Sashe 26
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Khausar na fitowa daga kichen ta girgiza kai tare da kallon Asma'u tace.
“Toh ni zan tafi sai anjima”.
Da mamaki Asma'u ta kalleta kana tace.
“Bangane ba kamar ya sauri kike?
Dama ba nan kika zoba ne?”.
Khausar kuwa kai ta girgiza tare da kallonta kana tace.
“A'a ba nan nazo ba dama gidan Aunty Ruƙayya naje to da naje sai na sameta tare da baƙi shine na kira Mommy nace zan ƙaraso nan mu gaisa.
Mommy kam cewa tayi wai da safiyar nan zanzo”.
Moddibo kuwa tunda yaji sautin Muryanta akusa dashi ya kasa ɗauke idanunsa akanta duk da cewa kallon Kasan ido yake mata.
Cikin sanyi Khausar ta cigaba da cewa.
“Toh shine nace tayi hakuri ba daɗewa zanyi ba shine fa tace inzo amma kada in daɗe saboda mune da aikin rana zan koma in ta yata nazo muyi wata mgna ce, kuma nafasa”.
Da sauri Asma'u tace.
“Dan Allah muyita”.
Kai ta jujjuya tare da cewa.
“Ba damuwa in kin samu dama kizo zamuyita, yanzun sauri nake”.
Ta ida maganar tare ɗago kanta.
Idanunta ne suka sauƙa cikin idanun Moddibo.
Atsorace ta zira Idonta cikin nasa tare da juya su acikin nasa wanda hakan ya zama kamar hararansa tayi ita kuma cikin mamakin yadda ya rame ya wani zama shiru, ne yayi matuƙar bata mamaki da tausayi domin da dane da tuni ya danna mata harara.
Cike da tsoro ta janye kwayar idanunta daga garesa, tana mai mamakin sauyinsa rayuwa, cikin wani irin sauri ta nufi ƙofar falon yayin da jikinta ke tsuma Muryanta na rawa tace.
“Ummi ni na tafi”.
Kallon yanda ta nufi ƙofar Ummi tayi kana ta kallo Moddibo da har zuwa lokacin idanunsa ke ƙasa da mamaki tace.
“Ya da sauri kamar kinga Dodo?”.
Kai ta girgiza batare data juya ba tace.
“A'a Ummi nikam na tafi”.
Cike da kulawa Ummi tace.
“Toh ki tsaya Kiyi breakfast mana”.
Kai ta girgiza still jikinta na tsuma tace.
“A'a Ummi Allah Mommy na za tayi faɗa idan na daɗe”.
Jinjina kai Ummi tayi kana tace.
“Toh shikenan nagode ki gaida Mommy ki gashi kin ki kitsaya kiyi breakfast”.
Da sauri tace.
“Allah Ummi sai da nayi breakfast agida kafin na fito”.
Kai Ummi ta gyaɗa kana tace.
“Ki gaida Mommy naki da Raudat dasu Haiydar”.
Cikin sauri ta fice daga falon bayan tace zasuji.
Moddibo kuwa ahankali ya jinginar da kansa da jikin kujeran tare da lumshe Idanunsa kana ya cije Lip ɗinsa na ƙasa, sai kuma yayi saurin buɗesu sabida ganin surar jikinta da yayi ziraran miraran.
Gashi da zaran yaji muryan yarinyar zai riƙa jin wani irin abu mai wuyar fassarawa kana lokacin da ƙwayar idanunsu suka haɗu babu abinda suka hango masa face.
Ƙirjinta tamkar zasu tsole mishi idanu.
Asma'u Mommy tasa ta kawo masa ɗan waken da sukayi sai ruwan Tea ba laifi yaci danwaken da ɗan dama kana yasha ruwan Tea.
Malam Ahmad ne yashigo tare da yi masa addu'ar Allah ya tsare miƙewa yayi ya fita kana yaja tsohuwar motarsa zuwan gidan Abba yana isa yayi Hong mai gadi ya buɗe masa Parking Yayi aharabar gidan kana yashiga sashen Abba bakinsa ɗauke da sallama ya shiga falon Cike da kulawa Abba da Hajiya Turai dake zaune gefensa suka amsa masa.
Anutse ya ƙarasa tare da zama gefen Abba cike da kulawa Abba yace.
