Sashe 5
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gyara zama Hajja Nana tayi cikin ƙanƙance Ido tace.
“Ke ko kunya bakya ji dube ki fa duk kin gama girma agida shekarunki kusan Ashirin ai wannan ma taumaka miki za'ayi dan kin gama tsufa”.
Buɗe baki Khausar tayi tare da kallon kanta kana ta kalli Hajja Nana cike da Isa Hajja Nana tace.
“Kalleni da kyau yo ƙarya na miki, ƙannen bayanki nawa aka Aurar wasu da yara bibbiyu wasu kuma ɗaddaya ke kam wannan wani sai dai yace bazawara ce ke dan kin gama girma”.
Wani kallo Khausar ta mata tare da cewa.
“A'a Hajja Nana ya isa haka cin fuska dan wlh bazan juraba.Wanda suka fini dubu nawa ne basuyi Aure ba, sai dai idan A Rugar kune ake irin wannan Auren, amma nikam yanzu ma nayi ƙarama da Aure.
Mommy kuwa kallon Khausar tayi tare da ɗaga mata hannu kana tace.
“Haka naki Khausar kiyi mana shiru”.
Sunkuyar da kanta ƙasa tayi batare da ta sake cewa Uffan ba kawai dai tasan in ba ita ke tare Hajja Nana ba Mommy kam ba abinda zatace tanaji tana gani za'a tauyeta.
Hajja Nana Khausar ta nunata da ɗan yatsa tace.
“Ki kiyayeni bada ke nake magana ba fitsararriya mara kunya!”.
Gyara zama Khausar tayi tare da juya mata manyan Idanunta da kawar da kai gefe.
Murmushi Dije dake gefen Khausar tayi tare da riƙe hannun ta da ido tayi mata alamar ta daina.
Gyaran murya Hajja Nana tayi tare da cewa.
“Aysha Ni dake nake magana bada Khausar ba, ya batun maganar da mukayi tunda Allah yasa tagama yanzu, sannan makon daya gabata Baffanta yazo daga Adamawa aranan daya zo aranan ya koma”.
Sai kuma ta kalli Khausar tare da watsa mata Harara kana ta maida kallonta kan Mommy dake sauraronta tace.
“Toh dama ace yazo da niyyar kwana zamu ƙara so nan, ayi magana to amma ke me kikace tsakaninta da Aliyu ɗan Uwanta!?”.
Ahankali Mommy ta sunkuyar da kanta ƙasa kana tayi shiru cikin yanayin sanyinta da Kawaici, da mutumtaka da kuma kamala tace.
“Toh Hajja Nana wannan magana duk yanda kuka zantar ai hakane Baffanta shine me Aurar da ita, dan haka duk abinda ya yanke akanta shine dai-dai”.
Jinjina kai Hajja Nana tayi tare da tura kallabin kanta kana ta gyara zamanta cikin jin daɗi tace.
“Shima yace min Insha Allah nan da wata ɗaya ko sati uku zai zo idan ya samu sarari zaizo su zanta da Uban goyon yarinyar, shima abashi mutuncinsa tunda shi ya raineta tun tana da wata wata uku shi yamata komai”.
Kai Mommy ta gyaɗa tare da faɗin.
“Bakomai duk abinda kuka tsara yayi Idan har Auren Khausar da ɗan Uwanta Al'khairi ne Allah ya tabbatar mana da alkhairinsa”.
Cikin sauri Khausar ta tura bakinta tare da cewa.
“Ni dai bana sonshi kuma ke dai Mommy ayita Addu'ar alkhairi”.
Wani kallo Mommy ta watsa mata alamar rufe min baki, shiru Khausar tayi tare da sunkuyar da kanta ƙasa Mommy kuwa kallon Hajja Nana tayi cikin sanyin murya tace.
“Ni dai Allah ya tabbatar da al'khairi idan al'khairi ne Allah ya tabbatar ya kuma zaɓa musu abinda yafi zama al'khairi atsakanin su.
Gyara zama Hajja Nana tayi kana tace.
“Ammen,Kuma Insha Allahu ma alkhairi ne”.
Kai Mommy ta gyaɗa tare da cewa.
“Adduar da mukeyi kenan”.
Miƙewa Khausar tayi tare da riƙe hannun Dije da alamun ɓacin rai tace.
“Dije mu tafi”.
