Sashe 43
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Suna na isa gidan Abban ta samu Malam Arɗo bayan sun gaisa Malam Arɗo yace.
“Toh jiya da daddare Lamiɗo ya kirani yace biki za'a haɗa dana ƴar wajensa kuma sunce Jumma'a na sama nema suke so aɗaura auren kunga yau saura kwana takwas nema, toh yace za ahaɗa dana Khausar”.
Jinjina kai innayi keyi cike da gamsuwa Malam Arɗo ya cigaba da cewa. “Sannan mun gama tattaunawa da Abban Jameel akan ayi kawai agama tunda dama Jameelu yayi ta jaddadawa cewa ayi ƙoƙari ayi shi cikin ƙanƙanin lokaci”.
Gyara zama Ummi tayi kana tace.
“Sosai ma ayi kokari ayi haka shiya dace”.
Gyara zama Malam Arɗo yayi kana yace .
“Sannan Alh Bashir yace kada ayi masa batun Auren”.
Kai Ummi ta gyaɗa cikin gamsuwa, shi kuwa Abban Jameel gyaran murya yayi tare da cewa.
“Innayi kada a faɗa masa fa, dan so nake muyi mishi ba zata”.
Cikin gamsuwa Innayi ta jinjina kai tare da cewa.
“Ai kuwa bazata kam suna da yawa kuma ɗin kanku akwai bazatar da zan muku.
Tunda in an ɗaura auren kai mishi ita za'ayi ko?".
Da sauri Abba yace.
“Ni zan kai mishi ita”.
Murmushi Innayi tayi tare da cewa.
“A'a kada ka damu a gayawa dangin amarya su shirya yan rakiyar amarya da basu gaza goma”.
Da sauri Ummi ta juyo ta kalleta tare da cewa.
“A'a Innayi bafa ƙasar nan bane, har Marocco nefa, ya za'ayi ace har mutun goma ai ɗawainiyar zatayi yawa, wurin sauƙesu ma ai jidali ne”.
Cikin sauri Malam Arɗo yace sosai ma kuwa.
Abba kuwa ido kawai ya zuba musu.
Ita kuwa innayi gyara zama tayi cike da yaƙini da kuma tabbaci tace.
“Kada ki damu Ummin Jameel, ai tuwon girma miyansa nama, kuma in dai masauƙine koda Gambulan baki ɗaya zamuje bazata rasa masauƙiba. Kana kema zakije Asma'u, Abban Jameel Malam Arɗo, dama Lamiɗon kansa zaije”.
Murmushi mai cike da nazari Abban Jameel yayi tare da tuno abubuwan da Jameel ya gaya mishi akan tarihin Modibbo da yace Innayi ta bashi.
Cikin gamsuwa yace.
Kada ki damu Fatima a gayawa mahaifiyar Khausar a samu mutun goma daga gefen dangin kausar na uwa da uba da ni kuwa zan gayawa Lamiɗo”.
Kai kawai Ummi ta iya gyaɗa musu, domin abin ya bata mmki tunda Modibbo fa ya gaya mata kuɗin tickets insa na business class 1,303,000 suku tum toh fisa bilillahi wannan kudi ai yawa garesu ace kusan mutun goma.
Jin Malam Arɗo yace.
“Ai akwai economic tickets, kudinsa bazai kai hakaba ni dashi nake amfani duk inda nake zuwa”.
Jin hakane yasa ta gane ashe mgnar zuci da tayi ya fito fili.
Innayi kuwa kai ta jinjina tare da cewa.
“In sha Allah dai ba abinda zai gagara”.
Abba kuwa cikin nitsuwa yace.
“Kayan lefenta kuwa nasa matar aminina Dr Ahmad zata haɗa komai, wata ƙil ya iso kafin muje".
Da sauri innayi tace.
“A'a a barsu sai munje can mu haɗa ai tunda zamuje da zuriyarta duk zasu gani”.
Da sauri Ummu tace.
“Ayi haka kuwa innayi a tafi da amarya ba lefe, ai za'ayi ta surutai”.
Cikin jinjina kai innayi tace.
“Barsu suyi lokacin sune”.
Nan suka ci-gaba da tattaunawa yadda komai zai wakana.
Tun daga wannan rana suka fara shirye-shiryen biki babu kama ƙafan Yaro.
Aranan da daddare aka kawo kayan Auren Amina kaya sunyi kyau sosai su Hajiya Lami ne suka tarbi kayan Auren Bayan anwatse Amina ta kalli Samira dake gefenta tayi tagumi wacce baki ɗaya ta rame ta sauya ta dawo shiru-shiru.
Kallon Samira tayi kana tace.
“Samira wallahi da gaske kin fara wari dan ina jin warin”.
Cikin zubda hawaye Samira ta kalleta Muryanta na rawa tace.
“Allah Amina kina ji ko?”.
Kai Amina ta gyaɗa cikin gaskiya da tace.