“Aliyu ka ƙara so?”.
Jinjina kai Moddibo yayi cikin sanyin murya yace.
“Eh Abba ina kwana ya ƙarfin jikin”.
“Jiki da sauƙi Aliyu”.
Bayan sun gama gaisawa Abba yayiwa Moddibo duk kan wasu bayanai kana ya bashi wasu takardu da duk wani abu daya kamata sai da Abba ya masa bayani.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe kana yace.
“Toh Abba ni zan tafi”.
Ahankali Abba ya sanya hannu a aljihu tare da ciro key mota sabo dal ƙiran PRADO ya miƙa Masa tare da cewa.
“Ga wannan Aliyu za'a kaika Airport dashi, in Manu driver ya dawo kuma gidan ku zaije ya ajiye maka ita”.
Cikin sauri Moddibo ya ɗago kansa tare da Kallonsa.
“Abba mota kuma?”.
Kai Abba ya gyaɗa masa alamar eh.
Cikin sanyi Moddibo ya sake kallon key motar kana yace.
“Abba to ai ina da mota”.
Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana yace.
“Uhm-Uhm Aliyu kenan. Ɗan Allah kada kayi min gardama ka karɓa kawai ka sanya albarka aciki”.
Sunkuyar da kai Moddibo yayi batare da da yace Uffan ba.
Kallonsa Hajiya Turai tayi kana tace.
“Ka karɓa mana Aliyu ai yanzu kam an zama ɗaya”.
Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.
“Toh shikenan Abba Nagode Allah yasaka da Akhairi Ubangiji Allah ya mayar maka da dubunsa”.
Murmushi Abba yayi kana yace.
“Ameen”.
Nan take ya ɗauko takardun motar ya miƙa masa tare da cewa.
“Jiya mukayi magana da Alhj Abubakar nasa ya kawo min da yamma gatanan lafiyarta ƙalau anyi mata dukkan abinda ya dace”.
Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.
“Nagode Abba Allah yasaka da alkhairi ni zan tafi”.
Ahankali Abba yace.
“Allah ya tsare Aliyu Allah ya bada abinda akaje nema”.
Ameen ya amsa kana ya miƙe Abba ya rakasa da kansa ya buɗe masa bayan motar ya shiga, sabuwar motarsa sosai motar ta burgesa duda bai wani damu da bakin abuba, amman collor bakin yayi masifar kyau dan sai sheƙin sabunta takeyi,
Manu ne ya shiga yaja motar suka fita.
Kai tsaye gidan Malam Arɗo ya wuce dashi bisa umarninsa.
Sallama yayi masa kana daga nan suka ɗauki hanyar da zata sadasu da cikin Taraba Jaligo ja gari na Baba Abasu babban birnin Gembila kenan wanda kuma tsakanin local government ɗin nasu zuwa cikin ƙwaryar birnin Taraban tafiyace ta musamman.
Koda suka isa cikin Taraba, basu tsayaba suka nausa hanyar Adamawa Yola.
Jauro yaya
Baffan Liman ne zaune agaban Hajja Nana cikin sanyi murya da ladabi yayi ƙasa da kansa tare da cewa.
“Hajja kiyi haƙuri bai kamata ace kina fushi akan abinda bai kai ya kawoba, wannan al'amari ba wani al'amari mai girma bane bai kamata ace ki ɗauki zafi akansa har haka ba”.
Kallonsa kawai Hajja Nana keyi tana girgiza ƙafa tare da girgiza kai.
Ajiyar zuciya Baffa Liman ya sauke kana ya cigaba da cewa.
“Idan kin lura Khausar fa jika ce agareki ba ƴa bace, kinga kuwa duk ikon ka akan jika yana zama mai rauni, bare wannan zamanin da muke ya bambanta dana baya dan Allah Addah Hajja kiyi wa wannan al'amarin Kyakkyawan fahimta”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da fesar da numfashi kana tace.
“Na lura sannan na fahimci Liman da kai dasu Garga, Sadu, Jauro baki ɗaya bakin ku ɗaya akan al'amarin Khausar tun da haka kuka ce ni bani da abinda zance kuje kuyi duk yanda kuka ga dama”.
