Sashe 25
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washe gari da safe Misalin ƙarfe 8:00 Anutse Moddibo ya fito daga falonsa cikin wani ɗanyen Boyel Sky blue Fuskarsa tayi fayau manyan Idanunsa dake lumshe sun sake girma sabida ramar da yayi, sajensa ya sake yawaita yayi fadi da cika, yana kuma ɗan hargitse alamun an kwana biyu ba'a gyarashi.
Kafadarsa na dama rataye da jakar laptop ɗinsa daga zip ɗin gefen wayoyinsa ya zira, sai hannunsa dake riƙe da jakar kayansa, a hankali yake tafiya, yayinda jikinsa ke fitar da sanyayyan ƙamshin tularen sa.
Kai tsaye sashen Innayi ya nufa ahankali Innayi dake breakfast ta ɗago Kai ta kallesa Anutse ya ƙarasa tare da zama gefenta.
Da mamaki take Kallonsa ganin kamar alamar cikin shirin tafiya yake.
Cikin sauri tace.
“Aliyu”.
Kallonta yayi da sauri domin bata fiye kiransa da Aliyu ba sai da babban dalili.
Cikin sanyin murya yace.
“Na'am Innayi”.
Hannunta riƙe da kofin tea tace.
“Ya haka? ya na ganka kamar mai yin tafiya?”.
Kai ya gyaɗa mata tare da tanƙwashe ƙafafunsa kana ya fuskanceta cikin ƙoƙarin danne damuwarsa kana yana mai jin farin cikin zai bar garin Gembila haka nan ya tsinci kansa da jin farin cikin yau dai zai bar Jahar Taraba domin baki ɗaya garin ya fice masa arai cikin sanyin murya yace.
“Innayi ba kama bace tafiyar ce”.
Cike da mamaki ta ɗago kanta kana tace.
“Aliyu tafiya zaka yi amma ban sani ba sai dai in ganka kana fita da jaka haka?”.
Ahankali ya riƙo tafin hannunta acikin nasa cike da mmkia yace.
“Kiyi haƙuri Innayi tafiyar ce nima tazo min a bazata kuma ba jiya Abban Jameel ya gaya mikiba”.
Kai ta girgirza tare da cewa.
“A'a bai gaya minba zakayi tafiya ba, ya dai cemin yana neman al'farma ni kuwa nace umurni kawai zai baka kamar yadda yake bawa Jameel ni na amince duniya da ƙiyama, ban bari yamin bayaniba sabida kar yaga kamar zan hanaƙa yaji ba daɗi. To waima Tafiya zuwa ina zakaje?”.
Cikin kwantar da murya yace.
“Tafiya zuwa Marocco!”.
Cikin tsananin kaɗuwa ta zaro idanunta baki ɗaya lokacin ɗaya ta ƙware tare da fara tari sakamakon ƙwarewa da tayi da dankalin dake bakinta”
Moddibo kuwa ganin yanda ta ƙware yasa yayi saurin daukan kofin ruwa ya miƙa mata tare da cewa.
“Sannu”.
Amsa tayi tasha amma still tarin bai tsaya ba lokaci ɗaya Idanunta yayi ja zufa ya shiga tsats-tsafo mata agaba ɗaya ilahirin jikinta shi kuwa Modibbo ido ya zuba mata tare da jera mata sannu da kuma ɗan bubbuga bayanta kaɗan-kaɗan yana mmkin wasu al'amuran a ranta domin ya sani tsawon zamansu da J ta hanashi zuwa Marocco wanda bai san me dalilntaba, kasancewar sa ba mutum ne mai yawan bincikeba yasa bai taɓa mata musuba ko bincike.
Ahankali ya ke mata sannu cike da tausayawa takai kimanin minti biyar kafin tarin ya lafa sannu Ahankali ta fara maida numfashi.
Tana sauƙe ajiyar zuciya ta juya ta kallesa kana tace.
“Marocco!!!! kuma Aliyu?”.
Jinjina kai yayi cikin sanyin murya yace.
“Eh Innayi Marocco zanje amma idan har kin amince, idan bakya so, bazanje ba sai in bawa Abba haƙuri”.
