Sashe 31
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Akuma dai-dai lokacin Malam Arɗo,Malam Ahmad da Abba ne zaune afalon Lamiɗo bayan sun gaisa sannan suka yimasa jawabi kan cewa sunji shiru shiru bai sake neman suba yasa suka dawo.
Anutse Lamiɗo ya gyara zama cike da dattako yace.
“Badamuwa Insha Allahu dama nima ina shirin zan ne meku ɗin saboda bani da ikon bada ita akaran kaina amma munyi magana da Baffan yarinya yau ɗin nan ma yazo daga can Adamawa zai nemi sahalewar kakar yarinya”.
Ajiyar zuciya suka sauƙe atare Kallonsu Lamiɗo yayi kana ya cigaba da cewa.
“Dake Itace taso kawo tangarɗa acikin al'amarin amma yace zaiji da lamarin duk abinda ake ciki yace min Insha Allahu gobe muyi ƙoƙari muje gamu gashi gata ya zama na munje neman Auren ne”.
Numfashi Malam Ahmad yafesar kana yace.
“To ai wannan duk mai sauƙi ne badamuwa za'ayi hakan”.
Kai Abba ya gyaɗa kana tare da faɗin.
“Bakomai Insha Allah goben zamuje”.
Murmushi Lamiɗo yayi cike da kamala yace.
“Eh zamu bari gobe idan munyi sallar Azahar sai muje kafin nan ya tattauna da mahaifiyarsa idan anyi sa'a abin zai zo da sauƙi dake shi yana da kyakkyawar fahimta sannan bashi da son zuciya”.
Jinjina kai Malam Arɗo yayi idanunsa akan Lamiɗo yace.
“Ba matsala Insha Allah nima ina da ƙafa agarinsu dan Malamin dana ke zuwa ɗaukan karatu awajensa ai ƙanin Kakarta ce kuma sunzo wajena tare shima nasan yana da kawaici, kara da dattako”.
Jinjina kai sukayi tare da tsaida magana akan washe gari Bayan Sallar Azahar zasu tafi.
Washe gari baki ɗayansu suka shirya har Mommy da Khausar Lamiɗo yace su shirya atafi dasu Khausar da Mommy suna motar Lamiɗo Malam Arɗo da Malam Ahmad suna motar Abba kai tsaye suka dauki hanyar Jauro yaya suna isa Jauro yaua kai tsaye gidan Hajja Nana suka nufa dai-dai lokacin dasu Baffa Jimeta suka fito daga sallar La'asar Malam Liman na ganin Malam Arɗo ya faɗaɗa fara'ar fuskarsa kana yace.
“A'a Malam marhaban lale sannunku da zuwa”.
Baffa Jimeta kuwa cikin sauri ya nufi Lamiɗo tare da miƙa masa hannu yace.
“A'a Sannunku da zuwa har kuzo kenan?”.
Murmushi Lamiɗo yayi cikin yanayin dattako da kamalarsa yace.
“Eyyy sosai ma ai ba'a bori da sanyin jiki”.
Abba dake tsaye jikin mota yace.
“Aikam dai ba'a Bori da sanyin jiki”.
Baffa Garga da fitowarsa daga masallaci kenan yace.
“A masha Allah harda Alh Usman mai Dala ne a Lallai sannun ku da zuwa maraba maraba ku karaso?”.
Ya faɗa tare da shigewa gaba kasancewar yanzu shine ƙarami tun bayan rasuwar Baffa Umaru yana shiga ciki yace.
“Addah Hajja abamu taburmai munyi baƙi”.
Miƙewa tayi daga zaune da take da murmushi afuskarta ta ɗauko taburmai ta miƙa masa karɓa yayi kana ya shimfiɗa musu Abaranda.
Daga ciki tace.
“Aaa baƙi mukayi sannunku da zuwa sannunku”.
Tana ƙoƙarin fita Khausar da Mommy Kuma na kokarin shiga Atake fara'ar dake fuskarta ya gushe Harara ta watsawa Khausar sai kuma ta maida kallonta kan Mommy tace.
“A Aysha kune atafe?”.
Kai Mommy ta gyaɗa kana tace.
“Eh”.
Sannan suka shiga cikin dakin mazan kuma Baffa Garga ya shimfida musu taburmai daga waje.
Koma ciki Hajja Nana tayi tare da ɗaukan ƙwaryar nono da ƙorron soyayyan Zabbi da aka yiwa Baffa Jimeta na zuwansa ta kalli Khausar dake gefen Mommy zaune haɗe fuska tayi babu walwala atare da ita tace.
“Toh fitsararriya uwar fitsararru zoki kai musu abin taɓawa kin zauna kina zare ido sai kace wata ta Allah rasa kunya ɓerar tanka”.
