Sashe 47
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Acan ɓangaren Moddibo kuwa jin ana ƙwala kiran sallar Maghriba yasanshi motsa laɓɓansa yashiga bin kiran Sallar kana yayi addu'ar da Manzon Allah (S.A.W)ya koyar sai kuma ya furta.
“Ya Salam, shin Mutanen nan me suke nufi dani, suna nufin ba zanyi Sallah acikin jam'i ba?”.
Ahankali ya juya idanunsa akan wannan Corridor dake gefen damansa cikin nutsuwa yabi hanyar yayi tafiya mai ɗan tsayi ya hango wasu ƙofofi guda biyu gefen hagu da dama ahankali ya murɗa ƙofar dake gefen dama.
“Ya Salam”.
Ya furta asaman laɓɓansa ganin wani tsarerren falo ahankali ya taka ya shiga ciki.
Sai kuma ya ɗan jujjuya kai, ƙofar dake kusa dashi ya nufa.
Wanda bedroom ne a hankali ya murɗa ya shiga.
Ƙofar bathroom ya sake murɗa yashiga, alwala kana ya fitowa.
Jujjuya ya kai yayi cikin sa'a yaga darduma a shimfiɗe a wata ƴar kusurwa awajen alamar ana sallah awajen anutse yayi sallar Maghriba awajen kana ya cigaba da addu'oi har aka kira Isha'i, bayan ya idar ya fito falon farko da aka fara ajiyesa.
Yana isa Idanunsa suka sauƙa akan dining da aka jera abinci kala-kala sai kuma ya juya kanshi hanyar shigowa nan yaga wasu hadimai guda uku maza suna tsaye.
Ganinsa yasa sukayi saurin sunkuyar da kansu ƙasa kana suka ɗaura hannunsu aƙirji alamar Barka da fitowa.
Cike da girmamawa ɗaya daga cikin su yace.
“Ranka ya daɗe ga abinci”.
Numfashi ya fesar kana ya tsira musu ido na second biyu tare da cewa.
“Shin meyesa aka tsareni anan?”.
Cike da ladabi da kuma Mutuntawa suke sake sunkuyar da kansu ɗaya daga cikinsu yace.
“Kayi haƙuri Ranka ya daɗe Umarni ne daga mai martaba yace kada mu bari a buɗe maka ƙofa dukkan abinda kake buƙata akwai shi anan basai ka fita ba”.
Cike da mmki ya kallesa kana ya lumshe idanunsa tare da fesar da iska mai zafi yace.
“Akan me za'a rufeni a hanani fita bayan ina da abubuwanyi”.
Cike da ladabi Hadimin ya sake sunkuyar da kansa wanda da alama shine babban su kana yace.
“Kayi haƙuri In Sha Allah Mai martaba yana nan zai zo wajenka”.
Batare daya sake furta komai ba ya koma ya zauna akan kujeran.
Allah ya sani shi yama rasa shin wani irin tunani zaiyi abu ɗaya dai yana jin wata nitsuwa ta musamman a jikinshi da zuciyarsa.
Anutse Hadimin ya sake biyo sa tare da cewa.
“Bismillah ka matso ga abinci”.
Kai ya girgiza duk da kuwa yunwa da yake ji amma yanayin da yake ciki bazai iya bari yaci abinci ba.
Ganin haka yasa ɗaya daga cikin hadiman ya nufi jikin Frigde kana ya kawo masa Fruits tare da ajiyewa akan stool agabansa.
Sanyayyar iska ya fesar daga bakinsa kasancewar sa mai son ƴaƴan itatuwa yasa ya miƙa hannu ya ɗauki apple ya ɗan fara ci ahankali...
Yayin da hadiman suka koma baya suka ci-gaba da tsayuwar anutse ya ɗago manyan idanunsa dake lumshe ya kallesu kana yace.
“Ku zauna mana”.
Murmushi sukayi tare da faɗin.
“A'a yallaɓai babu matsala kada ka damu wannan ai aikin mune”.
Da mamaki yake kallonsu kana yashiga tunanin wannan al'amarin ya yake.
