Sashe 68
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A ɓanƙaren su Modibbo kuwa, Sheiyk Jabeer ne tare Modibbo sai Jabeer bin Jabeer cikin kulawa Modibbo yace.
“Sheiykh yau yau kuma zaku koma?”.
Gyaran murya Sheikh Jabeer yayi tare da cewa.
“In Allah kuwa yanzuma zamu tafi airport dama kafin mu tafi masallaci nayi sallama da kowa na Fada harma da Didinku munyi sallama.
Tafiyar ce ta gaggawa ta sameni zan koma ne saboda gobe da yamma muna da zama da ƙungiyar *MI YETTI ALLAH* Akam matsalolin Garkuwa da mutane ƙasarmu ke fuskanta.
Toh yadda ake maida akalar zargin kan cewa Fulani ne keda alhaƙin hakanne yasa ƙungiyar *TABITAL POOLAKU* shiga mgnar da keɓance ƴaƴanta Fulani da wonkesu daga zargin da ake musu domin suma fulanin basu tsiraba, anayi musu wannan zalumcin su a ƙara da kashesu ma”.
Cikin sauƙe nannauyan numfashi Modibbo yace.
“Gsky wannan ƙudurine mai kyau, domin abune daya addabi ƙasarmu, kaga wala Allah cikin haka a gano masu aikata hakan”.
Cikin kulawa Sheiykh yace.
“In sha Allah kuwa, domin fulanin zamu wakilta mu naɗasu aikin bamu rahoton duk abinda ke gudana cikin dajukan za mu rabasu ko wanne state na Nigeria”.
Sai kuma suka kalli Jabeer bin Jabeer dake cewa.
“Musamman Zamfara Sokoto Katsina abun yafi tsamari a can”.
Moddibo ne ya ɗan fesar da numfashin mai zafi kana yace.
“Ni kuwa ina so a ruɓanya masu binciken Taraba yankin Gembulan domin anayi musu illa sosai, a sanadin su na rasa J na”.
Sheykh ne ya ɗan kali agogo dake hannunsa tare da cewa.
“Eh nima da batun Jameel da kayi mana bayani na kuduri aniyar in sha Allah, sai na gano waɗanda suka yi masa wannan kisan gillan, in ban mantaba kace min akwai wacce taga mota bibiyarsu kuma har ta ɗauki number'n ko?”. Da sauri Modibbo yace.
“Eh Khausar ce”.
Cikin samun cikekken yaƙini kan binciken Sheykh yace.
“Toh ba matsala idan kun nitsu, ka nemi min cikekken bayanin a wurinta, sai ka tura min komai, in Allah ya yarda jininshi bazai tafi a banzaba”.
Kai ya jinjina tare da cewa.
“In sha Allah kuwa”.
Daga nan sukayi sallama, Abualeey da kanshi yayiwa surkin nashi da ƙanin matarsa rakiya zuwa Airport, bai dawoba saida jirginsu ya tashi.
Acan ɓangaren su Khausar kuwa zaune take kan sallayar tun bayan data idar da sallar Azahar bata motsa ba.
Innayi dake gefe ta saki murmushi tare da faɗin.
“Kai Alhamdulillah naji daɗin nagartar Moddibo ina farin ciki da hakan”.
Kai Ummi dake gefenta ta jinjina kana tace.
“Ai dai kam Alhamdulillah”.
Daga haka suka cigaba da hira wanda mafi yawa akan Moddibo ne...
Acan ɓangaren Hajiya Bunayya kuwa zaune take a bedroom ita kaɗai yayin da Asiya ke toilet tana wanka.
Hajiya Bunayya kuwa wayane maƙale a kunnenta tana magana da Amina dogon tsaki taja tare da faɗin.
“Ke dai Amina bari wallahi dana san haka daular nan take da mu mukayi sihiri kika Auri Moddibo”.
Amina dake zaune acikin wani ƙaton falo na al'farma a Abuja tayi murmushi tare da faɗin.
“Umma kada ki damu nan ma wallahi muna cikin daula kinga gidan da aka kama nin kuwa, dan dai baki zo kinga gidan da aka kawo ni bane gidane mai masifar kyau na nunawa sa'afa”.
Sai kuma ta juya idanunta tare da kallon mashshurin falon nata kana ta cigaba da cewa.
