Sashe 117
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin sauƙe numfashi ta kalli Hajiya Lami Idanunta cike da ruwan hawaye tace.
“Na lura ko ɗana Sulaiman ƙyamar zama kusa dani yake yi sannan Lamiɗo koda abinci na kai masa sai yace in tattara in fita dashi shi ya ƙoshi.
Hankalina ya tashi Hajiya Lami kaddai mugun abinda naje yiwa Khausar ya dawo kaina ya addabi rayuwata?
Ji nake kamar ƙaiƙayin yasa gabana ya haɗe da bayana”.
Zare idanu Hajiya Lami tayi cikin yanayin tashin hankali tace.
“Mun shiga ukun mu Hajiya Bunayya wannan wani irin abu muke fuskanta a rayuwar ki kalli haka Samira fa yanzu yanda ta bushe ta rame duk ta lalace sannan nima bana bacci dana kwanta da daddare sai muggan mafarkai na rasa yanda zanyi da rayuwarta”
Cike da damuwa Hajiya Bunayya ta girgiza kai tare da cewa.
“Ke koni?,Auren Asiya sai matsowa yake gashi Lamiɗo ko zama kusa dani muyi maganar Auren nan baya yarda sai kyara da hantara ina ga baƙin jinin da Boka yace Khausar za tayi ya tabbata nice nayi shi”.
Cikin mamaki Hajiya Lami ta tallafe kuncin ta tana sauraron masifar daya riskesu lokacin ɗaya duniya tayi musu atishawar kaji.
Hajiya Bunayya kuwa da damuwa ta cigaba da cewa.
“Ƴaƴana ma duk sun fita harƙana dama Asiya ita tun can ba shiga harƙana take ba.
Kuma abin mamaki itace take ɗan daurewa tana zama kusa dani shekaran juya da taga ina ta fama da ƙaiƙayin nan ina zirya da sintiri shine ta faɗa wa Lamiɗo aje asibiti koda ta faɗa masa ma cewa yayi shi bazai samu damar kaina ba inje in Kai kaina idan na kuɗine in faɗa masa ko nawa ne magana ta ƙare”.
Tallafe kunci Hajiya Lami tayi kana tace.
“Ohhh Mukam munga ta kanmu wannan al'amari wacce irin Musifa da fitinace ta Kunno mana kai”.
Kafin Hajiya Bunayya tace wani abu Asiya ta fito daga cikin Bedroom ɗin ta kana ta zauna gefen su tare da girgiza kanta sai kuma ta kallesu ahankali ta sunkuyar da kanta Idanunta na cika da ruwan hawaye murya cike da rauni tace.
“Umma ku koma ga Allah ku nemi gafarar waɗanda kuka cutar sai kuga Allah ya kawo muku sauƙi wannan ishara ne Ubangiji yai muku Allah ya soku da Rahma ne daya kama ku tunda ranku baku mutu ba dan haka kunemi yafiyar wa'anda kuka cutar tun kafin lokaci ya ƙure muku”.
Kallonta suke tunda ta fara magana har ta dasa aya basu katse taba kamar yadda suka sqba.
Karo na farko a rayuwar su da suka ji jikinsu ya mutu akan abinda suke aikatawa kana kalaman ta ya ratsa su.
Ganin yanda jikinsu yayi sanyi alamar nadama tare dasu yasa cike da girmamawa matsayinsu na iyaye taci gaba dayi musu nasiyya mai ratsa jiki kana ta nuna musu kuskuren su da basu shawarar su nemi gafarar waɗanda suka cutar kana su nemi yafiyar Allah da yardarsa...
Morocco bangaren Khausar sosai al'amura ke tafiya yau ya kama Auren Asma'u da Dr Jameel saura mako biyu haka Auren Asiya da Zakariyya da kuma Yah Aliyu da Dija saura mako biyu Cif-cif sukuma a shirye-shiryen su saura Mako ɗaya su tafi Nigeria.
Ahankali ta ɗaga kanta tare da zubawa ƙofar falonta Ido jin sanyayyan kamshin turaren Moddibo wanda da alama ya dade da dawowa harma ya shiga side ɗin sa yayi wanka kai tsaye gefenta ya nufa ya ya kwanta kana ya ɗaura kansa kan cinyarta kasancewar tana kan 3sitter sai kuma yasa hannunsa ya shafa cikinta kafin ahankali ya maida hannunsa kan cikinta yace.