Harara Hajja Nana ta watsa mata tare da sake tura daurin Kallabinta gaba kana tace.
“Aikuwa wannan magana ya zama dole ki saurareta tunda batu ne na Aurenki akeyi”.
Cikin ƙankance Ido Khausar tace.
“Nifa bazanyi Aureba ehe ke baki da aiki sai ƙaƙale ƙaƙalen magana ina ruwanki da batun Aurena!?”.
Afusace ta kalleta kana tayi Ƙwaffa tare da cewa.
“Aikuwa dan Ubanki nike da ruwa dake kuma dole kiyu Aure”.
cikin tsirawa Hajja Nana ido tace.
“Amma dai na faɗa miki ki daina zagin mahaifina Aure kuwa idan Allah ya nufa zanyi amma ba wanda kike cewa ba kam!?”.
Ajiyar zuciya Hajja Nana ta sauke kana tana kallonta bako ƙyaftawa sai kuma ta sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.
“To wa kike so ki Aura?”.
Juya ido Khausar tayi tare da cewa.
“Aini nasan wanda zan Aura, kuma dan haka babu ruwanki dani sai kace ke lokacin da zaki yi Aure zaɓa miki wanda zaki Aura akayi ba ke kika zaɓa da kanki ba!”.
Girgiza kai Mommy tayi tare da nunawa Khausar hanya da hannu alamar tabar wajen ita har ga Allah bata so ma Hajja Nana ta tsaida Khausar a cikin mgnar ba in bana tsohuwaba taya zata tsaida Khausar bayan tasan yadda suke da juna.
Tura baki Khausar tayi tare da jan hannun Dije dake murmushi sam bata gajiya da kallon Dramer Khausar da Hajja Nana.
Khausar da Dije na isa ƙofar Bedroom ɗin zasu shiga Akuma dai-dai lokacin Asma'u tayi sallama cike da ladabi tsugunna agaban Mommy ta gaisheta Cike da kulawa Mommy ta amsa tare da tambayarta ya Umminta ta amsa da tana lafiya.
Kana ahankali ta maida kallonta kan Hajja Nana dake cin Inabi tace.
“Hajja Nana inayini fatan kunzo lafiya?”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da cewa.
“Lafiya lau Alhamdulillah Allah ya miki albarka kar dai ki riƙa ɗaukar hallayar wasu ƙawaye na tsiwa”.
Ɗan murmushi Asma'u tayi kana cikin sanyi ta gyaɗa kanta Khausar dake tsaye bakin ƙofa ta wani ɓata fuska tare da kawar da kai gefe.
Miƙewa Asma'u tayi ta nufi wajensu Khausar suka shiga Bedroom cikin ɗan sakin fuska da sanyi Asma'u tace.
“A Dije sannu da zuwa ya gida ya mutanen Jauro yaya!?”.
Murmushi Dije tayi cikin yanayin sanyin ta tace.
“Duk lafiya lau?”.
Kallon Dije Khausar tayi kana cikin sanyin tace.
“Ayyah Dije yayan Asma'u Malam Jameel Allah ya masa rasuwa kwanan nan ƴan Kidnapping suka kashesa!”.
Cike da tausayawa Dije tace.
“Ayyah Ubangiji Allah yajiƙan sa da rahma sukuma Allah ya tona musu asiri”.
Atare Asma'u da Khausar suka amsa da.
“Ameen”.
Asma'u kuwa Idanunta ne suka ciko da ruwan hawaye.
Cikin sanyi Khausar ta dafa kafaɗar ta kana tace.
“Dan Allah Asma'u kiyi haƙuri kin sani babu abinda Yah Jameel ke buƙata awajenmu face addu'a Insha Allah Yah Jameel na cikin rahamar Allah”.
Jinjina kai Asma'u tayi kana cikin sanyin murya tace.
“Insha Allah muna yi kuma zamu cigaba dayi”.
Miƙewa Asma'u tayi tare da kallon khausar cikin sanyin murya tace.
“Toni zan tafi”.
Da sauri Khausar ta ɗago kanta cike da kulawa tace.
“Sauri-sauri haka”.
Kai Asma'u ta gyaɗa tare da lumshe Idanunta cikin sanyin murya daya zame mata jiki tace.
“Wallahi gidan Innayi nake son zuwa dama na biyo ne akan ince muje ki rakani kuma sai na ganki da baƙuwa, shiyasa nayi shiru bance komai ba”.
