Sashe 21
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Cikin yanayin ɓacin rai Mommy ta ture kanta dake kan cinyar ta babu walwala atare da ita tace.
“To ai shikenan Khausar hankalinki ya kwanta, zagine da abin kunya kunja min, kukan me kuma zaki zo kina min, in banda rashin hankali dama rashin kunya Khausar yaushe Moddibo yace yana sonki yaushe Moddibo ya taɓa zuwa wajenki?”.
Kasa cewa komai Khausar tayi sai hawaye dake cigaba da kwaranya a Idanunta Shar-shar.
Cike da takaici Mommy ta cigaba da cewa.
“Mutumin da ko Amakaranta tsakaninki dashi sai dai faɗa kyara da hantara. Duk abinda ke faruwa ina sane ai ana bani labari amma saboda tsabar shashanci ki rasa wanda zaki ce kina so sai mutumin da bakwa zama inuwa ɗaya!”.
Kuka sosai Khausar ta fashe dashi cikin sheshsheƙan Kukan tace.
“Wallahi Mommy ba haka bane dan Allah ki tsaya ki saurareni”.
Kai Mommy ta Girgiza tare da tsira mata Ido tace.
“Hmmm Khausar kenan me zan saurara kuma, ai babu abinda zanji daga gareki tunda ke kika haifi kanki ke zaki yankewa kanki hukunci sannan ke zaki zaɓawa kanki miji wai ki kalli tsabar Idanunmu saboda tsaurin Ido kice Modibbo kike so to yaushe yace yana sonki?”.
Girgiza kai kawai tayi cikin matsanancin kuka da tashin hankali tace.
“Dan Allah Mommy kiyi haƙuri wallahi ba rashin kunya bane dolene yasa haka Mommy ki sanya mana al'barka acikin rayuwar auren da zamu yi”.
Cike da takaici Mommy ta kalleta kana tace.
“Toh Khausar tambayar da zan miki Moddibo yace yana sonki ko kuma ke kike haukanki?”.
Girgiza kai Khausar tayi cikin rawan murya tace.
“Mommy I don't know either he love me or not”.
Miƙewa Mommy tayi tare da jan dogon tsaki ta fice daga ɗakin ta nufi Falon Lamiɗo.
Khausar kuwa kanta ta kife ajikin katifa ta fashe da sassayan kuka tana sheshsheƙa Ajiyar zuciya Haiydar ya sauƙe tare da kallon Khausar cikin sanyin murya da rashin fahimta yace.
“Addah Khausi ban fahimci abinda Mommy take faɗa ba wai Malam Moddibo kike so ko kuma wa?”.
Kai ta gyaɗa masa Muryanta na rawa tace.
“Eh shi nake so”.
Zare ido Haiydar yayi tare da sanya salati kana yace.
“Toh shi Malam Moddibo yana sonki ne?,”.
Kai Khausar ta girgiza tare da ɗago Idanunta dake jiƙe da hawaye cikin raunin murya tace.
“Ban saniba Haiydar I really don't know”.
Cike da matsanancin mamaki da damuwa Haiydar yace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Khausar baki sani ba kuma?”.
Jinjina kai Khausar tayi cikin raunin murya tace.
“Bansani ba Haiydar Bansani ba Haiydar”.
Miƙewa Haiydar yayi cike da takaici yaja dogon tsaki tare da faɗin.
“Wallahi dama nasan hakane babu abinda zaisa in rakoki wajen Mommy”.
Ya ida maganar tare da ficewa cike da takaici da ban haushi.
Cikin rauni Khausar ta miƙe tare da nufar Bedroom ɗinta tana shiga ta faɗa bisa gado tare da sakin kuka mai masifar ɗaci da ƙuna.
Mommy kuwa kai tsaye falon Lamiɗo ta nufa bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon zaune ta samu Abba akan 2sitter.
Anutse Lamiɗo ya ɗago kansa tare da sakar mata da lallausan murmushi kana yace.
“Shatu Ikon Allah mai kuma ya ɓatawa Gimbiya Aysha rai”.
Fuska Mommy ta ɓata tare da narkar da murya kana tace.
“Na lura ma al'amarin Khausar dariya yake baka, baki ɗaya tun jiya Yarinyar nan ta ɓata min rai ta hargitsa min lissafi, sam kakarta bata da kirki tsohuwa ce mai zafi ta saba da iko da gadara akan ƙannenta ta saba da maganar ta kamar yankan wuƙace”.