Yana zaune yaga wani Hadimin ya turo ƙofa ya shigo yayin da wasu hadimai uku mata ke biye dashi hannunsu riƙe da manya-manyan Trolley suna shiga suka gaishesa cike da girmamawa kana suka nufi bedroom ɗin suka buɗe Weldrop suka shirya masa kayan kana suka fito Hadimai matan suka tafi suka bar namijin.
Shi kuwa namijin cike da ladabi ya durƙusa gabansa tare da faɗin.
“Mai martaba yace ayi maka sannu da zuwa, sannan yace afaɗa maka ka kwantar da hankalin ka ka shiga kayi wanka ga kaya an kawo maka ka huta zuwa anjima zai zo kugana”.
Tunda ya fara magana Moddibo ke kallonsa jin ya dasa aya yasa shi faɗin.
“Ina buƙatar wayoyina suna cikin mota akawo min ko kuma suzo muyi duk maganar da zamuyi zan tafi ina da abubuwan yi”.
Cike da girmamawa Hadimin ya furta.
“Kayi haƙuri In Sha Allah zan isar masa da saƙonka”.
Kana ya miƙe ya fita...
Acan cikin gida Side ɗin mai Martaba kuwa Didi ce ke tafiya cikin sasarfa yayin da hadimai biyu ke biye da ita hannu ta sanya ta buɗe ƙofar falon yayin dasu kuma suka tsaya daga gefe.
Cikin Sassarfa ta ƙarasa shiga cikin falon Idanunta suka sauƙa akan Mahaifinta Sheikh Jabeer, Mijinta Sarki Youssef Muhammad Mouley, Waziri, Jakadiyar Sarki, Galadima cikin sauri da girmamawa Jakadiyar Sarki ta miƙa mata hannu alamar tazo ta zauna
Kai ta gyaɗa kana ta zauna tare da kallon Mahaifinta wato Sheiykh Jabeer cikin sanyi da yanayin damuwa ta furta.
“Abiey meke faruwa? Me nakeji? Kufahimtar dani na kasa fahimtar abinda Dr Jameel da Hakim ke faɗa min shin gaskiya ne”.
Cikin sauri Jabeer bin Jabeer ya matsa kusa da ita tare da riƙe hannunta cikin ƙauna da shaƙuwa ta Yah da ƙani yace.
“Didi ina ji ajikina ɗankine kuma tsatsonkine, ina ji ajikina wannan mutumin dana gani ɗankine wallahi domin babu abinda ya raba shi da Ibraahim kamanninsa da Ibraahim da kuma Mahaifinsa har ya ƙazanta.
Didi dai-dai da faratunsa irin na ƴaƴan kine”...
Aƙage ta matse hannunsa dake cikin nata kana idanunta cike da ruwan hawaye tace.
“Toh waye shi? A ina yake? kununa min shi?, dan Allah kuyi gaggawan kaini garesa domin idanuwa sun ƙagu suyi tozali dashi haka zalika kunnuwana su ƙagu suji sautin Muryansa”.
Gyaran murya da Sheiykh Jabeer yayi yasa ta dawo cikin nutsuwarta cike da kamala da tarin nutsuwa ya furta.
“Fatima ki nutsu mana, ai komai yazo da sauƙi Bi'iznillahi ta'ala ɗan da muka rasa tsawon shekaru, in Sha Allahu yazo garemu nima kaina na gamsu wannan ɗankine tsatsonkine”.
Numfashi mai martaba ya fesar tare da muskutawa kana ya furta.
“Nima inaji ajika babu haufi babu shakka ko tsoro wannan ɗana ne jini nane Abeey yaron nan Aliyu nane babu haufi jikina da jinina da zuciyata sun shaida min”.
Sai kuma ya maida kallonsa kan Sheykh Jabeer kana yace.
“Tabbas wannan al'amari ya girmama sai dai kuma yanzu saboda idon Fada da kuma yadda al'amarin yaja hankalin mutane yana buƙatar sirri”.