Ahankali ta gyara zama tare da fuskantar sa da kyau kana tace.
“Toh amma mai zakaje kayi a can?”.
Tayi tambayar zuciyarta na mai cigaba da bugawa da ƙarfi.
Lumshe Idanunsa yayi tare da sauƙe Ajiyar zuciya kana yace.
“Abba ne ya nemi al'farma da Inje in kula da Company'nsa sannan kuma jiya daya zo nayi tunanin kunyi cikekkiyar maganar ne dashi kafin ku shiga wurina, shiyasa ni ban faɗa miki ba, ya nemi taimako da Inje in taimaka masa akan batun Company sa buga Abaya, jallabiya, Carpet, Sallayu blanket's da dai sauransu”.
Kallonsa kawai Innayi keyi yayin da take ji tamkar zuciyarta zai fito saboda yanda yake bugawa.
Cikin sanyi Moddibo ya riƙe Hannunta dake cikin nasa yace.
“Akwai sabbin injinan aiki da za'a sauƙe na Company, sannan kuma za'a fara aikin dasa Injina za'a kakkafa toh akwai ɓuƙatar sa ido da kuma kula da abubuwan, amma Insha Allah bazan wuce wata biyu zuwa uku ba zan zo Innayi”.
Girgiza kai tayi tare da jingina bayanta da jikin bango ta lumshe Idanunta kana ta shiga maida numfashi.
Moddibo kuwa ido ya zuba mata kana Asanyaye yace.
“Amma Innayi idan har bakyason Inje zan kira Abba in Faɗa masa yayi haƙuri”.
Uffan bata ceba kana bata buɗe Idanunta ba daga ita sai Ubangiji kaɗai suka san mai take tunawa aranta takai kimanin minti biyar ahaka kafin ta ɗago Idanunta ta kallesa kana taja dogon numfashi ta sauƙe tare da sakin Murmushin mai tarin ma'anoni sannan tace.
“Bazan hanaka tafiya ba Aliyu, domin ko baka tafi yanzu ba, dama lokacin tafiyar ya ƙarato. na amince kayi masa duk kan abinda Jameelu zai masa daya kasance araye, domin hakan zai rage masa raɗaɗin ciwon rashin Jameelu”.
Kai Modibbo ya gyaɗa yana kallon yanayin fuskartar ahankali yace.
“Toh shikenan Insha Allah zanyi hakan”.
Innayi kuwa kallonsa tayi kana cikin sanyin murya tace.
“Amma yanzu-yanzu tafiyar kenan Aliyu?”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Eh Innayi zanbi jirgi zuwa Abuja ne, in naga komai biza na ya fito zan wuce”.
Jinjina kai tayi tare da cewa.
“Shikenan Ubangiji Allah ya sanya alkhairi Allah ya tabbatar da alkhairi sai nazo”.
Saurin Kallonta yayi cike da Mamaki yace.
“Sai kinzo kuma?”.
Sunkuyar da kanta ƙasa tayi tare da Girgiza masa kai kana tace.
“Mantawa nayi sai ka dawo nake son cewa".
A hankali ya zaro ATM ɗinshi na Zenith Bank daga al'jihunsa, cikin tafin Hannun ta yasa matashi kana a hankali yace.
“Ga ATM ɗina na Zenith Bank, kin san pin number ɗin, akwai kuɗi a ciki kusan 5 Million”.
Da sauri tace.
“Ina ka samosu?”.
Gyara zamanshi yayi kana yayi mata bayanin yadda sukayi da Abba sannan ya ɗaura da cewa.
“Akwai wasu a wurina, wannan ki riƙe kiyi dukkan abinda kike buƙata kafin in dawo, in haɗasu muyi ƙoƙarin barin garin nan, domin ya fita raina”.
Yayi mgnar yana tuno kalaman Hajja Nana ita kuwa Innayi cike da sanyi tace.
“Uhmmm Aliyu in Sha Allah kamar ma mun barima ai kama barin kai kam”.
Cikin sanyi ya jinjina
Kai tare da miƙewa yace.
