Sashe 30
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe cikin sanyin murya yace.
“A'a ba sai kace min Alh nan ba ka kirani da sunana kawai”.
Kai ya gyaɗa yana jinjina karamcinsa Aransa yace yana nan kamar ƙaninsa Ibrahim Youssef Muhammad Mouley. Ibrahim bashi da girman kai sai dai shi Ibrahim yafi wannan dariya afili kuma sai yace.
“Toh Moddibo”.
Murmushi Moddibo yayi kana yace.
“Yawwa ai yafi sannan kuma akwai abinci da aka kawo min so naci yamin yawa, kaje ka ɗauka mana sai kaci sabida kada ya lalace!”.
Cikin tsananin mamaki da ganin tsananin karancin Dottijon ya haɗa kai, tare da amsar key ɗin ɗakin da Moddibo ke miƙa masa, cike da yarda aminci yace.
“Ngd Ngd matuƙa Modibbo, Allah ya kara girma ya kare zuriyar Mouley baki ɗaya”.
Gyara tsayuwa yayi tare da girgiza kai yace.
“Amin Ya Allah”.
Gefensa mai gadin yabi kana yace.
“Bari na ɗauka to”.
Ya faɗi tare da nufar cikin, cikin nitsuwa Modibbo yabi bayanshi.
Yana shiga falon ya dauko Warmers din sannan ya fita.
Cike da girmamawa Moddibo yace.
“Toh saida safe Baba”.
Mai gadin na fita yace.
“Allah ya tashe mu lafiya ahuta gajiya”.
Sannan ya fice.
Ahankali Moddibo ya rufe ƙofar falon tare da kashe wutan falon da Ac kana ya nufi Bedroom ɗinsa Kallon AC bedroom din yayi jin kamar yayi mishi yawa ne yasa hannun ya ɗauki rimot ɗin kana ya rage gudunshi.
Kwanciya yayi akan gadon tare da lumshe Idanunsa cikin sauri ya buɗe Idanunsa tare da dafe ƙasan lokaci ɗaya zuciyarsa da jikinsa sunka harba a tare, baki ɗaya ya fahimci wannan muguwar yarinya haka zatayi ta addabar rayuwarsa kenan.
awannan rana dai haka ya kwana cikin wani irin yanayi bacci rabi da rabi yayi.
Washe gari Jumma'a haka ya wani cikin hotel din sai sallan jumma'a da ya fita ana isarwa ya dawo, daga nan ko bakin titin hotel ɗin bai leƙaba.
masallaci ne kaɗai ke fitar dashi.
Hakan yayi kwana biyu yana hutawansa.
Yau Lahadi a bisa tsarin ƙasar Marocco yau ɗin ne forkon sati.
Ƙarfe takwas ya samu Moddibo acikin Company Abba bisa jagorancin Habib.
Yana isa suka fara aiki gadan-gadan aiki ake tako ina babu kama ƙafar yaro domin dama sa hannunsa kawai ake kira da sahalewarsa a matsayinsa na mataimakin MD duk sabbin Injina da aka kawo aka shiga daddasasu da duk wasu gyare-gyare daya kama suka shiga yi domin samun asabunta Company da habaƙashi don har buga atamfofi, Laces, Mayafain laffaya da duk sauran abubuwan buƙata suke so farawa.
Domin shine Company na farko da aka buɗe sa acikin Rabat wanda aka haɓakasa sannan ake inganta kayyakinsu.
Bai bar cikin Company ba sai shida saura kwata kai tsaye masauƙin ya wuce yana isa yayi Hong mai gadi ya buɗe masa gate yana Parking suka gaisa.
Kana ya wuce yayi ciki. kai tsaye Bedroom ya wuce ya watsa ruwa kana ya ɗaura alwala ya fito Masallaci kasancewar ankira Maghariba bai fito ba saida akayi Isha'i kafin ya dawo yaci abinci da Habib ya kawo masa. bayan ya kammala ya ɗauko system ɗin sa ya tura Abba duk yanda sukayi tsare-tsaren abubuwan da kuma hotunan yanda abubuwan suka tafi sosai yayiwa Abba bayanin sannan Abba ya kara masa haske akan sauran abubuwan sai misalin shaɗaya ya tashi yana jin wani irin kasala bini-bini zaiyi miƙa tare da hamma kai tsaye toilet ya nufa ya watsa ruwa.