“Baby ya kake kana lafiya?”.
Murmushi Khausar tayi amma bata ce komai ba.
Sake manna kansa da cikin yayi tare da cewa.
“Meimei ta baka abinci Kaci?”.
Still shiru tayi sai kuma ya ɗago ya kalleta tare da cewa.
“Kinci abinci ko?”.
Kai ta gyaɗa masa tare da faɗin.
“Eh wallahi da gaske naci”.
Cikin tsira mata idanu yace.
“Da gaske?,Me kika ci?”.
Kai ta gyaɗa kana tace.
“Nayi wainar Fulawa kuma naci guda uku”.
Kai ya jinjina tare da faɗin.
“Masha Allah Alhamdulillah haka yayi kyau ai naga cikin ya ɗan tashi”.
A hankali ta ɗan ɗaura hannunta bisa sajenshi tana shafawa a hankali tace.
“Yau ina ka tafi tunda safe baka dawo ba”.
Saman hannunta ya shafa tare da cewa.
“Mun fita ne da Dr Jameel da Zakariyya kinsa ya dawo tun shekaran jiya sunje sun nuna min gidansu an tsara musu komai masha Allah.
Dan su bikin saura kwana goma ma zasuyi gaba”.
Cikin sauri ta kallesa sai kuma ta langwaɓar da kai tace.
”Toh muma mu tafi dasu mana Yah Mu'allim”.
Kai ya girgiza tare da faɗin.
”Tafiyarsu da ban tamu da ban”.
Sake marairaice murya tayi tace.
“Allah mu tafi dasu na ƙagu naga Raudat nayi kewar Momyna sosai”.
Cikin kwantar mata da hankali yace.
“In sha Allah zakije ki ganta”.
Kallonsa tayi sai kuma ta make kafaɗa tace.
“Ni dai wallahi da zamu tafi tare nafi so".
Yana gyara kwanciyarsa yace.
“Suɗin ma ina ga zance su haƙura kawai mu tafi tare, tunda saura sati ɗaya zamu je gwara su haƙura mu tafi”.
Cikin sauƙe ajiyar zuciya tace.
“Toh Allah yasa su haƙura mu tafi".
“Ameen”.
Sai kuma yayi saurin miƙewa daga jikinta jin wayarsa na ruri ɗagawa yayi ta kalli screen ɗin, sunan Sheikh Jabeer ya bayyana da murmushi afuskarsa ya dauka tare da cewa.
“Kaka”.
Daga ɗaya bangaren Sheikh Jabeer dake zaune cikin falonsa A'ish ɗin sa na zaune gefe ya saki murmushi tare da cewa.
“Na'am Jikalle Barka da yamma”.
Moddibo na gyarawa Khausar zama ajikinsa yace.
“Barka dai ya gida?".
Ahankali Sheykh yace.
“Lafiya lau”.
Ya ƙare mgnar yana gyara zama yace.
“Kwanaki munyi magana da kai akan ɓatan Jameel da plate number motar ɗin da muke magana akai?”.
Kai Moddibo ya gyaɗa tare da faɗin.
“Hakane”.
Anutse Sheikh Jabeer yace.
“Masha Allah idan ban manta ba cikin mutanenku akwai wacce tasan number motocin da ake zargin suna yawan binbiyarku gab da ɓacewan Jameel ”.
Kai Moddibo ya jinjina yana mai tuno J dinsa yace.
“Eh Khausar ce ma ”.
Cikin sauƙe ajiyar zuciya Sheikh Jabeer ya gyara zamansa tare da faɗin.
“Toh ba matsala idan har yanzu tana riƙe da number ka turo min saboda akwai ƙungiyar da Tabital Fulani suka kama a Taraba.
Wanda an kamasu da motoci tawaga guda kusan guda goma wanda gaskiya muke zaton motoci ne da suke harkan Kidnapping dasu saboda a dokar adaji aka kama su da kuma makamai kana da tarin kuɗaɗe".