Ahankali Baffa Liman ya ɗago ya kalleta kana ya sake sunkuyar da kansa.
Cikin alamun ɓacin rai ta cigaba da cewa.
“Amma fa kusa ni ba zata Auri wannan yaron ba, tunda har ta iya buɗe baki ta kalli tsabar idona tace bata son. Aliyu jikina kuma ɗan Uwanta toni babu hannu na akanta kuyi mata yanda take so amma banda Auren mara tushe da asali”.
Gyaran murya Baffa Garga yayi kana yace.
“Dan Allah Addah Hajja kiyi haƙuri shikansa. Muhammadu Jimeta yace zai zo amma yafi so yazo ya sameki cikin farin ciki kada akan batun Khausar ranki ya dinga ɓaci abanza a wofi”.
Fuska ta ɓata tare da Kallonsu ɗaya bayan ɗaya kana tace.
“Idan yayi niyyar zuwa yazo idan kuma baiyi niyyar zuwa ba yayi ta zama tunda shi kansa bayanta yake bi, tun da wai har cewa yake bazai yi mata dole ba”.
Baffa Liman ya sake sassauta muryarsa yace.
“Dan Allah Addah Hajja kiyi haƙuri ki bi lamarin asannu da izinin Ubangiji komai zai dai-dai-ta amma bama son ganinki cikin damuwa”.
Haka suka riƙa Rarrashinta tare da kalamai masu kwantar da zuciya.
Acan ɓangaren Moddibo kuwa tafiya tsakanin Taraba da Yola tafiya ce mai zaman kanta sai dai bata wuce awa biyu zuwa uku, tuƙi Manu keyi cike da ƙwarewa ga samun sabuwar mota.
Shi kuwa Modibbo a hankali ya fesar da sassayan numfashi.
Sabida ji yake wani irin yanayi yana lullubeshi gaba ɗaya tunanin J ɗin sa ya dawo masa ji yake tamkar idan ya juya gefen damansa zai ga J ɗin sa, ahankali ya zira hannunsa ya kara volume din ƙira'ar da yake ji acikin Suratul Nisa'i, sai kuma ya koma baya ya jingina bayanshi da jikin Seat ɗin.
Domin idan har ba karatu yake jiba ko kuma yake yi sam baya taɓa samun nutsuwa, saidai kuma ta wani ɓangaren haka nan yake jin wani irin farin ciki da yabar garin Gembila, ji yake tamkar yabar wani yanki da yake da tarin ƙunci, ji yake tamkar yabar wani waje mai duhu da zafi ji yake tamkar ana zare ransa da ruhinsa daga waje mai ƙunci da azaba, kana kamar ana nufar dashi awaje mai tarin nutsuwa da salama yakeji.
Domin tun bayan rasuwar Amininsa garin Gembila tayi masa zafi da ƙunci kana tayi masa duhu baya kallon haskenta gaba ɗaya ya tsani garin, to dama Meya rage masa da garin Innayinsa ce kaɗai sai kuma Ummi dasu Asma'u.
Sai Misalin ƙarfe biyu da rabi ya shiga cikin Adamawa suna isa cikin Adamawa.
Manu yayi Parking A dai-dai Masallacin jum'ae dake cikin Atiku Abubakar shopping mall ɗinsu nan sukayi Al'wala sukayi sallar Azahar Kasancewar hanya zai kama, ɗan tafiya yasa a gaba shiyasa yayi niyar ƙasaru ya haɗa da sallar La'asar domin karfe uku dai-dai jirginsu zai tashi.
Baya jin zai iya cin wani abu haka yasa ya kalli Manu cikin mutuntaka yace.
“Manu sannu da yunwa”.
Cikin girmamawa Manu yace.
“Laa ba komai ai kafin mu fito ma naci abinci”.
Kai ya jinjina kana yace.
“Muje ka kaini cikin Airport ɗin, sai kayi sauri ka juya, kada kayi dare a komawa”.
Cike da gamsuwa Manu yace.
“Toh”.
Daga nan ya kaishi Airport sannan shi kuma ya fito, ya ɗan samu abin da ya taɓa kana ya kama hanyar komawa Taraba, Gembila.
Ƙarfe uku Dai-dai jirginsu Modibbo ya tashi daga Adamawa zuwa birnin tarayyar Nigeria Abuja.