Anutse ya fito tare da kumtsaawa, kana ya kwanta akan gado tare da lumshe idanunsa tsikar jikinsa na tashi sanyin AC da ƙamshin Roomfreshner da kuma ƙamshin tularensa shi yasake haddasa masa jin wani masifaffen kasala cikin wani irin yanayi ya ƙudundune tamkar yaro lokaci ɗaya bacci yayi awon gaba dashi.
A hankali yake juye-juye yana mai jin da ganin abin kamar a mafarki kamar kuma a zahiri.
Kanshi longwaɓar cikin narkekkiyar murya yace.
“Zakeeh kasheni fa”.
Cikin tsoro tace.
“Ana asped Yah Mu'allim”.
Kai a jujjuya mata tare da cewa.
“Kije keda Allah, kiyi ta dakon zunubi, kina sane dai in har ban yafe mikiba cikin fushin Allah zaki kwana”.
Da sauri ta ƙara kwaɓe fuska, tare da cewa.
“Dan Allah Yah Mu'allim kayi haƙuri ka yafe min, nayi maka al'ƙwari ina nan tafe zanzo gare cikin aminci da rakiyar amintattu a ranar nayi al'ƙawarin gujewa fushin Ubangiji a ranar kada ka ɗaga min ƙafa ka mallaki dukkan ƙudurinka”.
Wani irin mataccen murmushi yayi tare da cewa.
“Yaushe ne ranar?”.
Da sauri tace.
“Nan kusa take”.
Wani irin kallo yayi mata tare da cewa.
“Ranar yaushe ce”.
A hankali tace.
“Raanar larabace ce”.
Cikin wani irin kallo yace.
“Na'amin ce, tunda al'ƙawari kikayi”.
Cikin sauri ta miƙe ta nufi toilet cikin mawuyacin hali ya ɗago idanunsa dake cike da feeling kana muryarsa na rawa yace.
“Pleaassss Hayatieee kada ki saɓa min al'ƙawarin dan idan kika saɓa min a wannan ranar”.
Girgiza kai Khausar tayi cikin kuka da raunin murya tace.
“Bazaka mutuba”.
Amatuƙar galabaici ya yunƙura da niyyar binta tayi saurin rufe kofar toilet.
Akuma dai-dai lokacin ya farka da wani irin azabebben kasala dafe kansa yayi da hannu bibbiyu yayin da Idanunsa suka cika da ruwan hawaye haka ya kwana cikin mawuyacin hali Allah ya sani ya fara ganin yarinyar aljana.
Washegari da sassafe ya tashi yayi wanka kana ya shirya cikin gezner fari ƙal da ya fito da ainihin kyawunsa Anutse ya fito falon hannunsa riƙe da Breafcase a dining area ya tsaya tare da buɗe Warmers din da Habib ya jere Wainar shinkafa ce da miyar taushe sai kuma soyayyan Arish da tea Wainar yaci kana yasha tea bayan ya gama ya mike tare da ɗaukar Breafcase ɗinsa da wayoyinsa da kuma mukullin motarsa kai tsaye Company ya nufa.
Gembila
Aɓangaren Abban sosai hankalinsa ya dan kwanta fahimtar lallai Moddibo yana aiki gadan-gadan bisa tsari da hikima komai na tafiya dai-dai.
Numfashi ya fesar tare da ciro wayarsa yayi dearling number Malam Arɗo bayan ya dauka sun gaisa.
Abba ya sauƙe Ajiyar zuciya kana yace.
“Yau kusan kwana shida kenan da zuwan mu gidan Lamiɗo akan maganar Aliyu da Khausar amma har yau bamuji ya sake neman muba amma tunda mu muke da buƙata yakama muji ta bakinsa”.
Ya gyara zamansa wayar akunnensa kana ya cigaba da cewa.
“Musamman ma da yanzu na tura Aliyu Marocco yana rayuwa shi kaɗai ya kamata ace anyi ƙoƙari anyi batun auren nan saboda kaɗai ci da damuwa zaiyi masa yawa”.
Jinjina kai Malam Arɗo yayi cike da gamsuwa yace.
“Nima abinda nake tunani kenan amma Insha Allahu gobe zamuje da daddare idan Allah ya kaimu rai da Lafiya”.