Ajiyar zuciya Khausar ta sauke tare da tsira mata ido cikin fesar da numfashi tace.
“Ayyah wallahi kuwa badan baƙuwar ba ai da naje na rakaki amma lafiya kuwa?”.
Kai Asma'u ta gyaɗa tana gyaran zaman hijabinta tace.
“Eh Ummi ce ta aikeni wajen Innayi akan Inje wajen.
Yaya Moddibo yau kusan sati kenan bai sake zuwa gidanmu ba sannan kuma Innayi ma ta kirata tana faɗa mata ko cikin gida baya fita”.
Jinjina kai Khausar tayi cike da tausayinsu tace.
“Allah sarki Malam Moddibo dole ya shiga cikin tashin hankali da alhinin rashin.
Yah Jameel insha Allahu jinin Yah Jameel da hakkinmu ba zai taɓa bari wannan mutanen su samu salama acikin rayuwarsu ba!”.
Kai Asma'u ta gyaɗa cikin sheshsheƙan Kuka tace.
“Tabbas sun cutar da rayuwar mu, cuta mafi muni sun zalunce mu kana sun ɗauke mana duk wani farin ciki da walwalarmu. Yah Jameel shine Komai namu Yah Jameel shine fitilar dake haska zukatanmu amma dare ɗaya suka rabamu da wannan hasken kuma jigonmu”.
Cikin sanyi da tausayawa Dije tace.
“Asmau'u kiyi haƙuri Allah baya zalunci sannan baya bari ayi zalunci da sannu Ubangiji zai fallasa asirin wanda suka aikata wannan ta'asar sannan sai sun wulaƙanta wulaƙanci mai muni insha Allah”.
Cikin sanyi da Khausar da su kaji mutuwar ya dawo musu sabo suka hada baki wajen cewa.
“Ameen”.
Miƙewa Asma'u tayi tare da faɗi.
“Bari na tafi dan Ummi tayi ta kiran wayarsa baya ɗauka sannan itama Ummi baki daya bata jin daɗin jikinta sosai ta dawo tamkar majinyaciya.
Khausar sai kinga gidanmu baki ɗaya duniyar bata mana daɗi”.
Cikin sanyin da rarrashi Khausar tace.
“Ayyah Asma'u am haka rayuwa ta gada Ubangiji Allah ya jikan Yah Jameel da rahma mu kuma Ubangiji yasa mana dangana azuciyarmu sannan mu cigaba dayi masa addu'a gatan da zamu nuna masa kenan”.
Kai Asma'u ta gyaɗa kana tace.
“in sha Allah, na tafi”.
Kai Khausar ta gyaɗa sannan ta kalli Dije tace.
“Muje mu rakata”.
Miƙewa Dije tayi sannan suka fita bayan Asma'u ta yiwa Mommy da Hajja Nana sallama har bakin hanya suka rakata saida ta samu adaidaita ta hau sannan suka koma.
Asma'u na isa gidan direct Sashen Innayi ta nufa zaune ta hango Innayi kan barandar ta tayi tagumi da hannunta na dama jin anɓude ƙofa yasa tayi saurin ɗaga kanta ganin Asma'u yasa ta saki Ajiyar zuciya.
Cikin sanyi Asma'u ta ƙarasa tare da zama agefenta cikin sanyin murya tace.
“Innayi”.
Numfashi Innayi ta fesar tare da tsira mata ido cikin alamun damuwa tace.
“Na'am Asma'u kin zo ya jikin Umminki!?”.
Kanta aƙasa tace.
“Innayi da sauƙi Ina Yah Moddibo fa?”.
Ajiyar zuciya me nauyi Innayi taja kafin ta sauƙe cike da damuwa tace.
“Asma'u bansan wani irin yanayi Moddibo yake ƙoƙarin shiga ba baki ɗaya ya zama wani iri ya dawo tamkar mara lafiya ya zama abin tausayi koda fitowa bayayi”.
Sai kuma ta runtse Idanunta cike da damuwa kana ta buɗe su tare da cewa.
“Ko abinci idan bana nuna masa ɓacin raina ba baya ci banda ruwan tea Babu abinda yake sha baki ɗaya ya sauya duk hankalina ya tashi na rasa yanda zanyi.
Gaba daya ƙasar nan tafi raina duniyar ta isheni”.