“Kinga manyan falona guda biyu da 3bedroom atsakiyar birnin Abuja fa muke inda muke ma ai alhamdulillah kuma kin manta muma zamu tafi Indi'a ne kwanan nan da Uncle Naseer”.
Dogon tsaki Hajiya Bunayya taja kana tace.
“Ke bakiga daular dake cikin nan bane shiyasa kike faɗin hakan”.
Murmushi Amina tayi tare da faɗin.
“Umma kema fa bakisan daular da nake ciki bane ki kwantar da hankalin ki in kin dawo kinzo zaki sha mmaki”.
Cikin gaskata wa Amina ta cigaba da kwantar wa da mahaifiyarta hankali kana ta ɗaura da faɗin.
“Umma kada fa ki manta muma Indi'a zamu tare kuma Indi'a ma ai tafi Morocco sanuwa da suna”.
Kai Hajiya Bunayya ta girgiza kana tace.
“Hmmm Amina kenan ta yaro kyau take bata ƙarko, abine da baki gani ba, duk labarin da zan baki bazaki gane bane irin cigaba, da nasara, wadatar da Khausar ta riska awannan masarauta ya wuce zatonki”.
Sai kuma ta ha ɗiye wani yawu mai masifar ɗaci kana ta cigaba da cewa.
“Bazaki taɓa fahimtar abinda nake faɗa ba har sai idonki ya gane miki.
Yoh Naseer da ko Sarkin Tasha Uban sa bai taɓa mulka ba, ina za'a haɗashi da Modibbo, kina sane da cewa Khausar kuwa mijinta shine Yarima mai jiran gadon mulkin Ƙasar Morocco gaba ɗayanta fa, sannan kuma shine babban ɗa Namiji awajen Mahaifinsa”.
Amina dake zaune ta dafe ƙirji cike da ƙyashi da hasadar jin matsayi da kuma nasaran da Khausar ta samu.
Hajiya Bunayya kam cikin ƙunan zuciya da tarin hassada ta cigaba da faɗin.
“Wannan tsinanniyar tsohuwar Innayi ta cucemu data ɓoye mana wannan al'amari nasarar Modibbo da mun san da wannan nasaba da yake dashi haka ai wallahi ko zan tafi tsirara ne wlh sai kin Auri Moddibo”.
Zazzafan Ajiyar zuciya Amina ta sauƙe kana tace.
“Umma ke kam kada ki damu”.
Kai Hajiya Bunayya ta girgiza ji take kamar ta ɗaura hannu aka tayi ta zunduma ihu cikin damuwa tace.
“Ya bazan damu ba Amina dole in damu gaba ɗaya hankalina ya tashi baƙin ba, yanda ban samu ba suma su rasa Wallahi, duk yanda zanyi Amina nayi miki al'ƙawarin sai na raba Auren Khausar da Moddibo ko ana Hamaza ha mata.
In dai dawo Nigeria ne kawai yafi wuya”.
Cikin sauƙe numfashi Amina tace.
“Gaskiya dai nima yanda kike zuzuta wannan cigaban nata, da dai ta wuceni gwara a kaso Auren nata ta dawo gida ta zauna”.
Yamutse fuska tayi tare da gyara zamanta kana ta cigaba da cewa.
“Ƴar banza agola kawai tazo tafi ƴaƴan masu gida nasara”.
Ƙwaffa Hajiya Bunayya tayi kana tace.
“Ke dai bari”.
Dai dai lokacin da Asiya ta fito daga wanka kallonta tayi tare da girgiza kai cikin yanayin sanyinta tace.
“Hmmmm Allah ya kyauta”.
Alalace ta kalleta tare da faɗin.
“Toh shegiya mai baƙin hali meye?
Ƴar masu matacciyar zuciya da bakisan abinda yake miki ciwo ba sai wani yaƙe baki kike kina murmushi adole kinga nasarar wani”.
Tana zama gaban dreesing mirror tace.
“Umma idan har bakayi baƙin ciki da nasarar wani ba kaima Allah zai kawo maka naka narasan”.
Ahantare Hajiya Bunayya ta harareta tare da cewa.
“Dalla can rufe min baki,Ki ɓace min daga ɗaki”.