Ahankali Abba ya jingina bayansa da jikin kujeran kana yace.
“Toh Allah ya kaimu bisa rai da Lafiya”.
Ameen malam Arɗo ya amsa kana suka katse kiran.
*Jauro Yaya*
Hajja Nana ce zaune ta tanƙwashe ƙafafunta Baffa Garga dake gefenta yayi Murmushi yana kallonta yace.
“Addah Nana ɗazu nayi magana da Hammadu”.
Kallonsa tayi tare da kawar da kai gefe tace.
“Ya masa kyau”.
Murmushin Baffa Garga ya faɗaɗa yana kallon yanda tayi kicin-kicin da fuska sassauta murya yayi kana yace In gaishe ki”.
Taɓe baki tayi ba yabo ba fallasa tace.
“Idan ya damu da gaisuwar ai sai yazo inda nake”.
Gyara zama Baffa Garga yayi kana yace.
“Addah Nana ai yace ma zai zo In sha Allahu gobe da safe zaiyi sammako yazo”.
Sassauta fuskarta tayi kana tace.
“Toh Allah ya kawo shi lafiya”.
Ameen Baffa Garga ya amsa tare da ɗauko mata wani hiran.
Washe gari:Asuban fari Baffa Jimeta yayi sammako ya ɗauko hanyar Taraba duk da sammako da yayi sai ƙarfe biyar da rabi ya isa Jauro yaya Aka shiga gaishe-gaishe da tambayar juna koda wasa bai kawowa Hajja Nana maganar Khausar ba sai bayan sallar Isha'i bayan sun ci abinci sun zauna da mahaifiyarsa da kuma Kawunnansa ana hira.
Ahankali ya gyara zamansa kana ya tanƙwashe ƙafafunsa agabanta ya karyar da wuyarsa cikin sanyin murya yace.
“Hajja Nana alfarma nake nema awajenki”.
Kallon second ukun tayi masa kana tace.
“Ni kuma wace alfarma zanyi maka ai da har ina da abinda zaka nemi alfarma awajena Umarni na zaka bi”.
Ahankali ya sassauta muryarsa yace.
“Ai yanzu ma Umarnin ki nake bi Hajja Nana Ni dai temako nema”.
Kallonsa tayi kana tace.
“Taimako akan me?”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da yin ƙasa da kansa yace.
“Taimako akan Marainiyar Allah”.
Baki ta buɗe tare da kallon ƙannenta sai kuma ta kallesa tace.
“Ai kowa ma Maraya ne sannan kowa ma zai iya kasancewa Maraya”.
Kai ya gyaɗa yana kallon yanda take jijjiga ƙafa yace.
“Eh nasani amma akan Khausar nake magana Hajja Nana nazo ne in sake Baki haƙuri akan laifin data aikata sannan muyi mata uzuri matsayinta na yarinya ƙarama”.
Kai ta gyaɗa ba yabo ba fallasa tace.
“Shikenan komai ya wuce tunda Ni ban kaiba Ni kaka ce kun nuna min bani da matsayi sannan banida ikon faɗa aji”.
Da sauri Baffa Jimeta ya kalleta amma baice komai ba ta cigaba da cewa.
“Acikin maganar rayuwar Khausar to ba matsala na cire hannuna ta Auri duk wanda taga dama take so Ni bani da damuwa aciki na janye hannu na tunda haka kuke buƙata”.
Numfashi Baffa Jimeta ya fesar cikin kwantar da murya yace.
“Toh shikenan kiyi haƙuri ki sanya Albarka aciki”.
Taɓe baki tayi kana tace.
“Zansa al'barka ai tunda bazan sa tsinuwa ba Ni dai babu bakina aciki sannan babu batub aurenta da wancan ɗan gaba da fatihan kam”.
Kai ya girgiza cikin sassauta murya yace.
“Mu dai kiyi haƙuri dan Allah kiyi haƙuri kiyi mana fatan alkhairi aciki”.
Ahankali ta kallesa kana tace.
“Toh Allah ya kyauta ya kiyaye gaba dama maganar data kawo ka kenan??”.
Cikin sauri ya girgiza mata kai kana yace.
“A'a bashi bane ya kawoni kewar ki nayi shine nace bari nazo in gaisheki”.
Hararansa tayi tare da kallon sauran ƙannenta tace.
