Sashe 62
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abualeey kuwa hannunsa na dama dake ɗauke da Zoben azurfa ya ɗaura akan Moddibo tare da faɗin.
“Allah ya maka albarka Ubangji Allah ya albarkanci rayuwarka. Allah ya baka zaman lafiya da matarka!”.
Haka nan Moddibo yake jin wani irin farin ciki ji yake yau kamar ranan Sallah ne, sabida wani irin nishaɗi da yakeji tamkar wanda aka yiwa bushara da Aljanna asaman lips ɗin sa yake amswa da.
“Ameen Ameen”.
Haka nan yake jin farin cikin addu'ar da Mahaifiyar sa da Mahaifinsa keyi masa...
Liƙi suka cigaba dayi musu suna zuba musu kuɗi kamar ba'asan darajar su ba...
Sarkin zaki kuwa hannunsa riƙe da Microphone yace.
“Hattara dai manyan bisa kanku wan'nan sune manyan ƙasar Morocco baki ɗayanta. Jiga-jigan manyan cikin birnin Rarat baki ɗaya manyane bisa kanku ku amsa da Ameen dan addu'a ce ta manyan Ameen.
Baki ɗaya mutanen falon suka amsa da.
“Ameen”.
Saboda sun san cewa addu'a da fatan Al'khairi iyayensa ke masa bayan sun gama suka juya suka tafi...
Aunty Ruƙayya da farin ciki ya gama cikata ganin yanda Moddibo da Khausar sukayi bala'in da cewa ga kuma yanda Moddibo ke raɗawa Khausar magana akunne wanda duk mai kallonsu a matsayin zantukan masoyane sukeyi yasa ta kalli Hajiya Bunayya wacce itace akusa da ita kana tace.
“Dan Allah Hajiya kalli Khausar da Moddibo tamkar dan junansu aka halicce su, haƙiƙa sun dace da juna Allah yayi Khausar zaɓi da mafi Al'khairi Ubangiji ya kawar da idanun maƙiya akansu”.
Yaƙe Hajiya Bunayya tayi Amaimakon tace Ameen sai ta sunkuyar da kanta tayi tare da cewa.
“Aikam”.
Wani irin zafi da ƙuna zuciyarta keyi ba zato taji hawayen hassada da ƙyashi na zuba daga idanunta ina ma ace Aminanta ce ke cikin wannan Daular duniya..
Daga can cikin falon kuwa Wasu zugan Maza da Mata manya ne suka nufi wajensu Moddibo da Khausar.
Sarkin Zaƙi na ganinsu ya ɗaga sautin muryarsa tare da cewa.
“Hattara dai Ango da Amarya ga Baffanayenku nan da Goggoninku”.
Ahankali Moddibo ya ɗaga kai yana kallonsu cikin wani irin yanayi mara misaltuwa wai yau shine acikin ahalinsa ana gabatar mishi dasu sahu-sahu.
Su kuwa cike da tarin ƙaunarsa suka riƙa yi musu liƙi da kuɗaɗe masu tarin yawa.
Aunty Hawwa ce ta kalli Aunty Hajara wacce suke daga ɗaya gefen Hajiya Bunayya kana Aunty Hauwa tace.
“Masha Allah Kinga yanda ake zubar da kuɗi tamkar ba'a cikin tsadar rayuwa”.
Dariya Aunty Hajara ta sanya tare da cewa.
“Aikam acikin wannan ahalin. Basuma san wani abu mai suna talauci ba komai nasu cikin wadata suke”.
Da ƙyar Hajiya Bunayya dake sauraransu ta haɗiye wani abu mai masifar ɗaci daya tokare mata maƙoshi Allah ne kaɗai yasan tashin hankali da ɗimuwar hassada da take ciki...
Haka aka riƙa gabatarwa Moddibo da ƴan uwansa
Abokan arziƙi, ƴaƴan Baffaninsa. Da ƴaƴan Goggoninsa sahu-sahu.