Kai ta gyaɗa tare da ficewa daga dakin kasancewar tasa kayanta kai tsaye ɗakin su Khausar ta nufa...
Acan ɓangaren Moddibo kuwa bayan sun Sheykh Jabeer sun tafi. suka cigaba da gaisawa da Manyan baƙi.
Har aka kira La'asar bayan an idar da sallar La'asar baki ɗaya baƙi suka tafi anci ansha wasu irin abinci na alfarma aka dafa wanda ma'aikatan manyan restaurant aka ɗebo sukayi girkin gargajiya dana zamani domin afita kunya.
kuma Alhamdulillah kwalliya ta biya kuɗin sabulu.
Moddibo kuwa gaba ɗaya wunin yau ɗin duk abinda yake Khausar ce ke faɗo masa arai da Zaran ya lumshe Idanunsa zai tuna sanda ya rungumeta yana budewa kuwa lokacin da yake wanke mata hannu acikin Madarane ke masa gizo duk wani abu da yake dauriya kawai yake.
Yayin da wani ɓangare na zuciyarsa ya tafi ga halin da Asma'u ke ciki kasancewar har suma tayi a daren jiya kana ko bayan barinsa sashen da sukenma bata cikin nutsuwarta, tun safe yaso zuwa dubata amma bai samu ba saboda hidindimu da suka yi masa yawa...
Acan Falon su Khausar kuwa suka zaune Jakadiya ta shigo bayan sun gaisa ta kalli Innayi tare da cewa.
“Innayi Didi na buƙatar ku baki ɗaya asashenta amma banda Khausar sannan abarta da mutum ɗaya kada ta zauna ita kaɗai”.
Kai Innayi ta jinjina tare da cewa.
“Toh ba damuwa sai abarta da Hajja Nana”.
Ta ida maganar tare da miƙewa ta nufi ƙofa yayin da Hajiya Bunayya,Aunty Ruƙayya, Aunty Hawwa, Aunty Hajara Asiya, Dije suka mara mata baya.
Kai tsaye suka nufi sashen Didi bakinsu ɗauke da sallama suka shiga tangamemen Falon suna shiga idanunsu ya sauƙa akan Wasu Mashahuran Akwatuna set biyar ko wannen kalansa da ban.
Lalla Khadijah ne ta ɗaga kai tare da kallon Innayi kana tace.
“Ku shigo ku zauna mana”.
Murmushi Innayi tayi kana suka shiga suka zazzauna akan lumtsa-lumtsan kujerun na al'farma.
Ɗaya daga cikinsu ne Yayar Didi wacce ta kasance ƴar farinsu ce Mai suna Afreen wacce kira da Ashshe matsawa tayi suka gaisa kana cikin sakin fuska tace.
“Toh Alhamdulillah ga lefe nan mun gama haɗawa na.
Amaryanmu so mun kira kune kuzo ku gani in Sha Allah za'a bawa Hadimai su kaishi Side ɗin da zasu zauna ne”.
Cike da tarin farin ciki Innayi ke kallon Set ɗin akwatunan kana tace.
“Masha Allah Alhamdulillah”.
Ummi kuwa cikin yanayin farin ciki tace.
“Kai masha Allah wannan duka lefene!?”.
Lokaci ɗaya Hajiya Bunayya ta nemi ƴar nutsuwarta ta rasa atake yanayin fuskarta ya rikiɗe afili zuwa hassada da ƙyashi ta kasa ɓoye baƙin cikinta.
Cikin fusata taja wani dogon tsaki tare da sauƙe numfashi wanda yaja hankali da yawa daga cikin mutanen falon suka kalleta.
Asiya dake gefenta tayi saurin dafa kafaɗarta ganin yanda ake kallonsu yasa tace.
“Umma lafiya?”.
Kai ta gyaɗa tare da yamutse fuska kana tace.
“Ƙirjina ne yake ciwo sai to kareni yake”.
A yatsine Lalla Hafsat ta kalleta tare da cewa.
“Ok ba matsala bari na kira Dr Jameel yazo ya duba ki da jiki sai ya baki magani”.
Ta ƙare mgnar a yaysine dan har ga Allah matar bata konta mata a raiba....
Littafin SAKAYYAH dai na kuɗi ki biya ki karanta cikin Aminci.