Kai Jabeer bin Jabeer ya jinjina tare da sake tuno kamannin Moddibo da kuma Ibraahim Sarki Youseep Muhammad Mouleey kuwa numfashi ya fesar kana ya cigaba da faɗin.
“Ga kuma yanda ya shigo ya iya sarrafa *Rinƙas* yaja hankalin mutane gaba ɗaya sannan kuma muna buƙatar tabbatarwa da shi kan al'adun masarautar da sanar dashi dukkan abinda ya dace, dan haka sai zuwa tsakiyar dare yanda hankalin mutane duk ya kau zamu shiga wajensa dan bincike da tabbatar wa”.
Kai suka jinjina cike da gamsuwa da kalamansa sai kuma ya maida idanunsa kan Sheykh Jabeer tare da faɗin.
“Abeey Wallahi wannan yaron ɗanane babu ma wani batun tabbarwa inaji ajikina ɗanane tsatsonane ɗanane da muka rasa tsawon lokaci”.
Cikin fesar da numfashi Sheikh Jabeer yace.
“Ka kwantar hankalinka Youseep na sani amma akwai buƙatar bincike akwai buƙatar mu san wani abu”.
Kai ya jinjina kana yace.
“Toh shikenan”. Kasancewar Sheykh Jabeer abokin Mahaifinsa Muhammad Mouley ne yasa baya iya yi masa musu.
Galadima da tunda aka fara magana bai ce komai ba, sai yanzu ya fesar da numfashi kana yace.
“Tabbas nima inaji ajikina wannan tsatson mune saboda inba haka ba bai isa ya sarrafa *Rinƙas* ba sannan kamannin nan yayi yawa kana ku kalli yanda yake bin taswiran gidan nan tamkar yasan wuraren, wannan yasa nakeda tabbacin da wuya ace akwai wani abinda bai saniba na al'adunmu sai dai abin tambayar shin taya hakan yakasance”.
Kai suka jinjina cike da gamsuwa kana suka cigaba da tattauna maganar daga haka suka tashi daga taron.
Yayin da Didi kam daren wannan ranan haka ta suku-ku baki ɗaya zuciyarta da nutsuwarta ya tafi izuwa ga ɗouki da kuma mararin son ganin yaron da akece yana tsananin kama da Ibrahim ɗin ta koda kuwa abincine ta kasa ci.
Acan ɓangaren Moddibo kuwa yana zaune a inda yake batare daya motsa ba bare kuma yaci abinci baki ɗaya abin duniya ya ishesa abubuwa goma da ashirin sun haɗe masa, tarin tambayoyin a kansa sama da dozin wanda innayi kaɗai yakeson ji da ganin yayi mata su, ahaka ya cigaba da zama kafin daga bisani wata zuciyar ta yanke shawarar ya tashi koda zai iya samun wata ƙofa ta baya da zai fice.
Ahankali ya miƙe tare da kallon gefen daman sa inda ya shiga yayi alwala kana ya kalli falon daga gefe ya hango wata ƙofa ahankali ya fita idanunsa suka sauƙa akan wani falo na daban shima still yana ɗauke da ƙofa hagu da dama murɗa ƙofar yayi ya fita anan yaga wani ƙofa hagu da dama sai kuma wani step daga tsakiyarsu daga can sama shima kofa ce hagu da dama...
Hadimansa kuwa ganin ya fita yasa suka shiga taka masa baya tunda basu da ikon hanasa cikin tsuke fuska ya kallesu, su kuwa cike da girmamawa ɗayansu yace.
“Ranka ya daɗe ko akwai abinda kake buƙata?”.
Girgiza kai kana yace.
“Um-um babu abinda nake buƙata”.
Kai suka gyaɗa tare da faɗin.
“Toh”.
Tunda basu da ikon hanashi tafiya.
Cike da a nitsuwa yake tafiya har ya haura step ɗin yanda ƙasan yake haka zalika saman yake komai na ginin iri ɗaya ne sai dai tsarin Furnitures ɗin ne suka banbanta.