Numfashi Moddibo ya fesar kana yace.
“Toh shikenan In sha Allah bari muyi maganar da ita”.
Bayan ya katse wayar ya maida kallonsa gare ta ahankali ya riƙe hannayenta cikin nasa cikin natsuwa ta zuba masa ido.
Cikin fesar da numfashi yace.
“Minha batun number motar nan da Asma'u tace kin riƙe,har yanzu kina riƙe dashi akan ki?”.
Kai ta gyaɗa cikin tabbatar tace.
“Tabbas kuwa har abada bazan manta number motar nan ba saboda na ganta alokuta uku maban-banta na ganshi a Jauro Yaya.
Na ganshi a bakin Makarantar mu.
Sannan ranan da muka yi rabuwa ta ƙarshe da Yah Jameel na ganshi yana bibiyarmu”.
Numfashi ya fesar tare da faɗin.
“Yanzu zaki iya faɗa min?”.
Kai ta gyaɗa mishi.
Ganin hakane yasa ya
ɗauki wayarsa ya danna kan number Sheikh Jabeer ya shiga wajen text yace.
“Gashi sa”.
Karɓa tayi ta rubuta number motar da komai da komai harda collor ta miƙa masa number ya tsirawa idanu sai kuma ya kalleta yace.
“Kin tabbatar shine dai-dai?”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Na tabbata shine babu shakka ko Haufi ko yanzu na rufe Idanuna ina kallon number motar”.
Kai ya jinjina kana yace.
“Ok ba laifi”.
Ba ɓata lokacin ya yiwa Sheikh Jabeer sending.
Ahankali ya maida hannunsa kan cikin nata wanda zuwa yanzu ya fara bayyana kallonta yayi tare da langwaɓar da kai yace.
“Minha yunwa nake ji mai zan samu?”.
Tana lunshe Idanunta cikin nasa tace.
“Mekake so?".
Muryansa cike da kasala ya sake narkewa jikinta tare da cewa.
“Me kika yi min?”.
Manyan Idanunta ta juya sai kuma ta sakar masa da murmushi tare da cewa.
“Nayi maka abinda kake so?”.
Ɗan ware idanunsa yayi yana cigaba da shafa cikinta yace.
“Mene?”.
Langwaɓar da kai tayi tace.
“Nayi dambu a tunanina zan iya ci sai kuma naji bazan iya ciba”.
Wani kallo ya mata me cike da tarin tausayi da jin ƙai yace.
“Ke kuma me yake miki daɗi In banda Fakala ba”.
Da sauri ta sanya tafin hannunta ta rufe fuskarta tare da cewa.
“Kai Yah Mu'allim”.
Kai ya jinjina kana yace.
“Ehem sai an jima da daddare zaki ce min kina son pakala”.
Marairaice fuska tayi kana tace.
“Ni dai wallahi kabar faɗa min haka kar kayi min sharri”.
Idanunsa ya buɗe kanta tare da faɗin.
“Sharrine ma?,Toh bari zan kama kine?”.
Murmushi tayi tare da faɗawa jikinsa amma bata ce komai ba.
AnanTaraba shirye-shiryen biki ya kankama tuni aka fara gyara amare an killace su.
Momy da kanta je gyara Asma'u Asiya ita ke mata Dilke sai wani ƙyalli suke sunyi kyau gwanin ban sha'awa soyayyar ta da Dr Jameel ɗin ta kuwa na tafiya hakama su Asiya.
Yau ya kama Auren saura kwana goma wanda ya rage saura kwana uku Moddibo su taho da Angwaye da ƴan ɗaurin Aure.
Yau tun safe Ummi da kanta da Asma'u suka tafi gidansu Innayi kasancewar key na hannunta Ummi da kanta ta shiga Side ɗin Moddibo da kanta ta gyara masa ta killace Asma'u kuwa gefen Innayi ta gyara ta killace ko ina yayi gonin ban sha'awa.
Ga kuma sabbin part guda biyu da ake ƙenƙesa sabon gini, na alfarma wanda tuni an gama komai nasu, wanda bisa shawarar inanayi aka tsara da umarnin Abualeey tare jagorancin Abban Jameel abune na kuɗi shiyasa tuni an gamsu wanda nanne masauƙinsu in sun iso.