By
*GARKUWAR MARUBUTA**SAKAYYAH book 2... Page 19*
Na
*Aysha Aliyu Garkuwa*
“Sheiykh yau yau kuma zaku koma?”.
Gyaran murya Sheikh Jabeer yayi tare da cewa.
“In Allah kuwa yanzuma zamu tafi airport dama kafin mu tafi masallaci nayi sallama da kowa na Fada harma da Didinku munyi sallama.
Tafiyar ce ta gaggawa ta sameni zan koma ne saboda gobe da yamma muna da zama da ƙungiyar *MI YETTI ALLAH* Akam matsalolin Garkuwa da mutane ƙasarmu ke fuskanta.
Toh yadda ake maida akalar zargin kan cewa Fulani ne keda alhaƙin hakanne yasa ƙungiyar *TABITAL POOLAKU* shiga mgnar da keɓance ƴaƴanta Fulani da wonkesu daga zargin da ake musu domin suma fulanin basu tsiraba, anayi musu wannan zalumcin su a ƙara da kashesu ma”.
Cikin sauƙe nannauyan numfashi Modibbo yace.
“Gsky wannan ƙudurine mai kyau, domin abune daya addabi ƙasarmu, kaga wala Allah cikin haka a gano masu aikata hakan”.
Cikin kulawa Sheiykh yace.
“In sha Allah kuwa, domin fulanin zamu wakilta mu naɗasu aikin bamu rahoton duk abinda ke gudana cikin dajukan za mu rabasu ko wanne state na Nigeria”.
Sai kuma suka kalli Jabeer bin Jabeer dake cewa.
“Musamman Zamfara Sokoto Katsina abun yafi tsamari a can”.
Moddibo ne ya ɗan fesar da numfashin mai zafi kana yace.
“Ni kuwa ina so a ruɓanya masu binciken Taraba yankin Gembulan domin anayi musu illa sosai, a sanadin su na rasa J na”.
Sheykh ne ya ɗan kali agogo dake hannunsa tare da cewa.
“Eh nima da batun Jameel da kayi mana bayani na kuduri aniyar in sha Allah, sai na gano waɗanda suka yi masa wannan kisan gillan, in ban mantaba kace min akwai wacce taga mota bibiyarsu kuma har ta ɗauki number'n ko?”. Da sauri Modibbo yace.
“Eh Khausar ce”.
Cikin samun cikekken yaƙini kan binciken Sheykh yace.
“Toh ba matsala idan kun nitsu, ka nemi min cikekken bayanin a wurinta, sai ka tura min komai, in Allah ya yarda jininshi bazai tafi a banzaba”.
Kai ya jinjina tare da cewa.
“In sha Allah kuwa”.
Daga nan sukayi sallama, Abualeey da kanshi yayiwa surkin nashi da ƙanin matarsa rakiya zuwa Airport, bai dawoba saida jirginsu ya tashi.
Acan ɓangaren su Khausar kuwa zaune take kan sallayar tun bayan data idar da sallar Azahar bata motsa ba.
Innayi dake gefe ta saki murmushi tare da faɗin.
“Kai Alhamdulillah naji daɗin nagartar Moddibo ina farin ciki da hakan”.
Kai Ummi dake gefenta ta jinjina kana tace.
“Ai dai kam Alhamdulillah”.
Daga haka suka cigaba da hira wanda mafi yawa akan Moddibo ne...
Acan ɓangaren Hajiya Bunayya kuwa zaune take a bedroom ita kaɗai yayin da Asiya ke toilet tana wanka.
Hajiya Bunayya kuwa wayane maƙale a kunnenta tana magana da Amina dogon tsaki taja tare da faɗin.
“Ke dai Amina bari wallahi dana san haka daular nan take da mu mukayi sihiri kika Auri Moddibo”.
Amina dake zaune acikin wani ƙaton falo na al'farma a Abuja tayi murmushi tare da faɗin.
“Umma kada ki damu nan ma wallahi muna cikin daula kinga gidan da aka kama nin kuwa, dan dai baki zo kinga gidan da aka kawo ni bane gidane mai masifar kyau na nunawa sa'afa”.
Sai kuma ta juya idanunta tare da kallon mashshurin falon nata kana ta cigaba da cewa.
