iya cewa ta fasa, don haka mu ɗaura auren nan yanzu-yanzu ana da goron da kuka kawo in dai akwai sadaki a hannunsu tunda ga waliyan yaro ga kuma nata waliyan”.
Ya ƙare mgnar tare da yin ƙasa da murya gudun kada Hajja Nana taji mgnar.
Cikin tsanananin mamaki da farin ciki mara misaltawa Abba Jameel yasa hannunshi cikin aljihunsa jiki na rawa ya zaro sabbin kuɗin yar dubu dubu wanda ya dauko dan yin hisani. Bandir ɗaya ya ajiye a tsakiyarsu wanda har jikinsa na rawa dan farin ciki yace.
“Gashi ina nemawa Aliyu Youseep Muhammad Mouley auren Khausar bisa sadaki dubu ɗari”.
Da sauri Bappa Jimeta ya gyara zamanshi tare da cewa.
“Na bawa Aliyu Youseep Muhammad Mouley auren ƴata Fatima Usman Abubakar Leewal bisa sadaki dubu ɗari.”
Cikin tsananin jin daɗin wannan al'amari da yazo musu da sauƙin aka ɗauka Auren Khausar da Modibbo a yau Litinin a cikin rugar Jauro yaya bisa shaidu Lamiɗo, Malam Arɗo, Malam Liman, da sauran ƙananan Hajja Nana baki ɗaya.
Bayan sun gama gudanar da ɗaurin auren kamar yadda shari'ar Muslunci ta tsara.
Cike da gamsuwa haɗin da tsananin jin daɗin ɗaurin auren Baffa Jimeta yace.
“Toh ba matsala Insha Allah duk abinda ake ciki zan gayawa Hajja Nana kuma zan taushi zuciyarta”.
Sai kuma duk suka juyo suka kalli Hajja Nana dake fitowa daga cikin rumfarta tana mai cewa.
“Uhmmm ta yara kyau take bata ƙarko, ai duk abinda kuke cewa dayi ina jinku badai kun ɗaya aurenba, toh ai hikenan maji magani”.
Cikin Sauri suka kuma kalli juna, ayi mace kunne kamar na maciji duk ƙantar sauti sai taji.
Sai kuma suka maida kallonsu kam Malam Liman dake cewa.
“Toh kisanya albarka kawai”.
Kai ta gyaɗa cike da takaici tace.
“Hmmm Allah ya sanya al'khairi Allah yasa yadda muka ɗauki mgnar marigayi da mahimmanci shima Modibbo a ɗauki mgnar da gsky”.
Bata jira cewarsu ba kuma ta juya cikin ɗakin,
Ida ta zubawa Khausar da tun lokacin da taji Hajja Nana nacewa badai kun ɗaura aurenba ta daskare a zaune, yayinda Mommy mgnar ta daki zuciyarta, dan batayi zaton abin da gaggawa haka ba. Sai kuma duk suka kalli Hajja Nana dake cewa.
“Wlh kinyi asarar ƙuruciyarki da kyanki ji yadda aka ɗaura aurenki kamar na bazawara mara gata”.
Zuwa yanzu Khausar kam bazata iya fahimtar kalaman Hajja Nana ba bare ta bata amsa. Ita kanta Mommy abin ya sata tafiya dogon nazari.
A can waje kuma
Anutse Lamiɗo ya gyara zama kana yace.
“Toh Alhamdulillah dama kwanan ake batun auren Amina nanda kwana goma, tunda an auren Khausar za'a haɗa bikin ayishi lokaci ɗaya, kana akai ko wacce gidan mijinta”.
Kusan a tare duk sukace.
“Allah ya kaimu lokacin”.
Amin Ya amsa tare daci gaba da cewa.
“Insha Allah zuwa gobe ko jibi Insha Allah zan dawo in muyi magana mahaifiyar yarinya”.
Nan dai suka gaba da tsastsara duk yadda abin zai kasance.
Sai Misalin ƙarfe biyar suka bar Jauro yaya ahanya sukayi sallar maghariba sai gab Isha'i suka isa gida.