“Wallahi Ina ji Amina sai kinji kamar warin Baragurbin ƙwai”.
Cikin raunin murya tace.
“Na sani dole za aji warin kawai Mommy na Idan na faɗa mata sai tace bata ji amma nasan dole za aji warin”.
Yamutse fuska Amina tayi kana tace.
“Gaskiya dai kam kina warin Baragurbin ƙwai wallahi ki dage ki koma wajen Boka ya baki magani”.
Kai Samira ta Girgiza.
Dai-dai lokacin Hajiya Bunayya ta shigo Harara ta watsawa Amina tace.
“Ke dai Wallahi Amina baki da hankali amaimakon ki kwantar mata da hankali sai ki ƙara tayar mata”.
Baki ta tura tare da kallon Hajiya Bunayya tace.
“Mommy wannan ba maganar tada hankali bane gaskiya ne kawai ku koma wajen Boka Kar'uzu yayi ƙoƙarin nemo mata magani”.
lokacin kuma Hajiya Lami ta fito daga toilet dake Bedroom din tace.
“Boka Kar'uzu har yau bai dawo ba daga tafiyar da yayi nima jira nake ya dawo Inje ko shekara jiya naje ban same shiba.
Cikin rauni Samira ta kallesu muryanta na rawa tace.
“Ni dai da an haƙura da neman Magani awajen Boka Kar'uzu kawai anema min maganin Islamic medicine ko Allah zaisa adace”.
Atare Hajiya Bunayya da Hajiya Lami suka ce me kike faɗa haka ki dai bari asake gwadawa agani.
Shiru tayi ba tare da tace musu uffan ba.
*Morocco*
Motar Moddibo ce tsaye abakin Mouley Yussef Hospital Rabat kusan kullum sai yazo amma da zaran security dake bakin gate din ya ga shine zai ki buɗe masa yau kwana biyu kenan yana sintirin zuwa cikin sanyi jiki ya juya ya koma gida yana so ya faɗawa Abba to amma ta ina zai fara faɗa masa zaice Jameel ɗinsa ko kuma yaya zuwa wannan lokacin hankalinsa ya gama tashi ya rasa shin wani irin tunani zaiyi cikin wannan tunanin ya koma gida.
Washe gari: alhamis haka ya tashi cikin matsanancin kasala saboda yanda aka kwana ana zuga ruwan sama gari yayi sanyi cikin damuwa da ciwon kasala da jin bugun zuciya ya kwana adaddafe ya tashi ya shirya kai tsaye Company ya nufa ya dudduba aikin da akayi zuwa yanzu gaba ɗaya angama daddasa Injinan da za ayi aiki dasu alissafinsu Insha Allah ranan Monday za afara bubbuga Nauikan, Abaya, Laffa, Jallabiya, Sallayu, blankets, Jakankuna, takalma za a cigaba da sarrafa kaya.
Kai tsaye motarsa ya shiga har ya nufi gida sai kuma ya sinci kansa da juya alamar motarsa kai tsaye Mouley Youssef Hospital Rabat ya nufa yana isa bakin gate ɗin dai-dai lokacin da security ya buɗe wa wata mota gate wannan damar Moddibo ya samu yayi saurin cinna hancin motarsa ciki.
Yana isa yayi Parking security na ganinsa yace.
“You again”.
Iya abinda ya iya faɗa kenan domin haiba da ƙwarjinsa yasa ba zai iya korinsa ba cike da nutsuwa Moddibo ya nufa cikin reception duk ido mutanen da Norses ɗin suka zuba masa suna kallon baiwar kyau nutsuwa da kamala da kuma ƙwarjini da yake dashi.
Kai tsaye Office ɗin Dr Jameel ya nufa yana isa yayi Knowking ahankali idanunsa suka sauƙa akan Dr Jameel dake tsaye Atsakiyar office Rungume da wata Norse Yana kissing din sassan jikinta cikin sauri ya runtse Idanunsa tare da faɗin.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin,J wai wani irin sauyi ne yazo maka arayuwar ka”.
Yayi mgnar cikin cushewar tunani duk da ɗabi'in wanda ake kira da Dr Jameel suna bashi cikekken yaƙinin cewa ba J dinsa bane wannan tsananin kamanceceniya ne. Toh amman kamanin da hatta muryarsu mgnar tafiyarsu komai iri ɗaya ne da na J ɗinsa yasa ya kasa amincewa kansa cewa ba J ɗinsa bane wannan.
Cikin fushi Dr Jameel ya ɗago kansa ya kalli Moddibo kana yace.
“Wai kai wani irin mutum ne tunda nace maka ba J ɗin da kake nema bane ka barni mana Meyesa zakayi ta bibiyar rayuwata?”.
Cikin sanyi Moddibo ya kallesa kana yace.
