Sashe 15
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Acan Falon Moddibo kuwa zaune yake akan Sallaya bayan ya idar da sallar Walha hannunsa riƙe da Alkur'ani yana karanta suratul Tauba yana Aya ta ɗari da ashirin da bakwai yaji wayarsa na Vibrating Kallon screen ɗin wayar yayi ganin sunan Abba yasa ya cigaba da karatun kasancewar saura Ayoyin biyun ƙarshe yasa ya cigaba yana ƙarasawa ya shafa addu'ar dai-dai lokacin wani sabon kiran ya sake shigowa.
Anutse ya ɗaga wayar tare da kaiwa Kunnensa yayi Sallama.
Cikin sanyin murya Abba ya amsa tare da cewa.
“Aliyu”.
Ahankali Moddibo yace.
“Na'am Abba ina kwana ya ƙarfin jikin naka?”.
Cikin sanyin murya Abba yace.
“Lafiya lau Alhamdulillah ya gida? Aliyu ya kwana biyu duk ban jika ba”.
Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauƙe kana yace.
“Wlh kuwa Abba ya ƙarfin jikin naka?”.
Ahankali Abba ya sauƙe numfashi kana yace.
“Jiki da sauƙi”.
gyara zamansa yayi tare da cewa.
“Toh Abba Allah ya ƙara sauƙi amma lafiya kuwa?”.
“Eh lfy lau. Yanzuma nayi waya da.
Mgnar Company na dake Marocco, to dama akwai kayan da mukayi Order sabbbin Injuna, sabida tsoffin sun fara samun matsala kasancewar sun kwana biyu to an kawo sabbin kuma Manager baya nan yaje duba lafiyarsa, kuma yanzu dole ana buƙatar sai akwai sahalewar wani da kuma sa hannu na kafin afara sauƙe kayan dole kuma akwai buƙatar tsayeyye da zai sa ido kan aikin kafa musarrafan da za'ayi”.
Tunda Abba ya fara magana Moddibo ya lumshe idanunsa yana cigaba da sauraron sa.
Abba ya cigaba da cewa.
“To yanemi da Inje, to ni kuma bazan iya ba, kullum ina fama da ciwon kai kuma kaga ga yanayin da nake ciki har yanzu ana zuwa min gaisuwa, shiyasa nake so ka shirya ka wakilceni, kaje ka fuskanci aikin idan yaso idan komai ya dai-dai-ta aka fara aiki in anyi rukunin forko saika dawo ba zaka daɗe ba”.
Moddibo kuwa shiru yayi tare da jingina bayansa da jikin Cushing.
Daga ɗaya ɓangaren Abba yace.
“Hello! Aliyu Hello!!, Hello!!! Aliyu kana jina kuwa?”.
Shi kuwa Moddibo cije Lip ɗinsa na ƙasa yayi Aransa yace bana son garin Gembila baki ɗaya jihar Taraba ta fitar masa ji yake tamkar wuta ake watsa masa aduk lokacin daya tuna shi kaɗaine ke rayuwa babu J ɗinsa, babu wani akusa dashi idan zai tafi masallaci shi kaɗai sannan idan zai dawo shi kaɗai kana idan zaici abinci shi kaɗai baki ɗaya ilahirin garin ya masa duhu kana ya masa ƙunci sam baya son zama acikinsa Nigeria kanta ta fice masa arai.
To amma kuma idan ya tafi Ummi ya zatayi.
Cikin sauri ya buɗe Idanunsa dake lumshe jin Abba na cewa.
“Aliyu ya dai kayi shiru baka ce komai ba?”.
Numfashi mai tsayi yaja kafin ya sauƙe ahankali cikin sanyin murya yace.
“Abba Ummi idan na tafi nayi nesa da Ummi ba zata ji daɗi ba sannan Innayina, da waye zan barta?”.
Ahankali Abba ya sauƙe Ajiyar zuciya tare da sauƙe dogon numfashi kana yace.
“Ba komai Aliyu Insha Allah za ayi ƙoƙari akula da duk kan al'amurran su sannan ba daɗewa zaka yiba”.
Cikin raunin murya Moddibo yace.
“Abba Ummi tace idan banje wajenta ba hankalinta na tashi damuwarta na tsananta. Abba bana son ganin Ummi cikin wani yanayi, Innayi na kuma bata da kowa a duniya saini in nayi nesa da ita ya zataji”.