Sunkuyar da kai Asma'u tayi tana jin hawaye na cika kwarmin Idanunta.
“Ke ko kunya bakya ji dube ki fa duk kin gama girma agida shekarunki kusan Ashirin ai wannan ma taumaka miki za'ayi dan kin gama tsufa”.
Buɗe baki Khausar tayi tare da kallon kanta kana ta kalli Hajja Nana cike da Isa Hajja Nana tace.
“Kalleni da kyau yo ƙarya na miki, ƙannen bayanki nawa aka Aurar wasu da yara bibbiyu wasu kuma ɗaddaya ke kam wannan wani sai dai yace bazawara ce ke dan kin gama girma”.
Wani kallo Khausar ta mata tare da cewa.
“A'a Hajja Nana ya isa haka cin fuska dan wlh bazan juraba.Wanda suka fini dubu nawa ne basuyi Aure ba, sai dai idan A Rugar kune ake irin wannan Auren, amma nikam yanzu ma nayi ƙarama da Aure.
Mommy kuwa kallon Khausar tayi tare da ɗaga mata hannu kana tace.
“Haka naki Khausar kiyi mana shiru”.
Sunkuyar da kanta ƙasa tayi batare da ta sake cewa Uffan ba kawai dai tasan in ba ita ke tare Hajja Nana ba Mommy kam ba abinda zatace tanaji tana gani za'a tauyeta.
Hajja Nana Khausar ta nunata da ɗan yatsa tace.
“Ki kiyayeni bada ke nake magana ba fitsararriya mara kunya!”.
Gyara zama Khausar tayi tare da juya mata manyan Idanunta da kawar da kai gefe.
Murmushi Dije dake gefen Khausar tayi tare da riƙe hannun ta da ido tayi mata alamar ta daina.
Gyaran murya Hajja Nana tayi tare da cewa.
“Aysha Ni dake nake magana bada Khausar ba, ya batun maganar da mukayi tunda Allah yasa tagama yanzu, sannan makon daya gabata Baffanta yazo daga Adamawa aranan daya zo aranan ya koma”.
Sai kuma ta kalli Khausar tare da watsa mata Harara kana ta maida kallonta kan Mommy dake sauraronta tace.
“Toh dama ace yazo da niyyar kwana zamu ƙara so nan, ayi magana to amma ke me kikace tsakaninta da Aliyu ɗan Uwanta!?”.
Ahankali Mommy ta sunkuyar da kanta ƙasa kana tayi shiru cikin yanayin sanyinta da Kawaici, da mutumtaka da kuma kamala tace.
“Toh Hajja Nana wannan magana duk yanda kuka zantar ai hakane Baffanta shine me Aurar da ita, dan haka duk abinda ya yanke akanta shine dai-dai”.
Jinjina kai Hajja Nana tayi tare da tura kallabin kanta kana ta gyara zamanta cikin jin daɗi tace.
“Shima yace min Insha Allah nan da wata ɗaya ko sati uku zai zo idan ya samu sarari zaizo su zanta da Uban goyon yarinyar, shima abashi mutuncinsa tunda shi ya raineta tun tana da wata wata uku shi yamata komai”.
Kai Mommy ta gyaɗa tare da faɗin.
“Bakomai duk abinda kuka tsara yayi Idan har Auren Khausar da ɗan Uwanta Al'khairi ne Allah ya tabbatar mana da alkhairinsa”.
Cikin sauri Khausar ta tura bakinta tare da cewa.
“Ni dai bana sonshi kuma ke dai Mommy ayita Addu'ar alkhairi”.
Wani kallo Mommy ta watsa mata alamar rufe min baki, shiru Khausar tayi tare da sunkuyar da kanta ƙasa Mommy kuwa kallon Hajja Nana tayi cikin sanyin murya tace.
“Ni dai Allah ya tabbatar da al'khairi idan al'khairi ne Allah ya tabbatar ya kuma zaɓa musu abinda yafi zama al'khairi atsakanin su.
Gyara zama Hajja Nana tayi kana tace.
“Ammen,Kuma Insha Allahu ma alkhairi ne”.
Kai Mommy ta gyaɗa tare da cewa.
“Adduar da mukeyi kenan”.
Miƙewa Khausar tayi tare da riƙe hannun Dije da alamun ɓacin rai tace.
“Dije mu tafi”.
Harara Hajja Nana ta watsa mata tare da sake tura daurin Kallabinta gaba kana tace.