Kana bayan an gama aka shiga gabatar masa da Hadimansa wanda zasu riƙa yi masa Hidima.
Bayan an gama wannan.
Jakadiya dake tsaye gefenshi riƙe da wasu Ƙore guda uku ahannunta babban na cike da madaran Shanu fari ƙal.
A hankali ta ajiye su agaban timtim da ƙafan Khausar ke kai sai kuma ta ɗauki ƙamarin Ƙwaryan ta ajiye acikin wanda yake ɗauke da ɗanyen madaran Shanu.
Kana ta ɗauki ɗayan mai matsakaici, tare da matsowa gefen Moddibo ta risina tare da cewa.
“Bismillah zaka wanke ƙafan Amarya da madara da fatan Ubangji Allah ya kareta daga sharrin da yake cikin fadar nan kana Allah ya haɗa ta da Alkhairan dake ciki”.
Juyawa Moddibo yayi tare da kallon Ibraahim da ya dafa kafaɗarsa.
Asma'u kuwa Lumshe idanu tayi tana kallon ƙawarta cike da annashuwa kana tana mamakin tarin al'adunsu masu matuƙar kyau da tsari babu wani abu na bidi'a aciki komai bisa tsari suke gudanar wa...
Ibraahim kuwa dake dage da kafaɗarsa cike da so da girmamawa yace.
“Bismillah Yah Aleey Don Allah kayi mana”.
Lumshe idanu Moddibo yayi tare da ɗaga juya kanshi ya kalli Innayi wacce keji tamkar ta taso tazo ta ɗagashu tasa yayi dukkan abinda ya dace.
Ganin alamun zaƙuwa tare da itane yasashi miƙewa a hankali kana ya dawo gaban Khausar ya zauna akan kujeran da aka ajiye kusa da tum-tim ɗin kujerar da Khausar ke kai kana ya zaune.
Sai kuma ya ɗan kalli Ibarahim dake cewa.
“Ɗa ƙafar dama zaka fara”.
Ɗan hararan Ibraahim yayi kana ya ɗan ronƙofo kaɗan ya sunkuya, a hankali ya sanya hannunsa na dama ya kamo ƙafan Khausar na dama tare da zare mata takalmin, tare da tsirawa fatar kafar lumsassun idanunsa,
Zakariyya ne ya ɗan yi gyaran Muryar da ya sashi,
Ɗan Lumshe ido kana ya buɗesu a hankali, yatsunta sunyi masifar kyau, kana faratun ƙafan ayanke suke fes-fes gwanin ban sha'awa.
Aransa yace ikon Allah wannan ita kuma haka tabar ƙafar nata.
Kansa ya ɗago tare da kallon kyakykyawan fuskarta dake fitar da annuri kana ya tsuke fuska ya ɗan harareta tare da cewa.
“Ko Amaryar shamuwa ana sa mata lalle. Amma ke naga alamun Amaren buzuzuma sun fiki ƙyalli”.
Jin abinda yace yasa ta tura baki da ɗan juya ido.
Ƙafanta ya jawo kana yasa cikin ƙwaryan dake gabansa wanda babu nono aciki ɗan matse ƙafar yayi har saida ta ɗanyi ƙara, shi kuwa wani murmushin da shi kaɗaine yasan ma'anarsa yayi.
Jakadiya kuwa nono ta ɗebo aƙaramin ƙwaryan ta miƙa masa.
Ita kuwa Khausar jin yadda yaja ƙafanta yasa ta risino wanda dai-dai lokacin take tura baki..
Karaf sai akan idanunsa ware manyan idanunsa yayi kana ya motsa laɓɓansa tare da faɗin.
“idanfa kina hararana, ƙwaƙule idanunki zanyi, kafin kije Lahira Ubangji ys ƙona miki su”.