Ajiyar zuciya Abba ya kuma sauƙe kana yace.
“Bakomai Insha Allah za muyi magana da Malam Ahmad za'a kwantar mata da hankalin ta, sannan dama inaso zamuyi magana dakai Innayi kuma kada ka damu zata iya dawowa gidana kafin ka dawo ko gidan Ummin”.
Ahankali Moddibo ya gyara zaman wayar akunnensa.
Yayinda Abba kuma ya cigaba da cewa.
“Akan kuɗin da aka har haɗa aka turo wanda Fatima ta saida Sarƙoƙinta da kuma motarta kazo zamuyi maganar ka karɓi kuɗin Asiya mata wata motar sannan sauran ta ajiye idan zata sai wasu kadarorin ma ta ajiye”.
A hankali ya gyara zamansa tare da rintse idanunsa kana ya cigaba da cewa.
“Sannan kaima naga motar da kake Amfani da ita tsohuwar mota ce ya kamata ka siya wata sabuwar motar ka riƙa hawa”.
Girgiza kai Moddibo yayi cikin raunin murya yace.
“Abba me zanyi da wata sabuwar mota Abba bana son Kuɗin dan Allah kadaina maganar Abba ni dai bana son Kuɗin Abba bana son su”.
Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da girgiza kai kana yace.
“A'a Aliyu ya za ayi kace haka?”.
Moddibo kuwa rumtse idanunsa yayi tare da taune Lip ɗinsa na ƙasa kana yace.
“Toh Abba me zanyi da kuɗin da suka kasa ceton min J me zanyi da kuɗin da suka kasa temakon ceto mun rayuwar J Abba bana son Kuɗin Abba dan Allah kada kayi min maganar kuɗin”.
Numfashi Abba ya fesar cikin sassauta murya yace.
“Aliyu kayi haƙuri dole muyi maganar kuɗin nan kaima kace baka son maganar kuɗin nan to ni kuma me zanyi dasu Aliyu kayi haƙuri kaji sannan dan Allah kayi ƙoƙari ka shirya ka tafi Marocco E PASSPORT naka zaka fitar dan Allah, mu fara neman damar fitan ko ta online zakayi komai, cikin makon nan nakeso ka tafin in Allah yasa ka samu buse”.
Shiru Moddibo yayi lokaci da yaji maganar Bashir ya dawo masa kunne na cewa yayi mafarki da M Jameel sannan yace ya faɗa masa cewa ya taya Abba harƙan kasuwancin sa dogon numfashi yaja mai sanyi duk da cewa baya so ya tafi ya bar Ummi da Innayi amma ji yake ya tsani zaman cikin Taraba da Gembila baki ɗaya Jahar Jaligo ta fita Aransa ga kuma tuno da abinda Bashir di ya faɗa ya sauƙe numfashi cikin sanyin murya yace.
“Toh shikenan Abba bari nayi magana da Innayi da Ummi”.
Kai Abba ya gyaɗa kana yace.
“Toh shikenan idan kunyi maganar dan Allah ka kirani yanzu yanzu ina jiranka”.
Cikin sanyin murya Moddibo yace.
“Toh shikenan ba matsala”.
Sannan ya katse kiran ya miƙe.
Acan ɗakin Innayi kuwa Hajja Nana na gama shan ruwan ta ajiye Cup ɗin tana sakin ajiyar zuciya.
Ahankali Innayi tace.
“Toh kici abinci”.
Girgiza kai tayi tare da faɗin.
“A'a bazan iya cin abinci ba barni kawai”.
Kallonta Innayi tayi kana tace.
“Toh Wai me ya tsananta ne har ya tayar miki da hankali haka?”.
Ƙwaffa Hajja Nana tayi tare da riƙe haɓa cike da takaici tace.
“Wai fa Khausar cewa tayi bata son Aliyu wai wani take so”.
Gyara zama Innayi tayi kana tace.
“Wai wani waye shi wanda take son?”.
Cikin fushi Hajja Nana taja dogon tsaki tare da cewa.
“Wai wani wai shi Moddibo take so Malamin Makarantar su inji Lamiɗo”.
Cikin sauri Innayi ta kalleta tare da jan dogon numfashi kana ta lumshe Idanunta tare da buɗe su cikin sanyi ta kalli Hajja Nana kana tace.