“Toh shikenan Innayi amma dai bakiyi fushi dani bako?”.
Da sauri tace.
“La la la Aliyu banyi fushi da kaiba”.
hannunta ya riƙo tare da ɗaurawa a kanshi kana yace.
“Toh kuma baki samin Albarka ba”.
Cikin sanyin Murya tace.
“Allah yasan ya Albarka Ubangiji ya tsare gabanka da bayanka Allah maidakai lafiya ya kuma tsareka da lafiyarka, Ubangiji ya rabaka da sharrin duk kan abin ƙi walau mutum ko aljan ko wani irin abune ya *Tsareka da Tsoffin magauta ya hanasu ganeka bare cutar da kai kafin isarka tushenka”.*
Lumshe Idanunsa yayi kana yace.
“Ameen ya Allah Innayi ni zan tafi”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Toh ka tsaya bari na zo".
Kai ya gyaɗa sannan ya tsaya ɗaki tashiga ba daɗewa ta fito sanye da hijabi, suka nufi wurin motarsa,
“Yau innayi zafa ki koma gidan Abba ko Ummi dan zamani ke ɗaya a nan bai minba”.
Cikin sauri tace.
“Eh toh gsky k nima ina tsoro Ni kaɗai a nan to amman, gsky gwara min gidan Ummin Jameel kaga ita kamar ɗiya take a gareni gidan Abba kuwa ba wani sabawa nayi da matansa ba, amman can zamu zauna ɗakin Asma'u nasam Malam Ahmad kuma baida matsala”.
Cikin gamsuwa da haka yace.
“Gsky kam hakan yafi, zan gaya Abban in kin gama haɗa kayanki Asma'u zata zo ku tafi”.
Kai ta jinjina cikin gamsuwa tace.
“Ba laifi”.
Jingina yayi da jikin motar bayan yasa jakarsa gefen mai zaman banza.
Ita kuwa Innayi a hankali ta matso kusa da marfin motar zira hannunta tayi ta ciki, zip ɗin jakarsa tabuɗe tasa jim kaɗan kuma ta maida ta rufe kana sukayi sallama ya mota ya tafi.
Kai tsaye gidan Ummi Moddibo ya nufa cikin nutsuwa yake Driving yayin da yake sauraran ƙira'ar Ahmad Sulaiman cikin suratul An'am yana isa gidan Ummi yayi Parking aƙofar kana ya fita ya shiga coumpund ɗin yana tafiya ahankali yana ɗaura ƙafarsa akan farandar sautin muryar Khausar ya ratsa Dodon Kukensa cikin sauri ya tsaya tare da rumtse idanunsa.
Sabida jin yadda tsikar jikinsa ya fara tashi tun daga tafin ƙafarsa har tsakiyar ƙwaƙwalwan kansa, ahankali ya jingina bayan sa da jikin bango yayin da zuciyarsa ta shiga bugawa da kaso Cassa'in da tara cikin ɗari.
Aransa yakeji kamar ya koma domin gaba ɗaya ya rasa meke sashi shiga wani yanayi da zaran yaji sautin Muryanta zaiji tamkar ana tsikara masa allura yama rasa ta wani irin yanayi zai misalta yanda yake ji akan yarinyar shin kunyarta yake ko kuma tsoronta yakeji, ko shakkarta shi kansa ya kasa tantancewa, taune Lip ɗinsa na ƙasa yayi da ƙarfi tare da buɗe idanunsa da suka sauya launi kana ya tura ƙofar falon tare da sallama yana mai tsare fuska.
Ummi dake zaune ta tsira masa ido tare da cewa.
“Babana har ka shirya kenan?
Kai ya gyaɗa tare da faɗin.
“Eh Ummi”.
Kana ya zauna agefenta ya zamana yana facing ɗin kichen.
Kallonsa Ummi tayi cike da kulawa tace.
“Amma dai ba kayi breakfast”.
Kai ya girgiza kana yace.
“Uhm-Uhm”.
Da Mamaki tace.
“Toh ya za'a ayi ka tafi da yunwa ba zaiyu ba Babana ba zaka tafi da yunwa ba”.