“Oho dai”.
“A'a ba sai kace min Alh nan ba ka kirani da sunana kawai”.
Kai ya gyaɗa yana jinjina karamcinsa Aransa yace yana nan kamar ƙaninsa Ibrahim Youssef Muhammad Mouley. Ibrahim bashi da girman kai sai dai shi Ibrahim yafi wannan dariya afili kuma sai yace.
“Toh Moddibo”.
Murmushi Moddibo yayi kana yace.
“Yawwa ai yafi sannan kuma akwai abinci da aka kawo min so naci yamin yawa, kaje ka ɗauka mana sai kaci sabida kada ya lalace!”.
Cikin tsananin mamaki da ganin tsananin karancin Dottijon ya haɗa kai, tare da amsar key ɗin ɗakin da Moddibo ke miƙa masa, cike da yarda aminci yace.
“Ngd Ngd matuƙa Modibbo, Allah ya kara girma ya kare zuriyar Mouley baki ɗaya”.
Gyara tsayuwa yayi tare da girgiza kai yace.
“Amin Ya Allah”.
Gefensa mai gadin yabi kana yace.
“Bari na ɗauka to”.
Ya faɗi tare da nufar cikin, cikin nitsuwa Modibbo yabi bayanshi.
Yana shiga falon ya dauko Warmers din sannan ya fita.
Cike da girmamawa Moddibo yace.
“Toh saida safe Baba”.
Mai gadin na fita yace.
“Allah ya tashe mu lafiya ahuta gajiya”.
Sannan ya fice.
Ahankali Moddibo ya rufe ƙofar falon tare da kashe wutan falon da Ac kana ya nufi Bedroom ɗinsa Kallon AC bedroom din yayi jin kamar yayi mishi yawa ne yasa hannun ya ɗauki rimot ɗin kana ya rage gudunshi.
Kwanciya yayi akan gadon tare da lumshe Idanunsa cikin sauri ya buɗe Idanunsa tare da dafe ƙasan lokaci ɗaya zuciyarsa da jikinsa sunka harba a tare, baki ɗaya ya fahimci wannan muguwar yarinya haka zatayi ta addabar rayuwarsa kenan.
awannan rana dai haka ya kwana cikin wani irin yanayi bacci rabi da rabi yayi.
Washe gari Jumma'a haka ya wani cikin hotel din sai sallan jumma'a da ya fita ana isarwa ya dawo, daga nan ko bakin titin hotel ɗin bai leƙaba.
masallaci ne kaɗai ke fitar dashi.
Hakan yayi kwana biyu yana hutawansa.
Yau Lahadi a bisa tsarin ƙasar Marocco yau ɗin ne forkon sati.
Ƙarfe takwas ya samu Moddibo acikin Company Abba bisa jagorancin Habib.
Yana isa suka fara aiki gadan-gadan aiki ake tako ina babu kama ƙafar yaro domin dama sa hannunsa kawai ake kira da sahalewarsa a matsayinsa na mataimakin MD duk sabbin Injina da aka kawo aka shiga daddasasu da duk wasu gyare-gyare daya kama suka shiga yi domin samun asabunta Company da habaƙashi don har buga atamfofi, Laces, Mayafain laffaya da duk sauran abubuwan buƙata suke so farawa.
Domin shine Company na farko da aka buɗe sa acikin Rabat wanda aka haɓakasa sannan ake inganta kayyakinsu.
Bai bar cikin Company ba sai shida saura kwata kai tsaye masauƙin ya wuce yana isa yayi Hong mai gadi ya buɗe masa gate yana Parking suka gaisa.
Kana ya wuce yayi ciki. kai tsaye Bedroom ya wuce ya watsa ruwa kana ya ɗaura alwala ya fito Masallaci kasancewar ankira Maghariba bai fito ba saida akayi Isha'i kafin ya dawo yaci abinci da Habib ya kawo masa. bayan ya kammala ya ɗauko system ɗin sa ya tura Abba duk yanda sukayi tsare-tsaren abubuwan da kuma hotunan yanda abubuwan suka tafi sosai yayiwa Abba bayanin sannan Abba ya kara masa haske akan sauran abubuwan sai misalin shaɗaya ya tashi yana jin wani irin kasala bini-bini zaiyi miƙa tare da hamma kai tsaye toilet ya nufa ya watsa ruwa.