Kasancewar ranan girkin Hajiya Bunayya ne yasa kai tsaye Mommy ta wuce Sashen ta tare da Khausar wacce take tafiya tamkar kazar da ƙwai ya fashewa, domin jin kanta take tamkar wacce aka rufe da ɗanyen fatan rago, wasu abubuwa na musamman ne ke yawo a jiki da zuciyarta ita kanta ta rasa yanayin da take ciki, kawai dai ta tsinci kanta da rayuwa da Modibbo a cikin zuciyata tun lokacin da taji wai an ɗaura aurensu.
Suna shiga kai tsaye ɗalibta ta wuce, duk da tsalle da Raudat keyi na ganinta ta gaza yi mata mgn.
Sai Mommy ce data ruggume Raudat ɗin.
Ita kuwa Khausar a hankali ta faɗa bisa gafonta, tare da rumtse idanunta da karfi.
Sai kuma ta buɗesu ganin fuskar Modibbo a ranar da sukayi robuwar ƙarshe jujjuya idonta tayi kamar yadda tayi mishi a lokacin, sai kuma ta lumshesu jin wasu tafasassun hawaye dake kwaranyo mata ba ƙaƙƙautawa.
Kamar a Film haka yanayin da suke rayuwa dashi a makaranta ya fara dawo mata, one by one, har zuwa ranar da suka kasance a mota, haka nan taji wani murmushin da batasan manufarsaba ya kumce mata, wanda kuma ya korowa hawayen da bata san ya kubce mata da kukaba.
Sai kuma ta saki sassayyan kuka jin Mommy ta zauna kusa da ita tana mai cewa.
“Toh kuma kukan me kikeyi Fatima”.
Ta ƙare mgnar da kiran asalin sunanta wanda bata cika kiranta da shiba.
Ita kuwa Khausar cikin ci gaba da sassayan kukan tace.
“Mommy kinaji fa wai sun ɗaura auren”.
Jawota jikinta Mommy da hawaye zubomata tayi tare da ɗaura kanta bisa cinyarta tana mai danne kukanta tace.
“Ba komai Mamana kiyi shiru, ai ba yau za'a tafi da keba ki share hawayenki, addu'arta bazata bari ki muzantaba a gidan aurenki”.
Ta ƙare mgnar tana share mata hawaye, daga nan taci gaba tausarta da kwantar mata da hankali dan ta lura gaba ɗaya ta ɗimauce abin ya daki zuciyarta ya kauda nitsuwarta.
Washegari Da safe Kai tsaye Bedroom din Mommy Lamiɗo ya shiga tare da yi mata bayanin duk yanda sukayi a Jauro yaya bayan sun dawo Sallar La'asar da batun auren da suka dauran.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe cikin sanyi ta ɗago kai tare da kallon Lamiɗo kana tace.
“Toh yanzu har an ɗaura Auren kuma ba jan lokacin asan yaron yana sonta, sannan kuma ace za ayi bikin cikin ƙankanin lokaci haka?”.
Ta ƙare mgnar cije da rauni.
Jinjina kai Abba yayi yana kallon yanayinta yace.
“Toh me za ajira Aysha ai abune na wasiyya kuma akwai damar yi sannan Already Khausar ta gama Secondary kawai tayi Aurenta tunda Alh Bashir yace a Marocco zasu zauna kinga shida kanshi yace zai kaita wurin mijinta”.
Kallonsa kawai Mommy keyi sabida tama rasa abincewa.
Ahankali Abba ya cigaba da cewa.
“Saboda ya lura yaron bayan son zaman nan sannan yana so yabar masa ragamar Company ahannunsa kinga idan sunje can sai ta cigaba da karatunta acan tunda dama yanayin makarantar su akwai cikekkiyar larabci kinga zata iya karatu a can, ta kuma yi zaman aurenta cikin aminci”.
Sunkuyar da kai Mommy tayi tana wasa da yatsun hannunta yayinda tausayin yarta yasa hawaye cika mata idanu A hankali tace.
“Kuma ba wanda ta sani a canfa, ya zatayi”.
Abba ya cigaba da cewa.