Kallonta kawai Lamiɗo yake yana murmushi.
Cikin yanayin damuwa ta cigaba da cewa.
“Duk abinda ta faɗa haka ne babu wanda ya isa ya musan ta mata gashi Khausar tazo tayi mata abinda bashi neba ta tafi tana zagina yanzu tana zuwa Rugar nan zata baza sunan Khausar hakan zanji daɗi ne?”.
Murmushi Lamiɗo yayi tare da gyara zaman sa kana ya miƙa mata hannunsa tare da cewa taho nan zo nan Shatuna”.
Maƙe kafaɗa tayi tare da tura baki kana ta narkar da fuska.
Murmushi Lamiɗo yayi tare da cewa.
“Ki zauna mana”.
Kallonsa kawai take amma ba tace Uffan ba.
Ahankali ya sanya hannunsa ya janyo tsintsiyar hannunta tare da zaunar da ita agefen sa cikin sanyin murya yace.
“To amma ai akwai abinda baki sani ba”.
Asanyaye ta kallesa tare da cewa.
“Toh menene ban sani ba?”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da tsira mata ido kana yace.
“Jiya Hajja Nana bata bani dama inyi mata Magana ba saboda yanda ta ɗauki abin da zafi take ta ihu da kururuwa da Masifa sannan dole mu bita ayanda taso”.
Jinjina Kai Mommy tayi tare da sauƙe numfashi.
Cikin sanyin Murya ya cigaba da cewa.
“Tun da kinga tsohuwa ce sannan tana da ƙarfin iko akan Khausar babu yanda muka iya, amma Baffanta ya fahimta domin yau kafin ya koma Ɓadamaya yabiyo nan munyi magana dashi”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana ya kalli Mommy da itama shi take kallo yace.
“Sannan yace ba zai mata dole ba kamar yanda idan Mahaifinta yana raye ba zai mata dole ba kamar yanda zai yiwa ƴaƴan sa haka zai mata saboda yana da ƴaƴa mata da yawa kamar yanda bai musu dole ba haka itama ba zai mata dole ba dan mahaifinta baya raye”.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da fesar da numfashi kana tace.
“Na sani shi yana da fahimta, amma ita tsohuwar ce gaba ɗaya ba zata fahimta ba”.
Lakace mata hanci Lamiɗo yayi kana da murmushi afuskarsa yace.
“Kada ki damu ɗan zai fahimtar da ita, dan yace ya bata haƙuri sannan idan ta huce zai sake dawowa ya bata haƙuri kuma Insha Allah zata fahimta”.
Jinjina kai Mommy tayi tare da gyara zamanta kana tace.
“Toh naji ta wannan gefen an samu fahimta amma fa Moddibo baya Son Khausar din ita da bakinta fa tace min bata san yana sonta ko baya sonta ba, ka taɓa ganin Moddibo yazo wajen Khausar ne?”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa.
“Eh na taɓa gani mana kwanaki sunzo da Asma'u”.
Girgiza kai Mommy tayi tare da fesar da numfashi kana tace.
“Zuwan da kaga yayi ta'aziyyan Ramadan yazo min domin yace alokacin da suka zo yimin ta'aziyya sun haɗu da Ori da ya muku bayani gawar Jameel toh sun fita bai shigo ya min ta'aziyya ba, shine suka zo da Asma'u yamin amma fa baice yana son Khausar ba hasalima Khausar da Moddibo basa zama inuwa ɗaya”.
Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauƙe tare da gyara zamansa ya fuskanceta tare da cewa.
“Ki nutsu mana Ni nafi so ki nutsu Ayshatu idan kin nutsu sai in miki bayani”.
Marairaice fuska tayi tare da langwaɓar da kai kana tace.
“Toh ai yanzu ma Anutse nake ranka shi daɗe kai nake sauraro”.
Murmushi yayi tare da riƙe tafin hannunta acikin nasa kana ya lumshe idanunsa tare da cewa.
“Jiya ma hargowar Hajja Nana ce ya hana in miki bayani shekaran jiya baki ji cewa nayi baƙi ba?”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Eh naji”.
Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauke kana ahankali yace.
“Toh Malam, Arɗo ne da Alh Bashir mai Dala Mahaifin marigayi Malam Jameel da kuma Malam Ahmad Baban Asma'u suka zo”.
Jinjina kai Mommy tayi kana cikin sanyin murya tace.