Uffan khausar bata ce mata ba ta miƙe ta ɗauki Ƙorran ta fita ta kai musu sannan ta dawo wani ƙorron Hajja Nana ta miƙa wa Mommy kana tace.
“Aysha Bismillah”.
Kallon yanda tayi kicin-kicin da fuska Khausar tayi taɓe baki tayi cikin tsira mata ido tace.
“Hajja Nana Ni kar inci ne?”.
Harara ta watsa mata kana tace.
“Duk yanda kika ga dama kiyi”.
Ware ido Khausar tayi ta kalli Hajja Nana data kawar da kai gefe murmushi tayi cikin sanyin Murya tace.
“A'a Idan kada inci sai inbar miki kayanki”.
Baki Hajja Nana ta taɓe kana tace.
“Oho cikin ko nawa fitsararriya Mara kunya mai ido atsakar ka”.
Fuska Khausar ta ɓata ta buɗe baki da niyyar magana Mommy tayi saurin ɗaga mata hannu alamar kada tace komai hakan yasa ta tsuke bakinta Mommy kuwa kindirmon ta ɗaga ta burga kana tasa sugar.
Daga waje Lamiɗo yace.
“Khausar fito mana ki burga mana Nonon”.
Kai Baffa Garga ya Girgiza kana yace.
“Ba matsala bari na burga muku”.
Murmushi Lamiɗo yayi kana yace.
“A'a bari dai ita ɗin tazo ta burga mana”.
Miƙewa Khausar tayi tare da ɗaukan goran zuwa ta fita ta burga musu Nonon kana ta zuba musu zumar sannan ta miƙe ta koma ɗaki bayan sun gama taɓe taɓe an sake gaisawa Lamiɗo ya kalli Baffa Jimeta cikin sassauta murya yace.
“Toh Alh Muhammadu Hausawa sunce maso ɗan tsun-tsu shike binsa da jifa, mun zo wajenku neman yafiya, afuwa da kuma alfarma sannan da neman iri domin nima ina cikin ƴan neman Auren ne”.
Cikin sauri Baffa Jimeta yayi dariya kana ya girgiza kai tare da kallon Lamiɗo yace.
“Haba Lamiɗo ba zamuyi haka da kaiba ai kai mai bada Auren Khausar ne baka cikin masu neman aure kana cikin masu bada Auren Khausar ne”.
Murmushi Lamiɗo yayi cike da jin daɗin karancinsu yace.
“Nagode da karamci”.
Gyara zama Baffa Jimeta yayi da murmushi afuskarsa yace.
“Ka cancanci fiye da hakan Lamiɗo”.
Jinjina kai Baffa Liman yayi cike da kamala yace.
“Ai mu saidai muyi addu'a da fatan alkhairi amma kaine mai bada Khausar”.
Cikin jin dadi yace.
“Nagode da kawaici Allah yasaka da alkhairi”.
Gyara zama Malam Arɗo yayi da murmushi afuskarsa yace.
“Toh mu mun yarda mun amince mune masu neman Aure”.
Abba dake Kallonsu ya faɗaɗa Murmushin fuskarsa kana yace.
“Mune masu neman aure da kuma neman iri agareku bisa cika wasiyyar da ɗana ya bari ina fatan zan samu sauki da haɗin kanku wajen cikawa ɗana burinsa koda bayan ransa kamar yanda ya faɗa min”.
Ya ida maganar cikin rauni idanunsa na tara ƙwalla.
Ajiyar zuciya Baffa Jimeta ya sauke cike da tausayawa yace.
“Bakomai Alh Bashir Insha Allah babu abinda zai gagara aida mu daku duk mun zama ɗaya Lamiɗo yamin bayanin duk abinda ke tafiya kan cewa wasiyya ce daga wajen danƙa marigayi Jameelu”.
Ahankali Abba ya sunkuyar da kansa hawaye na cigaba da taruwa akwarmin Idanunsa.
Cikin sanyi Baffa Jimeta ya cigaba da cewa.
“Insha Allah bazai gagara ba zamuyi ƙoƙari amma yanzu kuyi haƙuri da al'amarin tsohuwa in Allah ya yarda babu abinda zai gagara”.
Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauke tare da gyara zamansa yace.
“Allah Ubangiji yasa haka mukam ma da gwaɓin mu muka zo duk da cewa akwai tsoro atare damu amma muna da kyakkyawan yaƙini akanku hakan yasa kafin muzo muka taho da gishiri da goro na neman izini”.
Murmushi Malam Liman yayi yana kallon Lamiɗo yace.
“Lallai kuwa zamu barku da Hajja Nana ku fafata”.
Zare da ido Lamiɗo yayi tare da sanya dariya kana cikin sauri yace.
“Na tuba ayimin afuwa ai Hajja Nana saiku zakuji da ita”.
Gyara zama Malam Liman yayi cike da nutsuwa yace.