“Na lura ko ɗana Sulaiman ƙyamar zama kusa dani yake yi sannan Lamiɗo koda abinci na kai masa sai yace in tattara in fita dashi shi ya ƙoshi.
Hankalina ya tashi Hajiya Lami kaddai mugun abinda naje yiwa Khausar ya dawo kaina ya addabi rayuwata?
Ji nake kamar ƙaiƙayin yasa gabana ya haɗe da bayana”.
Zare idanu Hajiya Lami tayi cikin yanayin tashin hankali tace.
“Mun shiga ukun mu Hajiya Bunayya wannan wani irin abu muke fuskanta a rayuwar ki kalli haka Samira fa yanzu yanda ta bushe ta rame duk ta lalace sannan nima bana bacci dana kwanta da daddare sai muggan mafarkai na rasa yanda zanyi da rayuwarta”
Cike da damuwa Hajiya Bunayya ta girgiza kai tare da cewa.
“Ke koni?,Auren Asiya sai matsowa yake gashi Lamiɗo ko zama kusa dani muyi maganar Auren nan baya yarda sai kyara da hantara ina ga baƙin jinin da Boka yace Khausar za tayi ya tabbata nice nayi shi”.
Cikin mamaki Hajiya Lami ta tallafe kuncin ta tana sauraron masifar daya riskesu lokacin ɗaya duniya tayi musu atishawar kaji.
Hajiya Bunayya kuwa da damuwa ta cigaba da cewa.
“Ƴaƴana ma duk sun fita harƙana dama Asiya ita tun can ba shiga harƙana take ba.
Kuma abin mamaki itace take ɗan daurewa tana zama kusa dani shekaran juya da taga ina ta fama da ƙaiƙayin nan ina zirya da sintiri shine ta faɗa wa Lamiɗo aje asibiti koda ta faɗa masa ma cewa yayi shi bazai samu damar kaina ba inje in Kai kaina idan na kuɗine in faɗa masa ko nawa ne magana ta ƙare”.
Tallafe kunci Hajiya Lami tayi kana tace.
“Ohhh Mukam munga ta kanmu wannan al'amari wacce irin Musifa da fitinace ta Kunno mana kai”.
Kafin Hajiya Bunayya tace wani abu Asiya ta fito daga cikin Bedroom ɗin ta kana ta zauna gefen su tare da girgiza kanta sai kuma ta kallesu ahankali ta sunkuyar da kanta Idanunta na cika da ruwan hawaye murya cike da rauni tace.
“Umma ku koma ga Allah ku nemi gafarar waɗanda kuka cutar sai kuga Allah ya kawo muku sauƙi wannan ishara ne Ubangiji yai muku Allah ya soku da Rahma ne daya kama ku tunda ranku baku mutu ba dan haka kunemi yafiyar wa'anda kuka cutar tun kafin lokaci ya ƙure muku”.
Kallonta suke tunda ta fara magana har ta dasa aya basu katse taba kamar yadda suka sqba.
Karo na farko a rayuwar su da suka ji jikinsu ya mutu akan abinda suke aikatawa kana kalaman ta ya ratsa su.
Ganin yanda jikinsu yayi sanyi alamar nadama tare dasu yasa cike da girmamawa matsayinsu na iyaye taci gaba dayi musu nasiyya mai ratsa jiki kana ta nuna musu kuskuren su da basu shawarar su nemi gafarar waɗanda suka cutar kana su nemi yafiyar Allah da yardarsa...
Morocco bangaren Khausar sosai al'amura ke tafiya yau ya kama Auren Asma'u da Dr Jameel saura mako biyu haka Auren Asiya da Zakariyya da kuma Yah Aliyu da Dija saura mako biyu Cif-cif sukuma a shirye-shiryen su saura Mako ɗaya su tafi Nigeria.
Ahankali ta ɗaga kanta tare da zubawa ƙofar falonta Ido jin sanyayyan kamshin turaren Moddibo wanda da alama ya dade da dawowa harma ya shiga side ɗin sa yayi wanka kai tsaye gefenta ya nufa ya ya kwanta kana ya ɗaura kansa kan cinyarta kasancewar tana kan 3sitter sai kuma yasa hannunsa ya shafa cikinta kafin ahankali ya maida hannunsa kan cikinta yace.