Anutse ya fito tare da kumtsaawa, kana ya kwanta akan gado tare da lumshe idanunsa tsikar jikinsa na tashi sanyin AC da ƙamshin Roomfreshner da kuma ƙamshin tularensa shi yasake haddasa masa jin wani masifaffen kasala cikin wani irin yanayi ya ƙudundune tamkar yaro lokaci ɗaya bacci yayi awon gaba dashi.
A hankali yake juye-juye yana mai jin da ganin abin kamar a mafarki kamar kuma a zahiri.
Kanshi longwaɓar cikin narkekkiyar murya yace.
“Zakeeh kasheni fa”.
Cikin tsoro tace.
“Ana asped Yah Mu'allim”.
Kai a jujjuya mata tare da cewa.
“Kije keda Allah, kiyi ta dakon zunubi, kina sane dai in har ban yafe mikiba cikin fushin Allah zaki kwana”.
Da sauri ta ƙara kwaɓe fuska, tare da cewa.
“Dan Allah Yah Mu'allim kayi haƙuri ka yafe min, nayi maka al'ƙwari ina nan tafe zanzo gare cikin aminci da rakiyar amintattu a ranar nayi al'ƙawarin gujewa fushin Ubangiji a ranar kada ka ɗaga min ƙafa ka mallaki dukkan ƙudurinka”.
Wani irin mataccen murmushi yayi tare da cewa.
“Yaushe ne ranar?”.
Da sauri tace.
“Nan kusa take”.
Wani irin kallo yayi mata tare da cewa.
“Ranar yaushe ce”.
A hankali tace.
“Raanar larabace ce”.
Cikin wani irin kallo yace.
“Na'amin ce, tunda al'ƙawari kikayi”.
Cikin sauri ta miƙe ta nufi toilet cikin mawuyacin hali ya ɗago idanunsa dake cike da feeling kana muryarsa na rawa yace.
“Pleaassss Hayatieee kada ki saɓa min al'ƙawarin dan idan kika saɓa min a wannan ranar”.
Girgiza kai Khausar tayi cikin kuka da raunin murya tace.
“Bazaka mutuba”.
Amatuƙar galabaici ya yunƙura da niyyar binta tayi saurin rufe kofar toilet.
Akuma dai-dai lokacin ya farka da wani irin azabebben kasala dafe kansa yayi da hannu bibbiyu yayin da Idanunsa suka cika da ruwan hawaye haka ya kwana cikin mawuyacin hali Allah ya sani ya fara ganin yarinyar aljana.
Washegari da sassafe ya tashi yayi wanka kana ya shirya cikin gezner fari ƙal da ya fito da ainihin kyawunsa Anutse ya fito falon hannunsa riƙe da Breafcase a dining area ya tsaya tare da buɗe Warmers din da Habib ya jere Wainar shinkafa ce da miyar taushe sai kuma soyayyan Arish da tea Wainar yaci kana yasha tea bayan ya gama ya mike tare da ɗaukar Breafcase ɗinsa da wayoyinsa da kuma mukullin motarsa kai tsaye Company ya nufa.
Gembila
Aɓangaren Abban sosai hankalinsa ya dan kwanta fahimtar lallai Moddibo yana aiki gadan-gadan bisa tsari da hikima komai na tafiya dai-dai.
Numfashi ya fesar tare da ciro wayarsa yayi dearling number Malam Arɗo bayan ya dauka sun gaisa.
Abba ya sauƙe Ajiyar zuciya kana yace.
“Yau kusan kwana shida kenan da zuwan mu gidan Lamiɗo akan maganar Aliyu da Khausar amma har yau bamuji ya sake neman muba amma tunda mu muke da buƙata yakama muji ta bakinsa”.
Ya gyara zamansa wayar akunnensa kana ya cigaba da cewa.
“Musamman ma da yanzu na tura Aliyu Marocco yana rayuwa shi kaɗai ya kamata ace anyi ƙoƙari anyi batun auren nan saboda kaɗai ci da damuwa zaiyi masa yawa”.
Jinjina kai Malam Arɗo yayi cike da gamsuwa yace.
“Nima abinda nake tunani kenan amma Insha Allahu gobe zamuje da daddare idan Allah ya kaimu rai da Lafiya”.