“Moddibo?".
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da faɗin.
“Eh Moddibo?”.
Jinjina kai Innayi tayi kana tace.
“Kuma wai malamin su?".
Still Kai Hajja Nana ta gyaɗa mata.
Anutse ya ɗaga wayar tare da kaiwa Kunnensa yayi Sallama.
Cikin sanyin murya Abba ya amsa tare da cewa.
“Aliyu”.
Ahankali Moddibo yace.
“Na'am Abba ina kwana ya ƙarfin jikin naka?”.
Cikin sanyin murya Abba yace.
“Lafiya lau Alhamdulillah ya gida? Aliyu ya kwana biyu duk ban jika ba”.
Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauƙe kana yace.
“Wlh kuwa Abba ya ƙarfin jikin naka?”.
Ahankali Abba ya sauƙe numfashi kana yace.
“Jiki da sauƙi”.
gyara zamansa yayi tare da cewa.
“Toh Abba Allah ya ƙara sauƙi amma lafiya kuwa?”.
“Eh lfy lau. Yanzuma nayi waya da.
Mgnar Company na dake Marocco, to dama akwai kayan da mukayi Order sabbbin Injuna, sabida tsoffin sun fara samun matsala kasancewar sun kwana biyu to an kawo sabbin kuma Manager baya nan yaje duba lafiyarsa, kuma yanzu dole ana buƙatar sai akwai sahalewar wani da kuma sa hannu na kafin afara sauƙe kayan dole kuma akwai buƙatar tsayeyye da zai sa ido kan aikin kafa musarrafan da za'ayi”.
Tunda Abba ya fara magana Moddibo ya lumshe idanunsa yana cigaba da sauraron sa.
Abba ya cigaba da cewa.
“To yanemi da Inje, to ni kuma bazan iya ba, kullum ina fama da ciwon kai kuma kaga ga yanayin da nake ciki har yanzu ana zuwa min gaisuwa, shiyasa nake so ka shirya ka wakilceni, kaje ka fuskanci aikin idan yaso idan komai ya dai-dai-ta aka fara aiki in anyi rukunin forko saika dawo ba zaka daɗe ba”.
Moddibo kuwa shiru yayi tare da jingina bayansa da jikin Cushing.
Daga ɗaya ɓangaren Abba yace.
“Hello! Aliyu Hello!!, Hello!!! Aliyu kana jina kuwa?”.
Shi kuwa Moddibo cije Lip ɗinsa na ƙasa yayi Aransa yace bana son garin Gembila baki ɗaya jihar Taraba ta fitar masa ji yake tamkar wuta ake watsa masa aduk lokacin daya tuna shi kaɗaine ke rayuwa babu J ɗinsa, babu wani akusa dashi idan zai tafi masallaci shi kaɗai sannan idan zai dawo shi kaɗai kana idan zaici abinci shi kaɗai baki ɗaya ilahirin garin ya masa duhu kana ya masa ƙunci sam baya son zama acikinsa Nigeria kanta ta fice masa arai.
To amma kuma idan ya tafi Ummi ya zatayi.
Cikin sauri ya buɗe Idanunsa dake lumshe jin Abba na cewa.
“Aliyu ya dai kayi shiru baka ce komai ba?”.
Numfashi mai tsayi yaja kafin ya sauƙe ahankali cikin sanyin murya yace.
“Abba Ummi idan na tafi nayi nesa da Ummi ba zata ji daɗi ba sannan Innayina, da waye zan barta?”.
Ahankali Abba ya sauƙe Ajiyar zuciya tare da sauƙe dogon numfashi kana yace.
“Ba komai Aliyu Insha Allah za ayi ƙoƙari akula da duk kan al'amurran su sannan ba daɗewa zaka yiba”.
Cikin raunin murya Moddibo yace.
“Abba Ummi tace idan banje wajenta ba hankalinta na tashi damuwarta na tsananta. Abba bana son ganin Ummi cikin wani yanayi, Innayi na kuma bata da kowa a duniya saini in nayi nesa da ita ya zataji”.
Ajiyar zuciya Abba ya kuma sauƙe kana yace.
“Bakomai Insha Allah za muyi magana da Malam Ahmad za'a kwantar mata da hankalin ta, sannan dama inaso zamuyi magana dakai Innayi kuma kada ka damu zata iya dawowa gidana kafin ka dawo ko gidan Ummin”.