Kasancewar suna saman daga gefen dama komai White & Sky blue kalar Sararin samaniya sai kuma daga can gefen Hagu komai na cikinsa ya kasance Jane da ratsin fari haka nan yakeji kamar anayi ma shi jagorane.
“Ya Salam, shin Mutanen nan me suke nufi dani, suna nufin ba zanyi Sallah acikin jam'i ba?”.
Ahankali ya juya idanunsa akan wannan Corridor dake gefen damansa cikin nutsuwa yabi hanyar yayi tafiya mai ɗan tsayi ya hango wasu ƙofofi guda biyu gefen hagu da dama ahankali ya murɗa ƙofar dake gefen dama.
“Ya Salam”.
Ya furta asaman laɓɓansa ganin wani tsarerren falo ahankali ya taka ya shiga ciki.
Sai kuma ya ɗan jujjuya kai, ƙofar dake kusa dashi ya nufa.
Wanda bedroom ne a hankali ya murɗa ya shiga.
Ƙofar bathroom ya sake murɗa yashiga, alwala kana ya fitowa.
Jujjuya ya kai yayi cikin sa'a yaga darduma a shimfiɗe a wata ƴar kusurwa awajen alamar ana sallah awajen anutse yayi sallar Maghriba awajen kana ya cigaba da addu'oi har aka kira Isha'i, bayan ya idar ya fito falon farko da aka fara ajiyesa.
Yana isa Idanunsa suka sauƙa akan dining da aka jera abinci kala-kala sai kuma ya juya kanshi hanyar shigowa nan yaga wasu hadimai guda uku maza suna tsaye.
Ganinsa yasa sukayi saurin sunkuyar da kansu ƙasa kana suka ɗaura hannunsu aƙirji alamar Barka da fitowa.
Cike da girmamawa ɗaya daga cikin su yace.
“Ranka ya daɗe ga abinci”.
Numfashi ya fesar kana ya tsira musu ido na second biyu tare da cewa.
“Shin meyesa aka tsareni anan?”.
Cike da ladabi da kuma Mutuntawa suke sake sunkuyar da kansu ɗaya daga cikinsu yace.
“Kayi haƙuri Ranka ya daɗe Umarni ne daga mai martaba yace kada mu bari a buɗe maka ƙofa dukkan abinda kake buƙata akwai shi anan basai ka fita ba”.
Cike da mmki ya kallesa kana ya lumshe idanunsa tare da fesar da iska mai zafi yace.
“Akan me za'a rufeni a hanani fita bayan ina da abubuwanyi”.
Cike da ladabi Hadimin ya sake sunkuyar da kansa wanda da alama shine babban su kana yace.
“Kayi haƙuri In Sha Allah Mai martaba yana nan zai zo wajenka”.
Batare daya sake furta komai ba ya koma ya zauna akan kujeran.
Allah ya sani shi yama rasa shin wani irin tunani zaiyi abu ɗaya dai yana jin wata nitsuwa ta musamman a jikinshi da zuciyarsa.
Anutse Hadimin ya sake biyo sa tare da cewa.
“Bismillah ka matso ga abinci”.
Kai ya girgiza duk da kuwa yunwa da yake ji amma yanayin da yake ciki bazai iya bari yaci abinci ba.
Ganin haka yasa ɗaya daga cikin hadiman ya nufi jikin Frigde kana ya kawo masa Fruits tare da ajiyewa akan stool agabansa.
Sanyayyar iska ya fesar daga bakinsa kasancewar sa mai son ƴaƴan itatuwa yasa ya miƙa hannu ya ɗauki apple ya ɗan fara ci ahankali...
Yayin da hadiman suka koma baya suka ci-gaba da tsayuwar anutse ya ɗago manyan idanunsa dake lumshe ya kallesu kana yace.
“Ku zauna mana”.
Murmushi sukayi tare da faɗin.
“A'a yallaɓai babu matsala kada ka damu wannan ai aikin mune”.
Da mamaki yake kallonsu kana yashiga tunanin wannan al'amarin ya yake.