“Toh ni zan tafi sai anjima”.
Da mamaki Asma'u ta kalleta kana tace.
“Bangane ba kamar ya sauri kike?
Dama ba nan kika zoba ne?”.
Khausar kuwa kai ta girgiza tare da kallonta kana tace.
“A'a ba nan nazo ba dama gidan Aunty Ruƙayya naje to da naje sai na sameta tare da baƙi shine na kira Mommy nace zan ƙaraso nan mu gaisa.
Mommy kam cewa tayi wai da safiyar nan zanzo”.
Moddibo kuwa tunda yaji sautin Muryanta akusa dashi ya kasa ɗauke idanunsa akanta duk da cewa kallon Kasan ido yake mata.
Cikin sanyi Khausar ta cigaba da cewa.
“Toh shine nace tayi hakuri ba daɗewa zanyi ba shine fa tace inzo amma kada in daɗe saboda mune da aikin rana zan koma in ta yata nazo muyi wata mgna ce, kuma nafasa”.
Da sauri Asma'u tace.
“Dan Allah muyita”.
Kai ta jujjuya tare da cewa.
“Ba damuwa in kin samu dama kizo zamuyita, yanzun sauri nake”.
Ta ida maganar tare ɗago kanta.
Idanunta ne suka sauƙa cikin idanun Moddibo.
Atsorace ta zira Idonta cikin nasa tare da juya su acikin nasa wanda hakan ya zama kamar hararansa tayi ita kuma cikin mamakin yadda ya rame ya wani zama shiru, ne yayi matuƙar bata mamaki da tausayi domin da dane da tuni ya danna mata harara.
Cike da tsoro ta janye kwayar idanunta daga garesa, tana mai mamakin sauyinsa rayuwa, cikin wani irin sauri ta nufi ƙofar falon yayin da jikinta ke tsuma Muryanta na rawa tace.
“Ummi ni na tafi”.
Kallon yanda ta nufi ƙofar Ummi tayi kana ta kallo Moddibo da har zuwa lokacin idanunsa ke ƙasa da mamaki tace.
“Ya da sauri kamar kinga Dodo?”.
Kai ta girgiza batare data juya ba tace.
“A'a Ummi nikam na tafi”.
Cike da kulawa Ummi tace.
“Toh ki tsaya Kiyi breakfast mana”.
Kai ta girgiza still jikinta na tsuma tace.
“A'a Ummi Allah Mommy na za tayi faɗa idan na daɗe”.
Jinjina kai Ummi tayi kana tace.
“Toh shikenan nagode ki gaida Mommy ki gashi kin ki kitsaya kiyi breakfast”.
Da sauri tace.
“Allah Ummi sai da nayi breakfast agida kafin na fito”.
Kai Ummi ta gyaɗa kana tace.
“Ki gaida Mommy naki da Raudat dasu Haiydar”.
Cikin sauri ta fice daga falon bayan tace zasuji.
Moddibo kuwa ahankali ya jinginar da kansa da jikin kujeran tare da lumshe Idanunsa kana ya cije Lip ɗinsa na ƙasa, sai kuma yayi saurin buɗesu sabida ganin surar jikinta da yayi ziraran miraran.
Gashi da zaran yaji muryan yarinyar zai riƙa jin wani irin abu mai wuyar fassarawa kana lokacin da ƙwayar idanunsu suka haɗu babu abinda suka hango masa face.
Ƙirjinta tamkar zasu tsole mishi idanu.
Asma'u Mommy tasa ta kawo masa ɗan waken da sukayi sai ruwan Tea ba laifi yaci danwaken da ɗan dama kana yasha ruwan Tea.
Malam Ahmad ne yashigo tare da yi masa addu'ar Allah ya tsare miƙewa yayi ya fita kana yaja tsohuwar motarsa zuwan gidan Abba yana isa yayi Hong mai gadi ya buɗe masa Parking Yayi aharabar gidan kana yashiga sashen Abba bakinsa ɗauke da sallama ya shiga falon Cike da kulawa Abba da Hajiya Turai dake zaune gefensa suka amsa masa.
Anutse ya ƙarasa tare da zama gefen Abba cike da kulawa Abba yace.
“Aliyu ka ƙara so?”.