“Ooh sune suka zo!?”..
Kai ya gyaɗa mata still hannunsa na cikin nata yace.
“Eh”.
fesar da numfashi yayi kama yace.
“Toh kinsan me yaka wo su?”.
Kai ta Girgiza kana tace.
“A'a sai ka faɗa”.
Atake yanayin fuskarsa ya sauya daga murmushi zuwa rauni cikin sanyin murya da rauni yace.
“Magana suka zo akan wasiyyar da Marigayi Jameelu ya bari”.
Saurin Kallonsa Mommy tayi cikin sanyin murya da damuwa tace.
“Wasiyya kuma!?”.
Jinjina mata kai Lamiɗo yayi tare da fesar da numfashi kana yace.
“Eh”.
Ahankali tace.
“Wasiyya kuma Jameel ya bari akan me!?”.
Zamansa ya gyara tare da janye hannunsa ɗaya daga cikin na Mommy ya dafe goshinsa cikin raunin murya yace.
“Jameel yabar wasiyya ne akan Moddibo da Khausar”.
Lokaci ɗaya idanun Mommy suka ciko da Hawaye cikin raunin murya tace.
“Wasiyya akan Moddibo da Khausar kuma to akan me?”.
Jinjina mata kai yayi still muryarsa Araunane yace.
“Tabbas Mahaifinsa ya faɗa min cewa akwai ranan da suka je shi da Moddibo gidansa alokacin saura kwana uku asace sa har yake faɗa masa yafa zaɓawa Moddibo matar da zai Aura Amma shi kansa Moddibo bai sani ba domin koda Jameel ya faɗa murmushi Moddibo yayi alokacin har yake cewa Alhaji Bashiru. Abba kaji fa wai ni J zai za ɓawa mata kamar wani yaro ko makaho”.
Lumshe ido Lamiɗo yayi cikin rauni ya cigaba da cewa.
“Alokacin Abban sa yace ya faɗa masa wace mata ce sai Jameelu yayi dariya yace sai ya dawo asirri zai faɗa masa to bayan da ya dawo sai yace wa mahaifinsa dan Allah Abba ina neman alfarma acikin kwanakin nan domin wata ƙila akwai abinda zai iya faruwa acikin kwanakin nan wataƙil agaban ido na wataƙil kuma abayan Idona”.
“To ai shikenan Khausar hankalinki ya kwanta, zagine da abin kunya kunja min, kukan me kuma zaki zo kina min, in banda rashin hankali dama rashin kunya Khausar yaushe Moddibo yace yana sonki yaushe Moddibo ya taɓa zuwa wajenki?”.
Kasa cewa komai Khausar tayi sai hawaye dake cigaba da kwaranya a Idanunta Shar-shar.
Cike da takaici Mommy ta cigaba da cewa.
“Mutumin da ko Amakaranta tsakaninki dashi sai dai faɗa kyara da hantara. Duk abinda ke faruwa ina sane ai ana bani labari amma saboda tsabar shashanci ki rasa wanda zaki ce kina so sai mutumin da bakwa zama inuwa ɗaya!”.
Kuka sosai Khausar ta fashe dashi cikin sheshsheƙan Kukan tace.
“Wallahi Mommy ba haka bane dan Allah ki tsaya ki saurareni”.
Kai Mommy ta Girgiza tare da tsira mata Ido tace.
“Hmmm Khausar kenan me zan saurara kuma, ai babu abinda zanji daga gareki tunda ke kika haifi kanki ke zaki yankewa kanki hukunci sannan ke zaki zaɓawa kanki miji wai ki kalli tsabar Idanunmu saboda tsaurin Ido kice Modibbo kike so to yaushe yace yana sonki?”.
Girgiza kai kawai tayi cikin matsanancin kuka da tashin hankali tace.
“Dan Allah Mommy kiyi haƙuri wallahi ba rashin kunya bane dolene yasa haka Mommy ki sanya mana al'barka acikin rayuwar auren da zamu yi”.
Cike da takaici Mommy ta kalleta kana tace.
“Toh Khausar tambayar da zan miki Moddibo yace yana sonki ko kuma ke kike haukanki?”.
Girgiza kai Khausar tayi cikin rawan murya tace.
“Mommy I don't know either he love me or not”.
Miƙewa Mommy tayi tare da jan dogon tsaki ta fice daga ɗakin ta nufi Falon Lamiɗo.