Yana zaune yaga wani Hadimin ya turo ƙofa ya shigo yayin da wasu hadimai uku mata ke biye dashi hannunsu riƙe da manya-manyan Trolley suna shiga suka gaishesa cike da girmamawa kana suka nufi bedroom ɗin suka buɗe Weldrop suka shirya masa kayan kana suka fito Hadimai matan suka tafi suka bar namijin.
Shi kuwa namijin cike da ladabi ya durƙusa gabansa tare da faɗin.
“Mai martaba yace ayi maka sannu da zuwa, sannan yace afaɗa maka ka kwantar da hankalin ka ka shiga kayi wanka ga kaya an kawo maka ka huta zuwa anjima zai zo kugana”.
Tunda ya fara magana Moddibo ke kallonsa jin ya dasa aya yasa shi faɗin.
“Ina buƙatar wayoyina suna cikin mota akawo min ko kuma suzo muyi duk maganar da zamuyi zan tafi ina da abubuwan yi”.
Cike da girmamawa Hadimin ya furta.
“Kayi haƙuri In Sha Allah zan isar masa da saƙonka”.
Kana ya miƙe ya fita...
Acan cikin gida Side ɗin mai Martaba kuwa Didi ce ke tafiya cikin sasarfa yayin da hadimai biyu ke biye da ita hannu ta sanya ta buɗe ƙofar falon yayin dasu kuma suka tsaya daga gefe.
Cikin Sassarfa ta ƙarasa shiga cikin falon Idanunta suka sauƙa akan Mahaifinta Sheikh Jabeer, Mijinta Sarki Youssef Muhammad Mouley, Waziri, Jakadiyar Sarki, Galadima cikin sauri da girmamawa Jakadiyar Sarki ta miƙa mata hannu alamar tazo ta zauna
Kai ta gyaɗa kana ta zauna tare da kallon Mahaifinta wato Sheiykh Jabeer cikin sanyi da yanayin damuwa ta furta.
“Abiey meke faruwa? Me nakeji? Kufahimtar dani na kasa fahimtar abinda Dr Jameel da Hakim ke faɗa min shin gaskiya ne”.
Cikin sauri Jabeer bin Jabeer ya matsa kusa da ita tare da riƙe hannunta cikin ƙauna da shaƙuwa ta Yah da ƙani yace.
“Didi ina ji ajikina ɗankine kuma tsatsonkine, ina ji ajikina wannan mutumin dana gani ɗankine wallahi domin babu abinda ya raba shi da Ibraahim kamanninsa da Ibraahim da kuma Mahaifinsa har ya ƙazanta.
Didi dai-dai da faratunsa irin na ƴaƴan kine”...
Aƙage ta matse hannunsa dake cikin nata kana idanunta cike da ruwan hawaye tace.
“Toh waye shi? A ina yake? kununa min shi?, dan Allah kuyi gaggawan kaini garesa domin idanuwa sun ƙagu suyi tozali dashi haka zalika kunnuwana su ƙagu suji sautin Muryansa”.
Gyaran murya da Sheiykh Jabeer yayi yasa ta dawo cikin nutsuwarta cike da kamala da tarin nutsuwa ya furta.
“Fatima ki nutsu mana, ai komai yazo da sauƙi Bi'iznillahi ta'ala ɗan da muka rasa tsawon shekaru, in Sha Allahu yazo garemu nima kaina na gamsu wannan ɗankine tsatsonkine”.
Numfashi mai martaba ya fesar tare da muskutawa kana ya furta.
“Nima inaji ajika babu haufi babu shakka ko tsoro wannan ɗana ne jini nane Abeey yaron nan Aliyu nane babu haufi jikina da jinina da zuciyata sun shaida min”.
Sai kuma ya maida kallonsa kan Sheykh Jabeer kana yace.
“Tabbas wannan al'amari ya girmama sai dai kuma yanzu saboda idon Fada da kuma yadda al'amarin yaja hankalin mutane yana buƙatar sirri”.
Kai Jabeer bin Jabeer ya jinjina tare da sake tuno kamannin Moddibo da kuma Ibraahim Sarki Youseep Muhammad Mouleey kuwa numfashi ya fesar kana ya cigaba da faɗin.