“Insha Allah itama munyi ƙoƙari mun samu ta ɗan sauko amma duk da haka akwai karin ɗan lokaci da za'a bayar”.
Anutse Lamiɗo ya gyara zama cike da dattako yace.
“Badamuwa Insha Allahu dama nima ina shirin zan ne meku ɗin saboda bani da ikon bada ita akaran kaina amma munyi magana da Baffan yarinya yau ɗin nan ma yazo daga can Adamawa zai nemi sahalewar kakar yarinya”.
Ajiyar zuciya suka sauƙe atare Kallonsu Lamiɗo yayi kana ya cigaba da cewa.
“Dake Itace taso kawo tangarɗa acikin al'amarin amma yace zaiji da lamarin duk abinda ake ciki yace min Insha Allahu gobe muyi ƙoƙari muje gamu gashi gata ya zama na munje neman Auren ne”.
Numfashi Malam Ahmad yafesar kana yace.
“To ai wannan duk mai sauƙi ne badamuwa za'ayi hakan”.
Kai Abba ya gyaɗa kana tare da faɗin.
“Bakomai Insha Allah goben zamuje”.
Murmushi Lamiɗo yayi cike da kamala yace.
“Eh zamu bari gobe idan munyi sallar Azahar sai muje kafin nan ya tattauna da mahaifiyarsa idan anyi sa'a abin zai zo da sauƙi dake shi yana da kyakkyawar fahimta sannan bashi da son zuciya”.
Jinjina kai Malam Arɗo yayi idanunsa akan Lamiɗo yace.
“Ba matsala Insha Allah nima ina da ƙafa agarinsu dan Malamin dana ke zuwa ɗaukan karatu awajensa ai ƙanin Kakarta ce kuma sunzo wajena tare shima nasan yana da kawaici, kara da dattako”.
Jinjina kai sukayi tare da tsaida magana akan washe gari Bayan Sallar Azahar zasu tafi.
Washe gari baki ɗayansu suka shirya har Mommy da Khausar Lamiɗo yace su shirya atafi dasu Khausar da Mommy suna motar Lamiɗo Malam Arɗo da Malam Ahmad suna motar Abba kai tsaye suka dauki hanyar Jauro yaya suna isa Jauro yaua kai tsaye gidan Hajja Nana suka nufa dai-dai lokacin dasu Baffa Jimeta suka fito daga sallar La'asar Malam Liman na ganin Malam Arɗo ya faɗaɗa fara'ar fuskarsa kana yace.
“A'a Malam marhaban lale sannunku da zuwa”.
Baffa Jimeta kuwa cikin sauri ya nufi Lamiɗo tare da miƙa masa hannu yace.
“A'a Sannunku da zuwa har kuzo kenan?”.
Murmushi Lamiɗo yayi cikin yanayin dattako da kamalarsa yace.
“Eyyy sosai ma ai ba'a bori da sanyin jiki”.
Abba dake tsaye jikin mota yace.
“Aikam dai ba'a Bori da sanyin jiki”.
Baffa Garga da fitowarsa daga masallaci kenan yace.
“A masha Allah harda Alh Usman mai Dala ne a Lallai sannun ku da zuwa maraba maraba ku karaso?”.
Ya faɗa tare da shigewa gaba kasancewar yanzu shine ƙarami tun bayan rasuwar Baffa Umaru yana shiga ciki yace.
“Addah Hajja abamu taburmai munyi baƙi”.
Miƙewa tayi daga zaune da take da murmushi afuskarta ta ɗauko taburmai ta miƙa masa karɓa yayi kana ya shimfiɗa musu Abaranda.
Daga ciki tace.
“Aaa baƙi mukayi sannunku da zuwa sannunku”.
Tana ƙoƙarin fita Khausar da Mommy Kuma na kokarin shiga Atake fara'ar dake fuskarta ya gushe Harara ta watsawa Khausar sai kuma ta maida kallonta kan Mommy tace.
“A Aysha kune atafe?”.
Kai Mommy ta gyaɗa kana tace.
“Eh”.
Sannan suka shiga cikin dakin mazan kuma Baffa Garga ya shimfida musu taburmai daga waje.
Koma ciki Hajja Nana tayi tare da ɗaukan ƙwaryar nono da ƙorron soyayyan Zabbi da aka yiwa Baffa Jimeta na zuwansa ta kalli Khausar dake gefen Mommy zaune haɗe fuska tayi babu walwala atare da ita tace.
“Toh fitsararriya uwar fitsararru zoki kai musu abin taɓawa kin zauna kina zare ido sai kace wata ta Allah rasa kunya ɓerar tanka”.
Uffan khausar bata ce mata ba ta miƙe ta ɗauki Ƙorran ta fita ta kai musu sannan ta dawo wani ƙorron Hajja Nana ta miƙa wa Mommy kana tace.