Khausar kuwa kanta ta kife ajikin katifa ta fashe da sassayan kuka tana sheshsheƙa Ajiyar zuciya Haiydar ya sauƙe tare da kallon Khausar cikin sanyin murya da rashin fahimta yace.
“Addah Khausi ban fahimci abinda Mommy take faɗa ba wai Malam Moddibo kike so ko kuma wa?”.
Kai ta gyaɗa masa Muryanta na rawa tace.
“Eh shi nake so”.
Zare ido Haiydar yayi tare da sanya salati kana yace.
“Toh shi Malam Moddibo yana sonki ne?,”.
Kai Khausar ta girgiza tare da ɗago Idanunta dake jiƙe da hawaye cikin raunin murya tace.
“Ban saniba Haiydar I really don't know”.
Cike da matsanancin mamaki da damuwa Haiydar yace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Khausar baki sani ba kuma?”.
Jinjina kai Khausar tayi cikin raunin murya tace.
“Bansani ba Haiydar Bansani ba Haiydar”.
Miƙewa Haiydar yayi cike da takaici yaja dogon tsaki tare da faɗin.
“Wallahi dama nasan hakane babu abinda zaisa in rakoki wajen Mommy”.
Ya ida maganar tare da ficewa cike da takaici da ban haushi.
Cikin rauni Khausar ta miƙe tare da nufar Bedroom ɗinta tana shiga ta faɗa bisa gado tare da sakin kuka mai masifar ɗaci da ƙuna.
Mommy kuwa kai tsaye falon Lamiɗo ta nufa bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon zaune ta samu Abba akan 2sitter.
Anutse Lamiɗo ya ɗago kansa tare da sakar mata da lallausan murmushi kana yace.
“Shatu Ikon Allah mai kuma ya ɓatawa Gimbiya Aysha rai”.
Fuska Mommy ta ɓata tare da narkar da murya kana tace.
“Na lura ma al'amarin Khausar dariya yake baka, baki ɗaya tun jiya Yarinyar nan ta ɓata min rai ta hargitsa min lissafi, sam kakarta bata da kirki tsohuwa ce mai zafi ta saba da iko da gadara akan ƙannenta ta saba da maganar ta kamar yankan wuƙace”.
Kallonta kawai Lamiɗo yake yana murmushi.
Cikin yanayin damuwa ta cigaba da cewa.
“Duk abinda ta faɗa haka ne babu wanda ya isa ya musan ta mata gashi Khausar tazo tayi mata abinda bashi neba ta tafi tana zagina yanzu tana zuwa Rugar nan zata baza sunan Khausar hakan zanji daɗi ne?”.
Murmushi Lamiɗo yayi tare da gyara zaman sa kana ya miƙa mata hannunsa tare da cewa taho nan zo nan Shatuna”.
Maƙe kafaɗa tayi tare da tura baki kana ta narkar da fuska.
Murmushi Lamiɗo yayi tare da cewa.
“Ki zauna mana”.
Kallonsa kawai take amma ba tace Uffan ba.
Ahankali ya sanya hannunsa ya janyo tsintsiyar hannunta tare da zaunar da ita agefen sa cikin sanyin murya yace.
“To amma ai akwai abinda baki sani ba”.
Asanyaye ta kallesa tare da cewa.
“Toh menene ban sani ba?”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da tsira mata ido kana yace.
“Jiya Hajja Nana bata bani dama inyi mata Magana ba saboda yanda ta ɗauki abin da zafi take ta ihu da kururuwa da Masifa sannan dole mu bita ayanda taso”.
Jinjina Kai Mommy tayi tare da sauƙe numfashi.
Cikin sanyin Murya ya cigaba da cewa.
“Tun da kinga tsohuwa ce sannan tana da ƙarfin iko akan Khausar babu yanda muka iya, amma Baffanta ya fahimta domin yau kafin ya koma Ɓadamaya yabiyo nan munyi magana dashi”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana ya kalli Mommy da itama shi take kallo yace.
“Sannan yace ba zai mata dole ba kamar yanda idan Mahaifinta yana raye ba zai mata dole ba kamar yanda zai yiwa ƴaƴan sa haka zai mata saboda yana da ƴaƴa mata da yawa kamar yanda bai musu dole ba haka itama ba zai mata dole ba dan mahaifinta baya raye”.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da fesar da numfashi kana tace.
“Na sani shi yana da fahimta, amma ita tsohuwar ce gaba ɗaya ba zata fahimta ba”.