Saurin kallonsa Khausar tayi jin abinda yace girarsa ɗaya ya ɗaga mata tare da cigaba da faɗin.
“Yess ai na lura bakisan daraja da girman miji bako?”...
Uffan batace masa sai ma lumshe idanunta da tayi tana jin yanda ɗumkn tafin hannunsa ke ratsata...
Hannunsa na dama yasa ya tallafi ƙafartata kana ya karɓi ƙwaryar Nonon da hannunsa na hagu ahankali yake zuba Nonon akan ƙafarta...
Yayin da aransa yake tuna tabbas ya taɓa sanin wannan al'adar amafarkinsa da yake yawanyi...
Cike da nutsu da kuma ƙwarewa yake wanke ƙafafunta daga dai-dai idon sau zuwa kan zara-zaran yatsun ta ya wanke fess.
Ita kuwa sai mutsu-mutsi take da yatsun ƙafarta ɗan ji take kamar jakul-ku-kuli yake mata,'.
Yana gama wanke wa sai ga Didi da kanta wani farin ƙyalle mai masifar haske da ƙamshi ta miƙa masa.
Juyawa yayi yaga Mahaifiyarsa tsaye da kanta take bashi.
Didi kuwa kai ta jinjina masa alamar ya karɓa.
Ba musu ya karɓa tare da gogewa Khausar ƙafanta kana ya mayar cikin takalmin ta, sai kuma ya zaro ƙafara na hagu ya wanke kamar yanda yayiwa na damar.
Wani farin ƙyalle kamar na farko mai azabar ƙamshi Didi ta sake miƙa masa ya goge mata ƙafar kana ya ajiye.
Kallonsa Didi tayi tare da faɗin.
“Toh ka matso da kyau sai ka tallafi ƙwaryar Nonon cinyaka kasa hannunta duka biyu ka wanke”.
Da ɗan sauri ya ɗaga kansa ya kalleta.
Lumshe idanu tayi alamar kayi ɗan Albarka.
Kai ya jinjina hakan yau yake jinsa wani irin farin ciki mara misaltuwa tamkar wanda aka yiwa bushara da gidan aljanna.
Kujeran yaja ya matsa kusa da Khausar sosai yayin da Gwiwoyinta ke gugan Gwiwoyinsa.
Bakajin saurin komai sai busan sarewa da tashin jits, Yayin dasu Ibraahim kuwa suka koma ta bayansa suka tsaya, gudun kada su tsaya agaba su tare wa ƴan baya,
Hotuna yimusu ake yi babu tsayawa tako wacce kusurwa hoto ake musu, yayin da Yayunsa ke zuba musu Liƙi.
Ahankali ya kamo lallausan tafukan hannunta ya riƙe acikin nasa kana ya tsunduma su acikin ƙwaryar Nonon da Jakadiya ta ɗaura masa akan cinyarsa wanda aka zuba wasu Jajayen Flowes masu kyau da tsari.
Cikin nutsuwa ya fara wanke hannun, tare da ɗan jan ƴan yatsunta, a hankali, ya ɗan ƙara ware idanunsa lokaci da ya ja ƴar ƙaramar yatsarta ta hannun hagu, gani yadda ta tara faratunta sunyi zaƙo-zaƙo irin dai yanda ƴan matan zamani keyi, sai dai sunyi masifar kyau musamman ma na ƙaramin yatsanta na hagu duk yafi sauran faratun tsawo, matse hannun yayi acikin nasa.
Runtse idanunta tayi cike da raki da shagwaɓa ta furta.
“Wash! Allah”.
Ta faɗa tare da sunkuyo da kanta haɓarta na taɓa goshinsa ahankali ya ɗago kanshi, wanda hakan ya bawa hancinsa damar gogan hancinta.
Cikin tsuke fuska ya sanya ƙwayar idanunsa cikin nata tare da faɗin.
“Meye amfanin wannan farcen da kika bari ajikin ki?”.