“Baby ya kake kana lafiya?”.
Murmushi Khausar tayi amma bata ce komai ba.
Sake manna kansa da cikin yayi tare da cewa.
“Meimei ta baka abinci Kaci?”.
Still shiru tayi sai kuma ya ɗago ya kalleta tare da cewa.
“Kinci abinci ko?”.
Kai ta gyaɗa masa tare da faɗin.
“Eh wallahi da gaske naci”.
Cikin tsira mata idanu yace.
“Da gaske?,Me kika ci?”.
Kai ta gyaɗa kana tace.
“Nayi wainar Fulawa kuma naci guda uku”.
Kai ya jinjina tare da faɗin.
“Masha Allah Alhamdulillah haka yayi kyau ai naga cikin ya ɗan tashi”.
A hankali ta ɗan ɗaura hannunta bisa sajenshi tana shafawa a hankali tace.
“Yau ina ka tafi tunda safe baka dawo ba”.
Saman hannunta ya shafa tare da cewa.
“Mun fita ne da Dr Jameel da Zakariyya kinsa ya dawo tun shekaran jiya sunje sun nuna min gidansu an tsara musu komai masha Allah.
Dan su bikin saura kwana goma ma zasuyi gaba”.
Cikin sauri ta kallesa sai kuma ta langwaɓar da kai tace.
”Toh muma mu tafi dasu mana Yah Mu'allim”.
Kai ya girgiza tare da faɗin.
”Tafiyarsu da ban tamu da ban”.
Sake marairaice murya tayi tace.
“Allah mu tafi dasu na ƙagu naga Raudat nayi kewar Momyna sosai”.
Cikin kwantar mata da hankali yace.
“In sha Allah zakije ki ganta”.
Kallonsa tayi sai kuma ta make kafaɗa tace.
“Ni dai wallahi da zamu tafi tare nafi so".
Yana gyara kwanciyarsa yace.
“Suɗin ma ina ga zance su haƙura kawai mu tafi tare, tunda saura sati ɗaya zamu je gwara su haƙura mu tafi”.
Cikin sauƙe ajiyar zuciya tace.
“Toh Allah yasa su haƙura mu tafi".
“Ameen”.
Sai kuma yayi saurin miƙewa daga jikinta jin wayarsa na ruri ɗagawa yayi ta kalli screen ɗin, sunan Sheikh Jabeer ya bayyana da murmushi afuskarsa ya dauka tare da cewa.
“Kaka”.
Daga ɗaya bangaren Sheikh Jabeer dake zaune cikin falonsa A'ish ɗin sa na zaune gefe ya saki murmushi tare da cewa.
“Na'am Jikalle Barka da yamma”.
Moddibo na gyarawa Khausar zama ajikinsa yace.
“Barka dai ya gida?".
Ahankali Sheykh yace.
“Lafiya lau”.
Ya ƙare mgnar yana gyara zama yace.
“Kwanaki munyi magana da kai akan ɓatan Jameel da plate number motar ɗin da muke magana akai?”.
Kai Moddibo ya gyaɗa tare da faɗin.
“Hakane”.
Anutse Sheikh Jabeer yace.
“Masha Allah idan ban manta ba cikin mutanenku akwai wacce tasan number motocin da ake zargin suna yawan binbiyarku gab da ɓacewan Jameel ”.
Kai Moddibo ya jinjina yana mai tuno J dinsa yace.
“Eh Khausar ce ma ”.
Cikin sauƙe ajiyar zuciya Sheikh Jabeer ya gyara zamansa tare da faɗin.
“Toh ba matsala idan har yanzu tana riƙe da number ka turo min saboda akwai ƙungiyar da Tabital Fulani suka kama a Taraba.
Wanda an kamasu da motoci tawaga guda kusan guda goma wanda gaskiya muke zaton motoci ne da suke harkan Kidnapping dasu saboda a dokar adaji aka kama su da kuma makamai kana da tarin kuɗaɗe".
Numfashi Moddibo ya fesar kana yace.