“Kada ki damu, ɗan naji Abban Jameel yace in Malam Ahmad ya yarda da rakiyar Ummin Jameel da Asma'u zasuje, ga kuma Hajia Bunayyah itama zan biya mata su kaita tare”.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe kana tace.
“Hmmm abin ne naga kamar anyi sa da gaggawa Khausar fa yarinya ce, wlh tsoron yaronan ne fal zuciyarta jiya kwana tayi batayi bacciba”.
Murmushi Lamiɗo yayi tare da riƙe tafin hannunta acikin nasa yace.
“A ba wani yarinta aciki ai Insha Allah komai zai tafi dai-dai zakiyi alfari da Aurenta da Moddibo ke lokacin da aka aurar dake ai bakima kaita shekaruba, mijinta kuma bar tunanin tana tsoronshi a a bata sonshi ke dai ku zuba ido zakusha mamakin yadda al'amarin zai kance in dai Khausar ta ɗauke ki ai kiyi shiru kawai yaro zayi mubaya'a”.
Ya ƙare mgnar da cikin sigar wasa da son kwantar mata da hankali.
Kai ta gyaɗa kana cikin sanyi tace.
“Allah yasa”.
Amin yace tare da miƙewa ya fita.
Acan ɓangaren Ummi kuwa bayan Sallar Azahar bayan Malam Ahmad ya dawo daga gidan Abba ya zayyanewa Ummi duk yanda Abba ya faɗa masa.
Ajiyar zuciya mai nauyi Ummi ta sauƙe tare da fesar da numfashi cikin tsananin jin daɗin kana tace.
“Alhamdulillah yau dai burin Jameeluna ya cika sannan wasiyyar daya bari ta kasance kai baki daɗin wannan al'amarin”.
Jinjina kai Malam Ahmad yayi cike da farin ciki yace.
“insha Allah”.
Numfashi Ummi ta fesar kana tace.
“Toh Allah ya tabbatar mana da alkhairi ya kaimu lokacin tafiyar, shiru zanyi bazan gayawa Asma'u ba tukun sai naga yadda Khausar ɗin ta nufeta da mgnar”.
Ameen ya amsa kana ya fice.
Ahankali Asma'u ta fito daga Bedroom tare da kallon Ummi kana tace.
“Ummi wai maganar me naji kuna yi kamar batun Aure?”.
Kai Ummi ta jinjina da alamun farin ciki afuskarta tace.
“Hmmm”. Sai kuma tayi shiru, ita kuwa Asma'u cikin son tabbatar da abinda kunnuwanta suka jiyemata cike da kaɗuwa tace.
“Dan Allah Ummi ki gaya min na tuba”.
Cikin tsanananin jin dadin ɗaya kasa biya a saman fuskarta tace.
“Eh maganar Auren Moddibo mukeyi”.
Zare ido Asma'u tayi kana tace.
“Ummi Yaya Moddibo zaiyi Aurene?”.
Jinjina kai Ummi tayi tana kallonta tace.
“Eh yanayi Aure dai”.
Murmushi Asma'u tayi cike da farin ciki tace.
“Ummi Wacece matar?”.
Ummi na murmushi tace.
“Aminiyar kice matar”.
Asma'u kuwa cike da matsanancin mamaki da al'ajabi ta zare Idanunta waje kana tace.
“Khausar!?”.
Kai Ummi ta jinjina tare da faɗin.
“Tabbas kuwa da izinin Ubangiji Itace”.
Tafa hannu tayi tare da buga still da Mamaki da kuma al'ajabi tace.
_“Lahailah ha Illallahu Muhammad Rasulullahi (S.A.W)”_ Yah Moddibo da Khausar.
Kallon yanda ta zare ido da sallami Ummi tayi kana tace.
“Haƙƙun kuwa dan tuni an ɗaurama”.
Dafe kunci Asma'u tayi da matsanancin mamaki gani da kaɗuwa ɗoki da bai sake taba tace.
“Dan Allah Ummi yaushe aka fara wannan maganar?”.
Hannunta Ummi ta riƙe tare da zaunar da ita agefenta yace.
“Ki nutsu mana Asma'u me wannan kamar wanda akace an haɗa Auren mutum da Dodo!?”.