Ahankali Abba ya jingina bayansa da jikin kujeran kana yace.
“Toh Allah ya kaimu bisa rai da Lafiya”.
Ameen malam Arɗo ya amsa kana suka katse kiran.
*Jauro Yaya*
Hajja Nana ce zaune ta tanƙwashe ƙafafunta Baffa Garga dake gefenta yayi Murmushi yana kallonta yace.
“Addah Nana ɗazu nayi magana da Hammadu”.
Kallonsa tayi tare da kawar da kai gefe tace.
“Ya masa kyau”.
Murmushin Baffa Garga ya faɗaɗa yana kallon yanda tayi kicin-kicin da fuska sassauta murya yayi kana yace In gaishe ki”.
Taɓe baki tayi ba yabo ba fallasa tace.
“Idan ya damu da gaisuwar ai sai yazo inda nake”.
Gyara zama Baffa Garga yayi kana yace.
“Addah Nana ai yace ma zai zo In sha Allahu gobe da safe zaiyi sammako yazo”.
Sassauta fuskarta tayi kana tace.
“Toh Allah ya kawo shi lafiya”.
Ameen Baffa Garga ya amsa tare da ɗauko mata wani hiran.
Washe gari:Asuban fari Baffa Jimeta yayi sammako ya ɗauko hanyar Taraba duk da sammako da yayi sai ƙarfe biyar da rabi ya isa Jauro yaya Aka shiga gaishe-gaishe da tambayar juna koda wasa bai kawowa Hajja Nana maganar Khausar ba sai bayan sallar Isha'i bayan sun ci abinci sun zauna da mahaifiyarsa da kuma Kawunnansa ana hira.
Ahankali ya gyara zamansa kana ya tanƙwashe ƙafafunsa agabanta ya karyar da wuyarsa cikin sanyin murya yace.
“Hajja Nana alfarma nake nema awajenki”.
Kallon second ukun tayi masa kana tace.
“Ni kuma wace alfarma zanyi maka ai da har ina da abinda zaka nemi alfarma awajena Umarni na zaka bi”.
Ahankali ya sassauta muryarsa yace.
“Ai yanzu ma Umarnin ki nake bi Hajja Nana Ni dai temako nema”.
Kallonsa tayi kana tace.
“Taimako akan me?”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da yin ƙasa da kansa yace.
“Taimako akan Marainiyar Allah”.
Baki ta buɗe tare da kallon ƙannenta sai kuma ta kallesa tace.
“Ai kowa ma Maraya ne sannan kowa ma zai iya kasancewa Maraya”.
Kai ya gyaɗa yana kallon yanda take jijjiga ƙafa yace.
“Eh nasani amma akan Khausar nake magana Hajja Nana nazo ne in sake Baki haƙuri akan laifin data aikata sannan muyi mata uzuri matsayinta na yarinya ƙarama”.
Kai ta gyaɗa ba yabo ba fallasa tace.
“Shikenan komai ya wuce tunda Ni ban kaiba Ni kaka ce kun nuna min bani da matsayi sannan banida ikon faɗa aji”.
Da sauri Baffa Jimeta ya kalleta amma baice komai ba ta cigaba da cewa.
“Acikin maganar rayuwar Khausar to ba matsala na cire hannuna ta Auri duk wanda taga dama take so Ni bani da damuwa aciki na janye hannu na tunda haka kuke buƙata”.
Numfashi Baffa Jimeta ya fesar cikin kwantar da murya yace.
“Toh shikenan kiyi haƙuri ki sanya Albarka aciki”.
Taɓe baki tayi kana tace.
“Zansa al'barka ai tunda bazan sa tsinuwa ba Ni dai babu bakina aciki sannan babu batub aurenta da wancan ɗan gaba da fatihan kam”.
Kai ya girgiza cikin sassauta murya yace.
“Mu dai kiyi haƙuri dan Allah kiyi haƙuri kiyi mana fatan alkhairi aciki”.
Ahankali ta kallesa kana tace.
“Toh Allah ya kyauta ya kiyaye gaba dama maganar data kawo ka kenan??”.
Cikin sauri ya girgiza mata kai kana yace.
“A'a bashi bane ya kawoni kewar ki nayi shine nace bari nazo in gaisheki”.
Hararansa tayi tare da kallon sauran ƙannenta tace.
“Oho dai”.