Cikin sanyi tace.
“Dan yin susa in ƙaiƙayi ya dameni”.
Sosai ya daure wurin danne yanayin da muryata ta sashi a ciki, a hankali ya ɗan matse yatsar kana a hankali yace.
“Shin bakisan cewa shi farce shine rumfar shaiɗan ajikin ɗan Adam ba?”.
Shiru tayi ba tare da ta cire idonta daga kan sajenshi da takeyiwa kallon kurillaba.
Shi kuwa numfashi ya fesar tare da cewa.
“Ya za'a yi ki tarawa sheɗan Mafaka ajikin ki?No wonder shiyasa kika cika rawan kai ashe muhalli kikayi ibilis a jikinki”.
Bakinta ta tura tana kallon yanda yake matse mata hannu.
Shi kuwa Moddibo cikin sanyin murya ya cigaba da cewa.
“Shiyada duk rashin ji da neman mgn duk kece a gaba ashe-ashe muhalli kika tarawa sheɗan agangar jikinki. Toh kiji da kyau, ko kiyanke faratun nan ko kuwa idan na tashi da kaina zan haɗa da ƴan yatsunki in yanke kana na wurgawa karnuka su cinye”.
Cikin yanayin tsoronsa da sanyin murya tace.
“Dan Allah ka sake min hannuna zafi fa yake min”.
Sake matsawo kusa da ita yayi tare da faɗin.
“Bazan sake ba”. Da sauri tace.
“Afwan”.
Cikin kasala yace.
“Sai kinyi al'ƙawarin zaki yanke farcen”.
Da sauri ta gyaɗa masa kai cikin narke fuska tace.
“Nayi al'ƙawari zan yanke amma zan bar ɗaya”.
Fuska ya ɗaure tare da faɗin.
“Ban yarda ba duka zaki yanke”.
Kai ta gyaɗa kana tace.
“Na yarda zan yanke toh ka sake min hannu”.
Wani irin murmushi mutanen dake wajen sukayi yayinda wasu ke binsu da kallon sha'awa.
“Allah ya maka albarka Ubangji Allah ya albarkanci rayuwarka. Allah ya baka zaman lafiya da matarka!”.
Haka nan Moddibo yake jin wani irin farin ciki ji yake yau kamar ranan Sallah ne, sabida wani irin nishaɗi da yakeji tamkar wanda aka yiwa bushara da Aljanna asaman lips ɗin sa yake amswa da.
“Ameen Ameen”.
Haka nan yake jin farin cikin addu'ar da Mahaifiyar sa da Mahaifinsa keyi masa...
Liƙi suka cigaba dayi musu suna zuba musu kuɗi kamar ba'asan darajar su ba...
Sarkin zaki kuwa hannunsa riƙe da Microphone yace.
“Hattara dai manyan bisa kanku wan'nan sune manyan ƙasar Morocco baki ɗayanta. Jiga-jigan manyan cikin birnin Rarat baki ɗaya manyane bisa kanku ku amsa da Ameen dan addu'a ce ta manyan Ameen.
Baki ɗaya mutanen falon suka amsa da.
“Ameen”.
Saboda sun san cewa addu'a da fatan Al'khairi iyayensa ke masa bayan sun gama suka juya suka tafi...
Aunty Ruƙayya da farin ciki ya gama cikata ganin yanda Moddibo da Khausar sukayi bala'in da cewa ga kuma yanda Moddibo ke raɗawa Khausar magana akunne wanda duk mai kallonsu a matsayin zantukan masoyane sukeyi yasa ta kalli Hajiya Bunayya wacce itace akusa da ita kana tace.
“Dan Allah Hajiya kalli Khausar da Moddibo tamkar dan junansu aka halicce su, haƙiƙa sun dace da juna Allah yayi Khausar zaɓi da mafi Al'khairi Ubangiji ya kawar da idanun maƙiya akansu”.