Langwaɓar da kai yayi tare da Marerece murya yace.
“Ummi bana jin yunwa fa”.
Fuska ta ɓata kana tace.
“Bafa zaiyu ba Babana baza ka tafi da yunwa ba”.
Kafadarsa na dama rataye da jakar laptop ɗinsa daga zip ɗin gefen wayoyinsa ya zira, sai hannunsa dake riƙe da jakar kayansa, a hankali yake tafiya, yayinda jikinsa ke fitar da sanyayyan ƙamshin tularen sa.
Kai tsaye sashen Innayi ya nufa ahankali Innayi dake breakfast ta ɗago Kai ta kallesa Anutse ya ƙarasa tare da zama gefenta.
Da mamaki take Kallonsa ganin kamar alamar cikin shirin tafiya yake.
Cikin sauri tace.
“Aliyu”.
Kallonta yayi da sauri domin bata fiye kiransa da Aliyu ba sai da babban dalili.
Cikin sanyin murya yace.
“Na'am Innayi”.
Hannunta riƙe da kofin tea tace.
“Ya haka? ya na ganka kamar mai yin tafiya?”.
Kai ya gyaɗa mata tare da tanƙwashe ƙafafunsa kana ya fuskanceta cikin ƙoƙarin danne damuwarsa kana yana mai jin farin cikin zai bar garin Gembila haka nan ya tsinci kansa da jin farin cikin yau dai zai bar Jahar Taraba domin baki ɗaya garin ya fice masa arai cikin sanyin murya yace.
“Innayi ba kama bace tafiyar ce”.
Cike da mamaki ta ɗago kanta kana tace.
“Aliyu tafiya zaka yi amma ban sani ba sai dai in ganka kana fita da jaka haka?”.
Ahankali ya riƙo tafin hannunta acikin nasa cike da mmkia yace.
“Kiyi haƙuri Innayi tafiyar ce nima tazo min a bazata kuma ba jiya Abban Jameel ya gaya mikiba”.
Kai ta girgirza tare da cewa.
“A'a bai gaya minba zakayi tafiya ba, ya dai cemin yana neman al'farma ni kuwa nace umurni kawai zai baka kamar yadda yake bawa Jameel ni na amince duniya da ƙiyama, ban bari yamin bayaniba sabida kar yaga kamar zan hanaƙa yaji ba daɗi. To waima Tafiya zuwa ina zakaje?”.
Cikin kwantar da murya yace.
“Tafiya zuwa Marocco!”.
Cikin tsananin kaɗuwa ta zaro idanunta baki ɗaya lokacin ɗaya ta ƙware tare da fara tari sakamakon ƙwarewa da tayi da dankalin dake bakinta”
Moddibo kuwa ganin yanda ta ƙware yasa yayi saurin daukan kofin ruwa ya miƙa mata tare da cewa.
“Sannu”.
Amsa tayi tasha amma still tarin bai tsaya ba lokaci ɗaya Idanunta yayi ja zufa ya shiga tsats-tsafo mata agaba ɗaya ilahirin jikinta shi kuwa Modibbo ido ya zuba mata tare da jera mata sannu da kuma ɗan bubbuga bayanta kaɗan-kaɗan yana mmkin wasu al'amuran a ranta domin ya sani tsawon zamansu da J ta hanashi zuwa Marocco wanda bai san me dalilntaba, kasancewar sa ba mutum ne mai yawan bincikeba yasa bai taɓa mata musuba ko bincike.
Ahankali ya ke mata sannu cike da tausayawa takai kimanin minti biyar kafin tarin ya lafa sannu Ahankali ta fara maida numfashi.
Tana sauƙe ajiyar zuciya ta juya ta kallesa kana tace.
“Marocco!!!! kuma Aliyu?”.
Jinjina kai yayi cikin sanyin murya yace.
“Eh Innayi Marocco zanje amma idan har kin amince, idan bakya so, bazanje ba sai in bawa Abba haƙuri”.
Ahankali ta gyara zama tare da fuskantar sa da kyau kana tace.
“Toh amma mai zakaje kayi a can?”.