“Aikuwa wannan magana ya zama dole ki saurareta tunda batu ne na Aurenki akeyi”.
Cikin ƙankance Ido Khausar tace.
“Nifa bazanyi Aureba ehe ke baki da aiki sai ƙaƙale ƙaƙalen magana ina ruwanki da batun Aurena!?”.
Afusace ta kalleta kana tayi Ƙwaffa tare da cewa.
“Aikuwa dan Ubanki nike da ruwa dake kuma dole kiyu Aure”.
cikin tsirawa Hajja Nana ido tace.
“Amma dai na faɗa miki ki daina zagin mahaifina Aure kuwa idan Allah ya nufa zanyi amma ba wanda kike cewa ba kam!?”.
Ajiyar zuciya Hajja Nana ta sauke kana tana kallonta bako ƙyaftawa sai kuma ta sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.
“To wa kike so ki Aura?”.
Juya ido Khausar tayi tare da cewa.
“Aini nasan wanda zan Aura, kuma dan haka babu ruwanki dani sai kace ke lokacin da zaki yi Aure zaɓa miki wanda zaki Aura akayi ba ke kika zaɓa da kanki ba!”.
Girgiza kai Mommy tayi tare da nunawa Khausar hanya da hannu alamar tabar wajen ita har ga Allah bata so ma Hajja Nana ta tsaida Khausar a cikin mgnar ba in bana tsohuwaba taya zata tsaida Khausar bayan tasan yadda suke da juna.
Tura baki Khausar tayi tare da jan hannun Dije dake murmushi sam bata gajiya da kallon Dramer Khausar da Hajja Nana.
Khausar da Dije na isa ƙofar Bedroom ɗin zasu shiga Akuma dai-dai lokacin Asma'u tayi sallama cike da ladabi tsugunna agaban Mommy ta gaisheta Cike da kulawa Mommy ta amsa tare da tambayarta ya Umminta ta amsa da tana lafiya.
Kana ahankali ta maida kallonta kan Hajja Nana dake cin Inabi tace.
“Hajja Nana inayini fatan kunzo lafiya?”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da cewa.
“Lafiya lau Alhamdulillah Allah ya miki albarka kar dai ki riƙa ɗaukar hallayar wasu ƙawaye na tsiwa”.
Ɗan murmushi Asma'u tayi kana cikin sanyi ta gyaɗa kanta Khausar dake tsaye bakin ƙofa ta wani ɓata fuska tare da kawar da kai gefe.
Miƙewa Asma'u tayi ta nufi wajensu Khausar suka shiga Bedroom cikin ɗan sakin fuska da sanyi Asma'u tace.
“A Dije sannu da zuwa ya gida ya mutanen Jauro yaya!?”.
Murmushi Dije tayi cikin yanayin sanyin ta tace.
“Duk lafiya lau?”.
Kallon Dije Khausar tayi kana cikin sanyin tace.
“Ayyah Dije yayan Asma'u Malam Jameel Allah ya masa rasuwa kwanan nan ƴan Kidnapping suka kashesa!”.
Cike da tausayawa Dije tace.
“Ayyah Ubangiji Allah yajiƙan sa da rahma sukuma Allah ya tona musu asiri”.
Atare Asma'u da Khausar suka amsa da.
“Ameen”.
Asma'u kuwa Idanunta ne suka ciko da ruwan hawaye.
Cikin sanyi Khausar ta dafa kafaɗar ta kana tace.
“Dan Allah Asma'u kiyi haƙuri kin sani babu abinda Yah Jameel ke buƙata awajenmu face addu'a Insha Allah Yah Jameel na cikin rahamar Allah”.
Jinjina kai Asma'u tayi kana cikin sanyin murya tace.
“Insha Allah muna yi kuma zamu cigaba dayi”.
Miƙewa Asma'u tayi tare da kallon khausar cikin sanyin murya tace.
“Toni zan tafi”.
Da sauri Khausar ta ɗago kanta cike da kulawa tace.
“Sauri-sauri haka”.
Kai Asma'u ta gyaɗa tare da lumshe Idanunta cikin sanyin murya daya zame mata jiki tace.
“Wallahi gidan Innayi nake son zuwa dama na biyo ne akan ince muje ki rakani kuma sai na ganki da baƙuwa, shiyasa nayi shiru bance komai ba”.