Yaƙe Hajiya Bunayya tayi Amaimakon tace Ameen sai ta sunkuyar da kanta tayi tare da cewa.
“Aikam”.
Wani irin zafi da ƙuna zuciyarta keyi ba zato taji hawayen hassada da ƙyashi na zuba daga idanunta ina ma ace Aminanta ce ke cikin wannan Daular duniya..
Daga can cikin falon kuwa Wasu zugan Maza da Mata manya ne suka nufi wajensu Moddibo da Khausar.
Sarkin Zaƙi na ganinsu ya ɗaga sautin muryarsa tare da cewa.
“Hattara dai Ango da Amarya ga Baffanayenku nan da Goggoninku”.
Ahankali Moddibo ya ɗaga kai yana kallonsu cikin wani irin yanayi mara misaltuwa wai yau shine acikin ahalinsa ana gabatar mishi dasu sahu-sahu.
Su kuwa cike da tarin ƙaunarsa suka riƙa yi musu liƙi da kuɗaɗe masu tarin yawa.
Aunty Hawwa ce ta kalli Aunty Hajara wacce suke daga ɗaya gefen Hajiya Bunayya kana Aunty Hauwa tace.
“Masha Allah Kinga yanda ake zubar da kuɗi tamkar ba'a cikin tsadar rayuwa”.
Dariya Aunty Hajara ta sanya tare da cewa.
“Aikam acikin wannan ahalin. Basuma san wani abu mai suna talauci ba komai nasu cikin wadata suke”.
Da ƙyar Hajiya Bunayya dake sauraransu ta haɗiye wani abu mai masifar ɗaci daya tokare mata maƙoshi Allah ne kaɗai yasan tashin hankali da ɗimuwar hassada da take ciki...
Haka aka riƙa gabatarwa Moddibo da ƴan uwansa
Abokan arziƙi, ƴaƴan Baffaninsa. Da ƴaƴan Goggoninsa sahu-sahu.
Kana bayan an gama aka shiga gabatar masa da Hadimansa wanda zasu riƙa yi masa Hidima.
Bayan an gama wannan.
Jakadiya dake tsaye gefenshi riƙe da wasu Ƙore guda uku ahannunta babban na cike da madaran Shanu fari ƙal.
A hankali ta ajiye su agaban timtim da ƙafan Khausar ke kai sai kuma ta ɗauki ƙamarin Ƙwaryan ta ajiye acikin wanda yake ɗauke da ɗanyen madaran Shanu.
Kana ta ɗauki ɗayan mai matsakaici, tare da matsowa gefen Moddibo ta risina tare da cewa.
“Bismillah zaka wanke ƙafan Amarya da madara da fatan Ubangji Allah ya kareta daga sharrin da yake cikin fadar nan kana Allah ya haɗa ta da Alkhairan dake ciki”.
Juyawa Moddibo yayi tare da kallon Ibraahim da ya dafa kafaɗarsa.
Asma'u kuwa Lumshe idanu tayi tana kallon ƙawarta cike da annashuwa kana tana mamakin tarin al'adunsu masu matuƙar kyau da tsari babu wani abu na bidi'a aciki komai bisa tsari suke gudanar wa...
Ibraahim kuwa dake dage da kafaɗarsa cike da so da girmamawa yace.
“Bismillah Yah Aleey Don Allah kayi mana”.
Lumshe idanu Moddibo yayi tare da ɗaga juya kanshi ya kalli Innayi wacce keji tamkar ta taso tazo ta ɗagashu tasa yayi dukkan abinda ya dace.
Ganin alamun zaƙuwa tare da itane yasashi miƙewa a hankali kana ya dawo gaban Khausar ya zauna akan kujeran da aka ajiye kusa da tum-tim ɗin kujerar da Khausar ke kai kana ya zaune.
Sai kuma ya ɗan kalli Ibarahim dake cewa.
“Ɗa ƙafar dama zaka fara”.