“Kinga manyan falona guda biyu da 3bedroom atsakiyar birnin Abuja fa muke inda muke ma ai alhamdulillah kuma kin manta muma zamu tafi Indi'a ne kwanan nan da Uncle Naseer”.
Dogon tsaki Hajiya Bunayya taja kana tace.
“Ke bakiga daular dake cikin nan bane shiyasa kike faɗin hakan”.
Murmushi Amina tayi tare da faɗin.
“Umma kema fa bakisan daular da nake ciki bane ki kwantar da hankalin ki in kin dawo kinzo zaki sha mmaki”.
Cikin gaskata wa Amina ta cigaba da kwantar wa da mahaifiyarta hankali kana ta ɗaura da faɗin.
“Umma kada fa ki manta muma Indi'a zamu tare kuma Indi'a ma ai tafi Morocco sanuwa da suna”.
Kai Hajiya Bunayya ta girgiza kana tace.
“Hmmm Amina kenan ta yaro kyau take bata ƙarko, abine da baki gani ba, duk labarin da zan baki bazaki gane bane irin cigaba, da nasara, wadatar da Khausar ta riska awannan masarauta ya wuce zatonki”.
Sai kuma ta ha ɗiye wani yawu mai masifar ɗaci kana ta cigaba da cewa.
“Bazaki taɓa fahimtar abinda nake faɗa ba har sai idonki ya gane miki.
Yoh Naseer da ko Sarkin Tasha Uban sa bai taɓa mulka ba, ina za'a haɗashi da Modibbo, kina sane da cewa Khausar kuwa mijinta shine Yarima mai jiran gadon mulkin Ƙasar Morocco gaba ɗayanta fa, sannan kuma shine babban ɗa Namiji awajen Mahaifinsa”.
Amina dake zaune ta dafe ƙirji cike da ƙyashi da hasadar jin matsayi da kuma nasaran da Khausar ta samu.
Hajiya Bunayya kam cikin ƙunan zuciya da tarin hassada ta cigaba da faɗin.
“Wannan tsinanniyar tsohuwar Innayi ta cucemu data ɓoye mana wannan al'amari nasarar Modibbo da mun san da wannan nasaba da yake dashi haka ai wallahi ko zan tafi tsirara ne wlh sai kin Auri Moddibo”.
Zazzafan Ajiyar zuciya Amina ta sauƙe kana tace.
“Umma ke kam kada ki damu”.
Kai Hajiya Bunayya ta girgiza ji take kamar ta ɗaura hannu aka tayi ta zunduma ihu cikin damuwa tace.
“Ya bazan damu ba Amina dole in damu gaba ɗaya hankalina ya tashi baƙin ba, yanda ban samu ba suma su rasa Wallahi, duk yanda zanyi Amina nayi miki al'ƙawarin sai na raba Auren Khausar da Moddibo ko ana Hamaza ha mata.
In dai dawo Nigeria ne kawai yafi wuya”.
Cikin sauƙe numfashi Amina tace.
“Gaskiya dai nima yanda kike zuzuta wannan cigaban nata, da dai ta wuceni gwara a kaso Auren nata ta dawo gida ta zauna”.
Yamutse fuska tayi tare da gyara zamanta kana ta cigaba da cewa.
“Ƴar banza agola kawai tazo tafi ƴaƴan masu gida nasara”.
Ƙwaffa Hajiya Bunayya tayi kana tace.
“Ke dai bari”.
Dai dai lokacin da Asiya ta fito daga wanka kallonta tayi tare da girgiza kai cikin yanayin sanyinta tace.
“Hmmmm Allah ya kyauta”.
Alalace ta kalleta tare da faɗin.
“Toh shegiya mai baƙin hali meye?
Ƴar masu matacciyar zuciya da bakisan abinda yake miki ciwo ba sai wani yaƙe baki kike kina murmushi adole kinga nasarar wani”.
Tana zama gaban dreesing mirror tace.
“Umma idan har bakayi baƙin ciki da nasarar wani ba kaima Allah zai kawo maka naka narasan”.
Ahantare Hajiya Bunayya ta harareta tare da cewa.
“Dalla can rufe min baki,Ki ɓace min daga ɗaki”.
Kai ta gyaɗa tare da ficewa daga dakin kasancewar tasa kayanta kai tsaye ɗakin su Khausar ta nufa...