Ajiyar zuciya Khausar ta sauke tare da tsira mata ido cikin fesar da numfashi tace.
“Ayyah wallahi kuwa badan baƙuwar ba ai da naje na rakaki amma lafiya kuwa?”.
Kai Asma'u ta gyaɗa tana gyaran zaman hijabinta tace.
“Eh Ummi ce ta aikeni wajen Innayi akan Inje wajen.
Yaya Moddibo yau kusan sati kenan bai sake zuwa gidanmu ba sannan kuma Innayi ma ta kirata tana faɗa mata ko cikin gida baya fita”.
Jinjina kai Khausar tayi cike da tausayinsu tace.
“Allah sarki Malam Moddibo dole ya shiga cikin tashin hankali da alhinin rashin.
Yah Jameel insha Allahu jinin Yah Jameel da hakkinmu ba zai taɓa bari wannan mutanen su samu salama acikin rayuwarsu ba!”.
Kai Asma'u ta gyaɗa cikin sheshsheƙan Kuka tace.
“Tabbas sun cutar da rayuwar mu, cuta mafi muni sun zalunce mu kana sun ɗauke mana duk wani farin ciki da walwalarmu. Yah Jameel shine Komai namu Yah Jameel shine fitilar dake haska zukatanmu amma dare ɗaya suka rabamu da wannan hasken kuma jigonmu”.
Cikin sanyi da tausayawa Dije tace.
“Asmau'u kiyi haƙuri Allah baya zalunci sannan baya bari ayi zalunci da sannu Ubangiji zai fallasa asirin wanda suka aikata wannan ta'asar sannan sai sun wulaƙanta wulaƙanci mai muni insha Allah”.
Cikin sanyi da Khausar da su kaji mutuwar ya dawo musu sabo suka hada baki wajen cewa.
“Ameen”.
Miƙewa Asma'u tayi tare da faɗi.
“Bari na tafi dan Ummi tayi ta kiran wayarsa baya ɗauka sannan itama Ummi baki daya bata jin daɗin jikinta sosai ta dawo tamkar majinyaciya.
Khausar sai kinga gidanmu baki ɗaya duniyar bata mana daɗi”.
Cikin sanyin da rarrashi Khausar tace.
“Ayyah Asma'u am haka rayuwa ta gada Ubangiji Allah ya jikan Yah Jameel da rahma mu kuma Ubangiji yasa mana dangana azuciyarmu sannan mu cigaba dayi masa addu'a gatan da zamu nuna masa kenan”.
Kai Asma'u ta gyaɗa kana tace.
“in sha Allah, na tafi”.
Kai Khausar ta gyaɗa sannan ta kalli Dije tace.
“Muje mu rakata”.
Miƙewa Dije tayi sannan suka fita bayan Asma'u ta yiwa Mommy da Hajja Nana sallama har bakin hanya suka rakata saida ta samu adaidaita ta hau sannan suka koma.
Asma'u na isa gidan direct Sashen Innayi ta nufa zaune ta hango Innayi kan barandar ta tayi tagumi da hannunta na dama jin anɓude ƙofa yasa tayi saurin ɗaga kanta ganin Asma'u yasa ta saki Ajiyar zuciya.
Cikin sanyi Asma'u ta ƙarasa tare da zama agefenta cikin sanyin murya tace.
“Innayi”.
Numfashi Innayi ta fesar tare da tsira mata ido cikin alamun damuwa tace.
“Na'am Asma'u kin zo ya jikin Umminki!?”.
Kanta aƙasa tace.
“Innayi da sauƙi Ina Yah Moddibo fa?”.
Ajiyar zuciya me nauyi Innayi taja kafin ta sauƙe cike da damuwa tace.
“Asma'u bansan wani irin yanayi Moddibo yake ƙoƙarin shiga ba baki ɗaya ya zama wani iri ya dawo tamkar mara lafiya ya zama abin tausayi koda fitowa bayayi”.
Sai kuma ta runtse Idanunta cike da damuwa kana ta buɗe su tare da cewa.
“Ko abinci idan bana nuna masa ɓacin raina ba baya ci banda ruwan tea Babu abinda yake sha baki ɗaya ya sauya duk hankalina ya tashi na rasa yanda zanyi.
Gaba daya ƙasar nan tafi raina duniyar ta isheni”.
Sunkuyar da kai Asma'u tayi tana jin hawaye na cika kwarmin Idanunta.