Ahankali Moddibo ya gyara zaman wayar akunnensa.
Yayinda Abba kuma ya cigaba da cewa.
“Akan kuɗin da aka har haɗa aka turo wanda Fatima ta saida Sarƙoƙinta da kuma motarta kazo zamuyi maganar ka karɓi kuɗin Asiya mata wata motar sannan sauran ta ajiye idan zata sai wasu kadarorin ma ta ajiye”.
A hankali ya gyara zamansa tare da rintse idanunsa kana ya cigaba da cewa.
“Sannan kaima naga motar da kake Amfani da ita tsohuwar mota ce ya kamata ka siya wata sabuwar motar ka riƙa hawa”.
Girgiza kai Moddibo yayi cikin raunin murya yace.
“Abba me zanyi da wata sabuwar mota Abba bana son Kuɗin dan Allah kadaina maganar Abba ni dai bana son Kuɗin Abba bana son su”.
Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da girgiza kai kana yace.
“A'a Aliyu ya za ayi kace haka?”.
Moddibo kuwa rumtse idanunsa yayi tare da taune Lip ɗinsa na ƙasa kana yace.
“Toh Abba me zanyi da kuɗin da suka kasa ceton min J me zanyi da kuɗin da suka kasa temakon ceto mun rayuwar J Abba bana son Kuɗin Abba dan Allah kada kayi min maganar kuɗin”.
Numfashi Abba ya fesar cikin sassauta murya yace.
“Aliyu kayi haƙuri dole muyi maganar kuɗin nan kaima kace baka son maganar kuɗin nan to ni kuma me zanyi dasu Aliyu kayi haƙuri kaji sannan dan Allah kayi ƙoƙari ka shirya ka tafi Marocco E PASSPORT naka zaka fitar dan Allah, mu fara neman damar fitan ko ta online zakayi komai, cikin makon nan nakeso ka tafin in Allah yasa ka samu buse”.
Shiru Moddibo yayi lokaci da yaji maganar Bashir ya dawo masa kunne na cewa yayi mafarki da M Jameel sannan yace ya faɗa masa cewa ya taya Abba harƙan kasuwancin sa dogon numfashi yaja mai sanyi duk da cewa baya so ya tafi ya bar Ummi da Innayi amma ji yake ya tsani zaman cikin Taraba da Gembila baki ɗaya Jahar Jaligo ta fita Aransa ga kuma tuno da abinda Bashir di ya faɗa ya sauƙe numfashi cikin sanyin murya yace.
“Toh shikenan Abba bari nayi magana da Innayi da Ummi”.
Kai Abba ya gyaɗa kana yace.
“Toh shikenan idan kunyi maganar dan Allah ka kirani yanzu yanzu ina jiranka”.
Cikin sanyin murya Moddibo yace.
“Toh shikenan ba matsala”.
Sannan ya katse kiran ya miƙe.
Acan ɗakin Innayi kuwa Hajja Nana na gama shan ruwan ta ajiye Cup ɗin tana sakin ajiyar zuciya.
Ahankali Innayi tace.
“Toh kici abinci”.
Girgiza kai tayi tare da faɗin.
“A'a bazan iya cin abinci ba barni kawai”.
Kallonta Innayi tayi kana tace.
“Toh Wai me ya tsananta ne har ya tayar miki da hankali haka?”.
Ƙwaffa Hajja Nana tayi tare da riƙe haɓa cike da takaici tace.
“Wai fa Khausar cewa tayi bata son Aliyu wai wani take so”.
Gyara zama Innayi tayi kana tace.
“Wai wani waye shi wanda take son?”.
Cikin fushi Hajja Nana taja dogon tsaki tare da cewa.
“Wai wani wai shi Moddibo take so Malamin Makarantar su inji Lamiɗo”.
Cikin sauri Innayi ta kalleta tare da jan dogon numfashi kana ta lumshe Idanunta tare da buɗe su cikin sanyi ta kalli Hajja Nana kana tace.
“Moddibo?".
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da faɗin.
“Eh Moddibo?”.
Jinjina kai Innayi tayi kana tace.
“Kuma wai malamin su?".
Still Kai Hajja Nana ta gyaɗa mata.