“Aysha Bismillah”.
Kallon yanda tayi kicin-kicin da fuska Khausar tayi taɓe baki tayi cikin tsira mata ido tace.
“Hajja Nana Ni kar inci ne?”.
Harara ta watsa mata kana tace.
“Duk yanda kika ga dama kiyi”.
Ware ido Khausar tayi ta kalli Hajja Nana data kawar da kai gefe murmushi tayi cikin sanyin Murya tace.
“A'a Idan kada inci sai inbar miki kayanki”.
Baki Hajja Nana ta taɓe kana tace.
“Oho cikin ko nawa fitsararriya Mara kunya mai ido atsakar ka”.
Fuska Khausar ta ɓata ta buɗe baki da niyyar magana Mommy tayi saurin ɗaga mata hannu alamar kada tace komai hakan yasa ta tsuke bakinta Mommy kuwa kindirmon ta ɗaga ta burga kana tasa sugar.
Daga waje Lamiɗo yace.
“Khausar fito mana ki burga mana Nonon”.
Kai Baffa Garga ya Girgiza kana yace.
“Ba matsala bari na burga muku”.
Murmushi Lamiɗo yayi kana yace.
“A'a bari dai ita ɗin tazo ta burga mana”.
Miƙewa Khausar tayi tare da ɗaukan goran zuwa ta fita ta burga musu Nonon kana ta zuba musu zumar sannan ta miƙe ta koma ɗaki bayan sun gama taɓe taɓe an sake gaisawa Lamiɗo ya kalli Baffa Jimeta cikin sassauta murya yace.
“Toh Alh Muhammadu Hausawa sunce maso ɗan tsun-tsu shike binsa da jifa, mun zo wajenku neman yafiya, afuwa da kuma alfarma sannan da neman iri domin nima ina cikin ƴan neman Auren ne”.
Cikin sauri Baffa Jimeta yayi dariya kana ya girgiza kai tare da kallon Lamiɗo yace.
“Haba Lamiɗo ba zamuyi haka da kaiba ai kai mai bada Auren Khausar ne baka cikin masu neman aure kana cikin masu bada Auren Khausar ne”.
Murmushi Lamiɗo yayi cike da jin daɗin karancinsu yace.
“Nagode da karamci”.
Gyara zama Baffa Jimeta yayi da murmushi afuskarsa yace.
“Ka cancanci fiye da hakan Lamiɗo”.
Jinjina kai Baffa Liman yayi cike da kamala yace.
“Ai mu saidai muyi addu'a da fatan alkhairi amma kaine mai bada Khausar”.
Cikin jin dadi yace.
“Nagode da kawaici Allah yasaka da alkhairi”.
Gyara zama Malam Arɗo yayi da murmushi afuskarsa yace.
“Toh mu mun yarda mun amince mune masu neman Aure”.
Abba dake Kallonsu ya faɗaɗa Murmushin fuskarsa kana yace.
“Mune masu neman aure da kuma neman iri agareku bisa cika wasiyyar da ɗana ya bari ina fatan zan samu sauki da haɗin kanku wajen cikawa ɗana burinsa koda bayan ransa kamar yanda ya faɗa min”.
Ya ida maganar cikin rauni idanunsa na tara ƙwalla.
Ajiyar zuciya Baffa Jimeta ya sauke cike da tausayawa yace.
“Bakomai Alh Bashir Insha Allah babu abinda zai gagara aida mu daku duk mun zama ɗaya Lamiɗo yamin bayanin duk abinda ke tafiya kan cewa wasiyya ce daga wajen danƙa marigayi Jameelu”.
Ahankali Abba ya sunkuyar da kansa hawaye na cigaba da taruwa akwarmin Idanunsa.
Cikin sanyi Baffa Jimeta ya cigaba da cewa.
“Insha Allah bazai gagara ba zamuyi ƙoƙari amma yanzu kuyi haƙuri da al'amarin tsohuwa in Allah ya yarda babu abinda zai gagara”.
Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauke tare da gyara zamansa yace.
“Allah Ubangiji yasa haka mukam ma da gwaɓin mu muka zo duk da cewa akwai tsoro atare damu amma muna da kyakkyawan yaƙini akanku hakan yasa kafin muzo muka taho da gishiri da goro na neman izini”.
Murmushi Malam Liman yayi yana kallon Lamiɗo yace.
“Lallai kuwa zamu barku da Hajja Nana ku fafata”.
Zare da ido Lamiɗo yayi tare da sanya dariya kana cikin sauri yace.
“Na tuba ayimin afuwa ai Hajja Nana saiku zakuji da ita”.
Gyara zama Malam Liman yayi cike da nutsuwa yace.
“Insha Allah itama munyi ƙoƙari mun samu ta ɗan sauko amma duk da haka akwai karin ɗan lokaci da za'a bayar”.