Jinjina kai Moddibo yayi cikin sanyin murya yace.
“Eh Abba ina kwana ya ƙarfin jikin”.
“Jiki da sauƙi Aliyu”.
Bayan sun gama gaisawa Abba yayiwa Moddibo duk kan wasu bayanai kana ya bashi wasu takardu da duk wani abu daya kamata sai da Abba ya masa bayani.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe kana yace.
“Toh Abba ni zan tafi”.
Ahankali Abba ya sanya hannu a aljihu tare da ciro key mota sabo dal ƙiran PRADO ya miƙa Masa tare da cewa.
“Ga wannan Aliyu za'a kaika Airport dashi, in Manu driver ya dawo kuma gidan ku zaije ya ajiye maka ita”.
Cikin sauri Moddibo ya ɗago kansa tare da Kallonsa.
“Abba mota kuma?”.
Kai Abba ya gyaɗa masa alamar eh.
Cikin sanyi Moddibo ya sake kallon key motar kana yace.
“Abba to ai ina da mota”.
Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana yace.
“Uhm-Uhm Aliyu kenan. Ɗan Allah kada kayi min gardama ka karɓa kawai ka sanya albarka aciki”.
Sunkuyar da kai Moddibo yayi batare da da yace Uffan ba.
Kallonsa Hajiya Turai tayi kana tace.
“Ka karɓa mana Aliyu ai yanzu kam an zama ɗaya”.
Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.
“Toh shikenan Abba Nagode Allah yasaka da Akhairi Ubangiji Allah ya mayar maka da dubunsa”.
Murmushi Abba yayi kana yace.
“Ameen”.
Nan take ya ɗauko takardun motar ya miƙa masa tare da cewa.
“Jiya mukayi magana da Alhj Abubakar nasa ya kawo min da yamma gatanan lafiyarta ƙalau anyi mata dukkan abinda ya dace”.
Jinjina kai Moddibo yayi kana yace.
“Nagode Abba Allah yasaka da alkhairi ni zan tafi”.
Ahankali Abba yace.
“Allah ya tsare Aliyu Allah ya bada abinda akaje nema”.
Ameen ya amsa kana ya miƙe Abba ya rakasa da kansa ya buɗe masa bayan motar ya shiga, sabuwar motarsa sosai motar ta burgesa duda bai wani damu da bakin abuba, amman collor bakin yayi masifar kyau dan sai sheƙin sabunta takeyi,
Manu ne ya shiga yaja motar suka fita.
Kai tsaye gidan Malam Arɗo ya wuce dashi bisa umarninsa.
Sallama yayi masa kana daga nan suka ɗauki hanyar da zata sadasu da cikin Taraba Jaligo ja gari na Baba Abasu babban birnin Gembila kenan wanda kuma tsakanin local government ɗin nasu zuwa cikin ƙwaryar birnin Taraban tafiyace ta musamman.
Koda suka isa cikin Taraba, basu tsayaba suka nausa hanyar Adamawa Yola.
Jauro yaya
Baffan Liman ne zaune agaban Hajja Nana cikin sanyi murya da ladabi yayi ƙasa da kansa tare da cewa.
“Hajja kiyi haƙuri bai kamata ace kina fushi akan abinda bai kai ya kawoba, wannan al'amari ba wani al'amari mai girma bane bai kamata ace ki ɗauki zafi akansa har haka ba”.
Kallonsa kawai Hajja Nana keyi tana girgiza ƙafa tare da girgiza kai.
Ajiyar zuciya Baffa Liman ya sauke kana ya cigaba da cewa.
“Idan kin lura Khausar fa jika ce agareki ba ƴa bace, kinga kuwa duk ikon ka akan jika yana zama mai rauni, bare wannan zamanin da muke ya bambanta dana baya dan Allah Addah Hajja kiyi wa wannan al'amarin Kyakkyawan fahimta”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da fesar da numfashi kana tace.
“Na lura sannan na fahimci Liman da kai dasu Garga, Sadu, Jauro baki ɗaya bakin ku ɗaya akan al'amarin Khausar tun da haka kuka ce ni bani da abinda zance kuje kuyi duk yanda kuka ga dama”.
Ahankali Baffa Liman ya ɗago ya kalleta kana ya sake sunkuyar da kansa.