Tayi tambayar zuciyarta na mai cigaba da bugawa da ƙarfi.
Lumshe Idanunsa yayi tare da sauƙe Ajiyar zuciya kana yace.
“Abba ne ya nemi al'farma da Inje in kula da Company'nsa sannan kuma jiya daya zo nayi tunanin kunyi cikekkiyar maganar ne dashi kafin ku shiga wurina, shiyasa ni ban faɗa miki ba, ya nemi taimako da Inje in taimaka masa akan batun Company sa buga Abaya, jallabiya, Carpet, Sallayu blanket's da dai sauransu”.
Kallonsa kawai Innayi keyi yayin da take ji tamkar zuciyarta zai fito saboda yanda yake bugawa.
Cikin sanyi Moddibo ya riƙe Hannunta dake cikin nasa yace.
“Akwai sabbin injinan aiki da za'a sauƙe na Company, sannan kuma za'a fara aikin dasa Injina za'a kakkafa toh akwai ɓuƙatar sa ido da kuma kula da abubuwan, amma Insha Allah bazan wuce wata biyu zuwa uku ba zan zo Innayi”.
Girgiza kai tayi tare da jingina bayanta da jikin bango ta lumshe Idanunta kana ta shiga maida numfashi.
Moddibo kuwa ido ya zuba mata kana Asanyaye yace.
“Amma Innayi idan har bakyason Inje zan kira Abba in Faɗa masa yayi haƙuri”.
Uffan bata ceba kana bata buɗe Idanunta ba daga ita sai Ubangiji kaɗai suka san mai take tunawa aranta takai kimanin minti biyar ahaka kafin ta ɗago Idanunta ta kallesa kana taja dogon numfashi ta sauƙe tare da sakin Murmushin mai tarin ma'anoni sannan tace.
“Bazan hanaka tafiya ba Aliyu, domin ko baka tafi yanzu ba, dama lokacin tafiyar ya ƙarato. na amince kayi masa duk kan abinda Jameelu zai masa daya kasance araye, domin hakan zai rage masa raɗaɗin ciwon rashin Jameelu”.
Kai Modibbo ya gyaɗa yana kallon yanayin fuskartar ahankali yace.
“Toh shikenan Insha Allah zanyi hakan”.
Innayi kuwa kallonsa tayi kana cikin sanyin murya tace.
“Amma yanzu-yanzu tafiyar kenan Aliyu?”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Eh Innayi zanbi jirgi zuwa Abuja ne, in naga komai biza na ya fito zan wuce”.
Jinjina kai tayi tare da cewa.
“Shikenan Ubangiji Allah ya sanya alkhairi Allah ya tabbatar da alkhairi sai nazo”.
Saurin Kallonta yayi cike da Mamaki yace.
“Sai kinzo kuma?”.
Sunkuyar da kanta ƙasa tayi tare da Girgiza masa kai kana tace.
“Mantawa nayi sai ka dawo nake son cewa".
A hankali ya zaro ATM ɗinshi na Zenith Bank daga al'jihunsa, cikin tafin Hannun ta yasa matashi kana a hankali yace.
“Ga ATM ɗina na Zenith Bank, kin san pin number ɗin, akwai kuɗi a ciki kusan 5 Million”.
Da sauri tace.
“Ina ka samosu?”.
Gyara zamanshi yayi kana yayi mata bayanin yadda sukayi da Abba sannan ya ɗaura da cewa.
“Akwai wasu a wurina, wannan ki riƙe kiyi dukkan abinda kike buƙata kafin in dawo, in haɗasu muyi ƙoƙarin barin garin nan, domin ya fita raina”.
Yayi mgnar yana tuno kalaman Hajja Nana ita kuwa Innayi cike da sanyi tace.
“Uhmmm Aliyu in Sha Allah kamar ma mun barima ai kama barin kai kam”.
Cikin sanyi ya jinjina
Kai tare da miƙewa yace.
“Toh shikenan Innayi amma dai bakiyi fushi dani bako?”.
Da sauri tace.
“La la la Aliyu banyi fushi da kaiba”.
hannunta ya riƙo tare da ɗaurawa a kanshi kana yace.