Lakace mata hanci Lamiɗo yayi kana da murmushi afuskarsa yace.
“Kada ki damu ɗan zai fahimtar da ita, dan yace ya bata haƙuri sannan idan ta huce zai sake dawowa ya bata haƙuri kuma Insha Allah zata fahimta”.
Jinjina kai Mommy tayi tare da gyara zamanta kana tace.
“Toh naji ta wannan gefen an samu fahimta amma fa Moddibo baya Son Khausar din ita da bakinta fa tace min bata san yana sonta ko baya sonta ba, ka taɓa ganin Moddibo yazo wajen Khausar ne?”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa.
“Eh na taɓa gani mana kwanaki sunzo da Asma'u”.
Girgiza kai Mommy tayi tare da fesar da numfashi kana tace.
“Zuwan da kaga yayi ta'aziyyan Ramadan yazo min domin yace alokacin da suka zo yimin ta'aziyya sun haɗu da Ori da ya muku bayani gawar Jameel toh sun fita bai shigo ya min ta'aziyya ba, shine suka zo da Asma'u yamin amma fa baice yana son Khausar ba hasalima Khausar da Moddibo basa zama inuwa ɗaya”.
Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauƙe tare da gyara zamansa ya fuskanceta tare da cewa.
“Ki nutsu mana Ni nafi so ki nutsu Ayshatu idan kin nutsu sai in miki bayani”.
Marairaice fuska tayi tare da langwaɓar da kai kana tace.
“Toh ai yanzu ma Anutse nake ranka shi daɗe kai nake sauraro”.
Murmushi yayi tare da riƙe tafin hannunta acikin nasa kana ya lumshe idanunsa tare da cewa.
“Jiya ma hargowar Hajja Nana ce ya hana in miki bayani shekaran jiya baki ji cewa nayi baƙi ba?”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Eh naji”.
Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauke kana ahankali yace.
“Toh Malam, Arɗo ne da Alh Bashir mai Dala Mahaifin marigayi Malam Jameel da kuma Malam Ahmad Baban Asma'u suka zo”.
Jinjina kai Mommy tayi kana cikin sanyin murya tace.
“Ooh sune suka zo!?”..
Kai ya gyaɗa mata still hannunsa na cikin nata yace.
“Eh”.
fesar da numfashi yayi kama yace.
“Toh kinsan me yaka wo su?”.
Kai ta Girgiza kana tace.
“A'a sai ka faɗa”.
Atake yanayin fuskarsa ya sauya daga murmushi zuwa rauni cikin sanyin murya da rauni yace.
“Magana suka zo akan wasiyyar da Marigayi Jameelu ya bari”.
Saurin Kallonsa Mommy tayi cikin sanyin murya da damuwa tace.
“Wasiyya kuma!?”.
Jinjina mata kai Lamiɗo yayi tare da fesar da numfashi kana yace.
“Eh”.
Ahankali tace.
“Wasiyya kuma Jameel ya bari akan me!?”.
Zamansa ya gyara tare da janye hannunsa ɗaya daga cikin na Mommy ya dafe goshinsa cikin raunin murya yace.
“Jameel yabar wasiyya ne akan Moddibo da Khausar”.
Lokaci ɗaya idanun Mommy suka ciko da Hawaye cikin raunin murya tace.
“Wasiyya akan Moddibo da Khausar kuma to akan me?”.
Jinjina mata kai yayi still muryarsa Araunane yace.
“Tabbas Mahaifinsa ya faɗa min cewa akwai ranan da suka je shi da Moddibo gidansa alokacin saura kwana uku asace sa har yake faɗa masa yafa zaɓawa Moddibo matar da zai Aura Amma shi kansa Moddibo bai sani ba domin koda Jameel ya faɗa murmushi Moddibo yayi alokacin har yake cewa Alhaji Bashiru. Abba kaji fa wai ni J zai za ɓawa mata kamar wani yaro ko makaho”.
Lumshe ido Lamiɗo yayi cikin rauni ya cigaba da cewa.
“Alokacin Abban sa yace ya faɗa masa wace mata ce sai Jameelu yayi dariya yace sai ya dawo asirri zai faɗa masa to bayan da ya dawo sai yace wa mahaifinsa dan Allah Abba ina neman alfarma acikin kwanakin nan domin wata ƙila akwai abinda zai iya faruwa acikin kwanakin nan wataƙil agaban ido na wataƙil kuma abayan Idona”.