Ɗan hararan Ibraahim yayi kana ya ɗan ronƙofo kaɗan ya sunkuya, a hankali ya sanya hannunsa na dama ya kamo ƙafan Khausar na dama tare da zare mata takalmin, tare da tsirawa fatar kafar lumsassun idanunsa,
Zakariyya ne ya ɗan yi gyaran Muryar da ya sashi,
Ɗan Lumshe ido kana ya buɗesu a hankali, yatsunta sunyi masifar kyau, kana faratun ƙafan ayanke suke fes-fes gwanin ban sha'awa.
Aransa yace ikon Allah wannan ita kuma haka tabar ƙafar nata.
Kansa ya ɗago tare da kallon kyakykyawan fuskarta dake fitar da annuri kana ya tsuke fuska ya ɗan harareta tare da cewa.
“Ko Amaryar shamuwa ana sa mata lalle. Amma ke naga alamun Amaren buzuzuma sun fiki ƙyalli”.
Jin abinda yace yasa ta tura baki da ɗan juya ido.
Ƙafanta ya jawo kana yasa cikin ƙwaryan dake gabansa wanda babu nono aciki ɗan matse ƙafar yayi har saida ta ɗanyi ƙara, shi kuwa wani murmushin da shi kaɗaine yasan ma'anarsa yayi.
Jakadiya kuwa nono ta ɗebo aƙaramin ƙwaryan ta miƙa masa.
Ita kuwa Khausar jin yadda yaja ƙafanta yasa ta risino wanda dai-dai lokacin take tura baki..
Karaf sai akan idanunsa ware manyan idanunsa yayi kana ya motsa laɓɓansa tare da faɗin.
“idanfa kina hararana, ƙwaƙule idanunki zanyi, kafin kije Lahira Ubangji ys ƙona miki su”.
Saurin kallonsa Khausar tayi jin abinda yace girarsa ɗaya ya ɗaga mata tare da cigaba da faɗin.
“Yess ai na lura bakisan daraja da girman miji bako?”...
Uffan batace masa sai ma lumshe idanunta da tayi tana jin yanda ɗumkn tafin hannunsa ke ratsata...
Hannunsa na dama yasa ya tallafi ƙafartata kana ya karɓi ƙwaryar Nonon da hannunsa na hagu ahankali yake zuba Nonon akan ƙafarta...
Yayin da aransa yake tuna tabbas ya taɓa sanin wannan al'adar amafarkinsa da yake yawanyi...
Cike da nutsu da kuma ƙwarewa yake wanke ƙafafunta daga dai-dai idon sau zuwa kan zara-zaran yatsun ta ya wanke fess.
Ita kuwa sai mutsu-mutsi take da yatsun ƙafarta ɗan ji take kamar jakul-ku-kuli yake mata,'.
Yana gama wanke wa sai ga Didi da kanta wani farin ƙyalle mai masifar haske da ƙamshi ta miƙa masa.
Juyawa yayi yaga Mahaifiyarsa tsaye da kanta take bashi.
Didi kuwa kai ta jinjina masa alamar ya karɓa.
Ba musu ya karɓa tare da gogewa Khausar ƙafanta kana ya mayar cikin takalmin ta, sai kuma ya zaro ƙafara na hagu ya wanke kamar yanda yayiwa na damar.
Wani farin ƙyalle kamar na farko mai azabar ƙamshi Didi ta sake miƙa masa ya goge mata ƙafar kana ya ajiye.
Kallonsa Didi tayi tare da faɗin.
“Toh ka matso da kyau sai ka tallafi ƙwaryar Nonon cinyaka kasa hannunta duka biyu ka wanke”.
Da ɗan sauri ya ɗaga kansa ya kalleta.
Lumshe idanu tayi alamar kayi ɗan Albarka.
Kai ya jinjina hakan yau yake jinsa wani irin farin ciki mara misaltuwa tamkar wanda aka yiwa bushara da gidan aljanna.