Cikin alamun ɓacin rai ta cigaba da cewa.
“Amma fa kusa ni ba zata Auri wannan yaron ba, tunda har ta iya buɗe baki ta kalli tsabar idona tace bata son. Aliyu jikina kuma ɗan Uwanta toni babu hannu na akanta kuyi mata yanda take so amma banda Auren mara tushe da asali”.
Gyaran murya Baffa Garga yayi kana yace.
“Dan Allah Addah Hajja kiyi haƙuri shikansa. Muhammadu Jimeta yace zai zo amma yafi so yazo ya sameki cikin farin ciki kada akan batun Khausar ranki ya dinga ɓaci abanza a wofi”.
Fuska ta ɓata tare da Kallonsu ɗaya bayan ɗaya kana tace.
“Idan yayi niyyar zuwa yazo idan kuma baiyi niyyar zuwa ba yayi ta zama tunda shi kansa bayanta yake bi, tun da wai har cewa yake bazai yi mata dole ba”.
Baffa Liman ya sake sassauta muryarsa yace.
“Dan Allah Addah Hajja kiyi haƙuri ki bi lamarin asannu da izinin Ubangiji komai zai dai-dai-ta amma bama son ganinki cikin damuwa”.
Haka suka riƙa Rarrashinta tare da kalamai masu kwantar da zuciya.
Acan ɓangaren Moddibo kuwa tafiya tsakanin Taraba da Yola tafiya ce mai zaman kanta sai dai bata wuce awa biyu zuwa uku, tuƙi Manu keyi cike da ƙwarewa ga samun sabuwar mota.
Shi kuwa Modibbo a hankali ya fesar da sassayan numfashi.
Sabida ji yake wani irin yanayi yana lullubeshi gaba ɗaya tunanin J ɗin sa ya dawo masa ji yake tamkar idan ya juya gefen damansa zai ga J ɗin sa, ahankali ya zira hannunsa ya kara volume din ƙira'ar da yake ji acikin Suratul Nisa'i, sai kuma ya koma baya ya jingina bayanshi da jikin Seat ɗin.
Domin idan har ba karatu yake jiba ko kuma yake yi sam baya taɓa samun nutsuwa, saidai kuma ta wani ɓangaren haka nan yake jin wani irin farin ciki da yabar garin Gembila, ji yake tamkar yabar wani yanki da yake da tarin ƙunci, ji yake tamkar yabar wani waje mai duhu da zafi ji yake tamkar ana zare ransa da ruhinsa daga waje mai ƙunci da azaba, kana kamar ana nufar dashi awaje mai tarin nutsuwa da salama yakeji.
Domin tun bayan rasuwar Amininsa garin Gembila tayi masa zafi da ƙunci kana tayi masa duhu baya kallon haskenta gaba ɗaya ya tsani garin, to dama Meya rage masa da garin Innayinsa ce kaɗai sai kuma Ummi dasu Asma'u.
Sai Misalin ƙarfe biyu da rabi ya shiga cikin Adamawa suna isa cikin Adamawa.
Manu yayi Parking A dai-dai Masallacin jum'ae dake cikin Atiku Abubakar shopping mall ɗinsu nan sukayi Al'wala sukayi sallar Azahar Kasancewar hanya zai kama, ɗan tafiya yasa a gaba shiyasa yayi niyar ƙasaru ya haɗa da sallar La'asar domin karfe uku dai-dai jirginsu zai tashi.
Baya jin zai iya cin wani abu haka yasa ya kalli Manu cikin mutuntaka yace.
“Manu sannu da yunwa”.
Cikin girmamawa Manu yace.
“Laa ba komai ai kafin mu fito ma naci abinci”.
Kai ya jinjina kana yace.
“Muje ka kaini cikin Airport ɗin, sai kayi sauri ka juya, kada kayi dare a komawa”.
Cike da gamsuwa Manu yace.
“Toh”.
Daga nan ya kaishi Airport sannan shi kuma ya fito, ya ɗan samu abin da ya taɓa kana ya kama hanyar komawa Taraba, Gembila.
Ƙarfe uku Dai-dai jirginsu Modibbo ya tashi daga Adamawa zuwa birnin tarayyar Nigeria Abuja.