Acan ɓangaren Moddibo kuwa bayan sun Sheykh Jabeer sun tafi. suka cigaba da gaisawa da Manyan baƙi.
Har aka kira La'asar bayan an idar da sallar La'asar baki ɗaya baƙi suka tafi anci ansha wasu irin abinci na alfarma aka dafa wanda ma'aikatan manyan restaurant aka ɗebo sukayi girkin gargajiya dana zamani domin afita kunya.
kuma Alhamdulillah kwalliya ta biya kuɗin sabulu.
Moddibo kuwa gaba ɗaya wunin yau ɗin duk abinda yake Khausar ce ke faɗo masa arai da Zaran ya lumshe Idanunsa zai tuna sanda ya rungumeta yana budewa kuwa lokacin da yake wanke mata hannu acikin Madarane ke masa gizo duk wani abu da yake dauriya kawai yake.
Yayin da wani ɓangare na zuciyarsa ya tafi ga halin da Asma'u ke ciki kasancewar har suma tayi a daren jiya kana ko bayan barinsa sashen da sukenma bata cikin nutsuwarta, tun safe yaso zuwa dubata amma bai samu ba saboda hidindimu da suka yi masa yawa...
Acan Falon su Khausar kuwa suka zaune Jakadiya ta shigo bayan sun gaisa ta kalli Innayi tare da cewa.
“Innayi Didi na buƙatar ku baki ɗaya asashenta amma banda Khausar sannan abarta da mutum ɗaya kada ta zauna ita kaɗai”.
Kai Innayi ta jinjina tare da cewa.
“Toh ba damuwa sai abarta da Hajja Nana”.
Ta ida maganar tare da miƙewa ta nufi ƙofa yayin da Hajiya Bunayya,Aunty Ruƙayya, Aunty Hawwa, Aunty Hajara Asiya, Dije suka mara mata baya.
Kai tsaye suka nufi sashen Didi bakinsu ɗauke da sallama suka shiga tangamemen Falon suna shiga idanunsu ya sauƙa akan Wasu Mashahuran Akwatuna set biyar ko wannen kalansa da ban.
Lalla Khadijah ne ta ɗaga kai tare da kallon Innayi kana tace.
“Ku shigo ku zauna mana”.
Murmushi Innayi tayi kana suka shiga suka zazzauna akan lumtsa-lumtsan kujerun na al'farma.
Ɗaya daga cikinsu ne Yayar Didi wacce ta kasance ƴar farinsu ce Mai suna Afreen wacce kira da Ashshe matsawa tayi suka gaisa kana cikin sakin fuska tace.
“Toh Alhamdulillah ga lefe nan mun gama haɗawa na.
Amaryanmu so mun kira kune kuzo ku gani in Sha Allah za'a bawa Hadimai su kaishi Side ɗin da zasu zauna ne”.
Cike da tarin farin ciki Innayi ke kallon Set ɗin akwatunan kana tace.
“Masha Allah Alhamdulillah”.
Ummi kuwa cikin yanayin farin ciki tace.
“Kai masha Allah wannan duka lefene!?”.
Lokaci ɗaya Hajiya Bunayya ta nemi ƴar nutsuwarta ta rasa atake yanayin fuskarta ya rikiɗe afili zuwa hassada da ƙyashi ta kasa ɓoye baƙin cikinta.
Cikin fusata taja wani dogon tsaki tare da sauƙe numfashi wanda yaja hankali da yawa daga cikin mutanen falon suka kalleta.
Asiya dake gefenta tayi saurin dafa kafaɗarta ganin yanda ake kallonsu yasa tace.
“Umma lafiya?”.
Kai ta gyaɗa tare da yamutse fuska kana tace.
“Ƙirjina ne yake ciwo sai to kareni yake”.
A yatsine Lalla Hafsat ta kalleta tare da cewa.
“Ok ba matsala bari na kira Dr Jameel yazo ya duba ki da jiki sai ya baki magani”.
Ta ƙare mgnar a yaysine dan har ga Allah matar bata konta mata a raiba....
Littafin SAKAYYAH dai na kuɗi ki biya ki karanta cikin Aminci.
By
*GARKUWAR MARUBUTA**SAKAYYAH book 2... Page 19*
Na
*Aysha Aliyu Garkuwa*