“Toh kuma baki samin Albarka ba”.
Cikin sanyin Murya tace.
“Allah yasan ya Albarka Ubangiji ya tsare gabanka da bayanka Allah maidakai lafiya ya kuma tsareka da lafiyarka, Ubangiji ya rabaka da sharrin duk kan abin ƙi walau mutum ko aljan ko wani irin abune ya *Tsareka da Tsoffin magauta ya hanasu ganeka bare cutar da kai kafin isarka tushenka”.*
Lumshe Idanunsa yayi kana yace.
“Ameen ya Allah Innayi ni zan tafi”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Toh ka tsaya bari na zo".
Kai ya gyaɗa sannan ya tsaya ɗaki tashiga ba daɗewa ta fito sanye da hijabi, suka nufi wurin motarsa,
“Yau innayi zafa ki koma gidan Abba ko Ummi dan zamani ke ɗaya a nan bai minba”.
Cikin sauri tace.
“Eh toh gsky k nima ina tsoro Ni kaɗai a nan to amman, gsky gwara min gidan Ummin Jameel kaga ita kamar ɗiya take a gareni gidan Abba kuwa ba wani sabawa nayi da matansa ba, amman can zamu zauna ɗakin Asma'u nasam Malam Ahmad kuma baida matsala”.
Cikin gamsuwa da haka yace.
“Gsky kam hakan yafi, zan gaya Abban in kin gama haɗa kayanki Asma'u zata zo ku tafi”.
Kai ta jinjina cikin gamsuwa tace.
“Ba laifi”.
Jingina yayi da jikin motar bayan yasa jakarsa gefen mai zaman banza.
Ita kuwa Innayi a hankali ta matso kusa da marfin motar zira hannunta tayi ta ciki, zip ɗin jakarsa tabuɗe tasa jim kaɗan kuma ta maida ta rufe kana sukayi sallama ya mota ya tafi.
Kai tsaye gidan Ummi Moddibo ya nufa cikin nutsuwa yake Driving yayin da yake sauraran ƙira'ar Ahmad Sulaiman cikin suratul An'am yana isa gidan Ummi yayi Parking aƙofar kana ya fita ya shiga coumpund ɗin yana tafiya ahankali yana ɗaura ƙafarsa akan farandar sautin muryar Khausar ya ratsa Dodon Kukensa cikin sauri ya tsaya tare da rumtse idanunsa.
Sabida jin yadda tsikar jikinsa ya fara tashi tun daga tafin ƙafarsa har tsakiyar ƙwaƙwalwan kansa, ahankali ya jingina bayan sa da jikin bango yayin da zuciyarsa ta shiga bugawa da kaso Cassa'in da tara cikin ɗari.
Aransa yakeji kamar ya koma domin gaba ɗaya ya rasa meke sashi shiga wani yanayi da zaran yaji sautin Muryanta zaiji tamkar ana tsikara masa allura yama rasa ta wani irin yanayi zai misalta yanda yake ji akan yarinyar shin kunyarta yake ko kuma tsoronta yakeji, ko shakkarta shi kansa ya kasa tantancewa, taune Lip ɗinsa na ƙasa yayi da ƙarfi tare da buɗe idanunsa da suka sauya launi kana ya tura ƙofar falon tare da sallama yana mai tsare fuska.
Ummi dake zaune ta tsira masa ido tare da cewa.
“Babana har ka shirya kenan?
Kai ya gyaɗa tare da faɗin.
“Eh Ummi”.
Kana ya zauna agefenta ya zamana yana facing ɗin kichen.
Kallonsa Ummi tayi cike da kulawa tace.
“Amma dai ba kayi breakfast”.
Kai ya girgiza kana yace.
“Uhm-Uhm”.
Da Mamaki tace.
“Toh ya za'a ayi ka tafi da yunwa ba zaiyu ba Babana ba zaka tafi da yunwa ba”.
Langwaɓar da kai yayi tare da Marerece murya yace.
“Ummi bana jin yunwa fa”.
Fuska ta ɓata kana tace.
“Bafa zaiyu ba Babana baza ka tafi da yunwa ba”.