“Ga kuma yanda ya shigo ya iya sarrafa *Rinƙas* yaja hankalin mutane gaba ɗaya sannan kuma muna buƙatar tabbatarwa da shi kan al'adun masarautar da sanar dashi dukkan abinda ya dace, dan haka sai zuwa tsakiyar dare yanda hankalin mutane duk ya kau zamu shiga wajensa dan bincike da tabbatar wa”.
Kai suka jinjina cike da gamsuwa da kalamansa sai kuma ya maida idanunsa kan Sheykh Jabeer tare da faɗin.
“Abeey Wallahi wannan yaron ɗanane babu ma wani batun tabbarwa inaji ajikina ɗanane tsatsonane ɗanane da muka rasa tsawon lokaci”.
Cikin fesar da numfashi Sheikh Jabeer yace.
“Ka kwantar hankalinka Youseep na sani amma akwai buƙatar bincike akwai buƙatar mu san wani abu”.
Kai ya jinjina kana yace.
“Toh shikenan”. Kasancewar Sheykh Jabeer abokin Mahaifinsa Muhammad Mouley ne yasa baya iya yi masa musu.
Galadima da tunda aka fara magana bai ce komai ba, sai yanzu ya fesar da numfashi kana yace.
“Tabbas nima inaji ajikina wannan tsatson mune saboda inba haka ba bai isa ya sarrafa *Rinƙas* ba sannan kamannin nan yayi yawa kana ku kalli yanda yake bin taswiran gidan nan tamkar yasan wuraren, wannan yasa nakeda tabbacin da wuya ace akwai wani abinda bai saniba na al'adunmu sai dai abin tambayar shin taya hakan yakasance”.
Kai suka jinjina cike da gamsuwa kana suka cigaba da tattauna maganar daga haka suka tashi daga taron.
Yayin da Didi kam daren wannan ranan haka ta suku-ku baki ɗaya zuciyarta da nutsuwarta ya tafi izuwa ga ɗouki da kuma mararin son ganin yaron da akece yana tsananin kama da Ibrahim ɗin ta koda kuwa abincine ta kasa ci.
Acan ɓangaren Moddibo kuwa yana zaune a inda yake batare daya motsa ba bare kuma yaci abinci baki ɗaya abin duniya ya ishesa abubuwa goma da ashirin sun haɗe masa, tarin tambayoyin a kansa sama da dozin wanda innayi kaɗai yakeson ji da ganin yayi mata su, ahaka ya cigaba da zama kafin daga bisani wata zuciyar ta yanke shawarar ya tashi koda zai iya samun wata ƙofa ta baya da zai fice.
Ahankali ya miƙe tare da kallon gefen daman sa inda ya shiga yayi alwala kana ya kalli falon daga gefe ya hango wata ƙofa ahankali ya fita idanunsa suka sauƙa akan wani falo na daban shima still yana ɗauke da ƙofa hagu da dama murɗa ƙofar yayi ya fita anan yaga wani ƙofa hagu da dama sai kuma wani step daga tsakiyarsu daga can sama shima kofa ce hagu da dama...
Hadimansa kuwa ganin ya fita yasa suka shiga taka masa baya tunda basu da ikon hanasa cikin tsuke fuska ya kallesu, su kuwa cike da girmamawa ɗayansu yace.
“Ranka ya daɗe ko akwai abinda kake buƙata?”.
Girgiza kai kana yace.
“Um-um babu abinda nake buƙata”.
Kai suka gyaɗa tare da faɗin.
“Toh”.
Tunda basu da ikon hanashi tafiya.
Cike da a nitsuwa yake tafiya har ya haura step ɗin yanda ƙasan yake haka zalika saman yake komai na ginin iri ɗaya ne sai dai tsarin Furnitures ɗin ne suka banbanta.
Kasancewar suna saman daga gefen dama komai White & Sky blue kalar Sararin samaniya sai kuma daga can gefen Hagu komai na cikinsa ya kasance Jane da ratsin fari haka nan yakeji kamar anayi ma shi jagorane.