“Toh shikenan In sha Allah bari muyi maganar da ita”.
Bayan ya katse wayar ya maida kallonsa gare ta ahankali ya riƙe hannayenta cikin nasa cikin natsuwa ta zuba masa ido.
Cikin fesar da numfashi yace.
“Minha batun number motar nan da Asma'u tace kin riƙe,har yanzu kina riƙe dashi akan ki?”.
Kai ta gyaɗa cikin tabbatar tace.
“Tabbas kuwa har abada bazan manta number motar nan ba saboda na ganta alokuta uku maban-banta na ganshi a Jauro Yaya.
Na ganshi a bakin Makarantar mu.
Sannan ranan da muka yi rabuwa ta ƙarshe da Yah Jameel na ganshi yana bibiyarmu”.
Numfashi ya fesar tare da faɗin.
“Yanzu zaki iya faɗa min?”.
Kai ta gyaɗa mishi.
Ganin hakane yasa ya
ɗauki wayarsa ya danna kan number Sheikh Jabeer ya shiga wajen text yace.
“Gashi sa”.
Karɓa tayi ta rubuta number motar da komai da komai harda collor ta miƙa masa number ya tsirawa idanu sai kuma ya kalleta yace.
“Kin tabbatar shine dai-dai?”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Na tabbata shine babu shakka ko Haufi ko yanzu na rufe Idanuna ina kallon number motar”.
Kai ya jinjina kana yace.
“Ok ba laifi”.
Ba ɓata lokacin ya yiwa Sheikh Jabeer sending.
Ahankali ya maida hannunsa kan cikin nata wanda zuwa yanzu ya fara bayyana kallonta yayi tare da langwaɓar da kai yace.
“Minha yunwa nake ji mai zan samu?”.
Tana lunshe Idanunta cikin nasa tace.
“Mekake so?".
Muryansa cike da kasala ya sake narkewa jikinta tare da cewa.
“Me kika yi min?”.
Manyan Idanunta ta juya sai kuma ta sakar masa da murmushi tare da cewa.
“Nayi maka abinda kake so?”.
Ɗan ware idanunsa yayi yana cigaba da shafa cikinta yace.
“Mene?”.
Langwaɓar da kai tayi tace.
“Nayi dambu a tunanina zan iya ci sai kuma naji bazan iya ciba”.
Wani kallo ya mata me cike da tarin tausayi da jin ƙai yace.
“Ke kuma me yake miki daɗi In banda Fakala ba”.
Da sauri ta sanya tafin hannunta ta rufe fuskarta tare da cewa.
“Kai Yah Mu'allim”.
Kai ya jinjina kana yace.
“Ehem sai an jima da daddare zaki ce min kina son pakala”.
Marairaice fuska tayi kana tace.
“Ni dai wallahi kabar faɗa min haka kar kayi min sharri”.
Idanunsa ya buɗe kanta tare da faɗin.
“Sharrine ma?,Toh bari zan kama kine?”.
Murmushi tayi tare da faɗawa jikinsa amma bata ce komai ba.
AnanTaraba shirye-shiryen biki ya kankama tuni aka fara gyara amare an killace su.
Momy da kanta je gyara Asma'u Asiya ita ke mata Dilke sai wani ƙyalli suke sunyi kyau gwanin ban sha'awa soyayyar ta da Dr Jameel ɗin ta kuwa na tafiya hakama su Asiya.
Yau ya kama Auren saura kwana goma wanda ya rage saura kwana uku Moddibo su taho da Angwaye da ƴan ɗaurin Aure.
Yau tun safe Ummi da kanta da Asma'u suka tafi gidansu Innayi kasancewar key na hannunta Ummi da kanta ta shiga Side ɗin Moddibo da kanta ta gyara masa ta killace Asma'u kuwa gefen Innayi ta gyara ta killace ko ina yayi gonin ban sha'awa.
Ga kuma sabbin part guda biyu da ake ƙenƙesa sabon gini, na alfarma wanda tuni an gama komai nasu, wanda bisa shawarar inanayi aka tsara da umarnin Abualeey tare jagorancin Abban Jameel abune na kuɗi shiyasa tuni an gamsu wanda nanne masauƙinsu in sun iso.