Kujeran yaja ya matsa kusa da Khausar sosai yayin da Gwiwoyinta ke gugan Gwiwoyinsa.
Bakajin saurin komai sai busan sarewa da tashin jits, Yayin dasu Ibraahim kuwa suka koma ta bayansa suka tsaya, gudun kada su tsaya agaba su tare wa ƴan baya,
Hotuna yimusu ake yi babu tsayawa tako wacce kusurwa hoto ake musu, yayin da Yayunsa ke zuba musu Liƙi.
Ahankali ya kamo lallausan tafukan hannunta ya riƙe acikin nasa kana ya tsunduma su acikin ƙwaryar Nonon da Jakadiya ta ɗaura masa akan cinyarsa wanda aka zuba wasu Jajayen Flowes masu kyau da tsari.
Cikin nutsuwa ya fara wanke hannun, tare da ɗan jan ƴan yatsunta, a hankali, ya ɗan ƙara ware idanunsa lokaci da ya ja ƴar ƙaramar yatsarta ta hannun hagu, gani yadda ta tara faratunta sunyi zaƙo-zaƙo irin dai yanda ƴan matan zamani keyi, sai dai sunyi masifar kyau musamman ma na ƙaramin yatsanta na hagu duk yafi sauran faratun tsawo, matse hannun yayi acikin nasa.
Runtse idanunta tayi cike da raki da shagwaɓa ta furta.
“Wash! Allah”.
Ta faɗa tare da sunkuyo da kanta haɓarta na taɓa goshinsa ahankali ya ɗago kanshi, wanda hakan ya bawa hancinsa damar gogan hancinta.
Cikin tsuke fuska ya sanya ƙwayar idanunsa cikin nata tare da faɗin.
“Meye amfanin wannan farcen da kika bari ajikin ki?”.
Cikin sanyi tace.
“Dan yin susa in ƙaiƙayi ya dameni”.
Sosai ya daure wurin danne yanayin da muryata ta sashi a ciki, a hankali ya ɗan matse yatsar kana a hankali yace.
“Shin bakisan cewa shi farce shine rumfar shaiɗan ajikin ɗan Adam ba?”.
Shiru tayi ba tare da ta cire idonta daga kan sajenshi da takeyiwa kallon kurillaba.
Shi kuwa numfashi ya fesar tare da cewa.
“Ya za'a yi ki tarawa sheɗan Mafaka ajikin ki?No wonder shiyasa kika cika rawan kai ashe muhalli kikayi ibilis a jikinki”.
Bakinta ta tura tana kallon yanda yake matse mata hannu.
Shi kuwa Moddibo cikin sanyin murya ya cigaba da cewa.
“Shiyada duk rashin ji da neman mgn duk kece a gaba ashe-ashe muhalli kika tarawa sheɗan agangar jikinki. Toh kiji da kyau, ko kiyanke faratun nan ko kuwa idan na tashi da kaina zan haɗa da ƴan yatsunki in yanke kana na wurgawa karnuka su cinye”.
Cikin yanayin tsoronsa da sanyin murya tace.
“Dan Allah ka sake min hannuna zafi fa yake min”.
Sake matsawo kusa da ita yayi tare da faɗin.
“Bazan sake ba”. Da sauri tace.
“Afwan”.
Cikin kasala yace.
“Sai kinyi al'ƙawarin zaki yanke farcen”.
Da sauri ta gyaɗa masa kai cikin narke fuska tace.
“Nayi al'ƙawari zan yanke amma zan bar ɗaya”.
Fuska ya ɗaure tare da faɗin.
“Ban yarda ba duka zaki yanke”.
Kai ta gyaɗa kana tace.
“Na yarda zan yanke toh ka sake min hannu”.
Wani irin murmushi mutanen dake wajen sukayi yayinda wasu ke binsu da kallon sha'awa.