“Kaji tsoron Allah J! Shin wace irin rayuwa kasa kanka aciki J!? J mata ka fara bi ka maida kanka kamar kare wanda baisan abinda yake ba J yada ilimin ka zaka maida kanka haka cikin fushin Ubangiji kake so ka faɗa”.
Cike da ɓacin rai Dr Jameel ya juya ya kallesa kana yace.
“Anyi ɗin idan kana da iko ka hana nace maka Ni ba J ɗin ka ba kabarni inji daɗin rayuwata mana, jikinka ko jikina rayuwarka ko rayuwata matane dole in bisu inji daɗin rayuwata yoh akwai abinda ya kaisu daɗi ne”.
Cikin takaici Moddibo yace.
“J baka ji tsoron Allah ba da bakinka kake jaddada min aikin ka cewa zina kakeyi?”.
Harara Dr Jameel ya watsa masa cike da gadara yace.
“Anyi ɗin”.
Dafe kai Moddibo yayi tare da faɗin.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.
Cike da takaici Dr Jameel ya fisgo Norse din Wacce da alama ba musulma bace yana janyota ya manna bakinshi da nata.
Cikinta sauri Moddibo ya runtse Idanunsa da ƙarfi ya kifa kansa da jikin bango yana karanta duk wata addu'a da tazo bakinsa cikin sauri ya juya ya fita cikin motarsa ya zauna kasa tabuka komai yayi sai hawaye dake kwaranyo masa cikin ransa yace.
“Na gamsu wannan ba J na bane haƙiƙa ba Jameel ɗin Ummi bane.
Amman wallahi nayi al'ƙawarin in Sha Allah, zan gyara masa rayuwarsa da yardar Allah zai zama tamkar J dina na baya in sha Allah zaici albarkacin kamaninsa da J ɗina”.
Dr Jameel kuwa bayan sun gama aikata masha'arsu da wannan Arniyar ya shiga toilet yayi wanka yana fitowa yaji wayarsa na ringing Yana ɗaga wayar yayi Picking tare da kaiwa Kunnensa cike da girmamawa yace.
“Hello Unclee da kanka kuma?”.
Shiru yayi na wasu sekonni sai kuma yace.
“Toh shikenan ba matsala yanzun nan kuwa ganin zuwa.
Yana katse kiran ya gyara rigarsa tare da gyara zaman Necktie wuyansa.
Juyawa yayi ya kalli Norse din cikin bada umarni yace.
“Idan kin gama ki gyara min office ki rufe”.
Cike da yauƙi tace.
“Ok sir”.
Yana fita yashiga motarsa yaja.
Cikin sauri Moddibo dake zubda hawaye yabi bayansa duk inda ya juya akalar motarsa nan Moddibo yake bi shi kansa Moddibo baisan inda zaije ba kuma baisan me zaice masa ba, kuma baisan abinda zaiyiba.
“Toh jiya da daddare Lamiɗo ya kirani yace biki za'a haɗa dana ƴar wajensa kuma sunce Jumma'a na sama nema suke so aɗaura auren kunga yau saura kwana takwas nema, toh yace za ahaɗa dana Khausar”.
Jinjina kai innayi keyi cike da gamsuwa Malam Arɗo ya cigaba da cewa. “Sannan mun gama tattaunawa da Abban Jameel akan ayi kawai agama tunda dama Jameelu yayi ta jaddadawa cewa ayi ƙoƙari ayi shi cikin ƙanƙanin lokaci”.
Gyara zama Ummi tayi kana tace.
“Sosai ma ayi kokari ayi haka shiya dace”.
Gyara zama Malam Arɗo yayi kana yace .
“Sannan Alh Bashir yace kada ayi masa batun Auren”.
Kai Ummi ta gyaɗa cikin gamsuwa, shi kuwa Abban Jameel gyaran murya yayi tare da cewa.
“Innayi kada a faɗa masa fa, dan so nake muyi mishi ba zata”.
Cikin gamsuwa Innayi ta jinjina kai tare da cewa.
“Ai kuwa bazata kam suna da yawa kuma ɗin kanku akwai bazatar da zan muku.
Tunda in an ɗaura auren kai mishi ita za'ayi ko?".
Da sauri Abba yace.
“Ni zan kai mishi ita”.
Murmushi Innayi tayi tare da cewa.
“A'a kada ka damu a gayawa dangin amarya su shirya yan rakiyar amarya da basu gaza goma”.
Da sauri Ummi ta juyo ta kalleta tare da cewa.
“A'a Innayi bafa ƙasar nan bane, har Marocco nefa, ya za'ayi ace har mutun goma ai ɗawainiyar zatayi yawa, wurin sauƙesu ma ai jidali ne”.
Cikin sauri Malam Arɗo yace sosai ma kuwa.
Abba kuwa ido kawai ya zuba musu.
Ita kuwa innayi gyara zama tayi cike da yaƙini da kuma tabbaci tace.
“Kada ki damu Ummin Jameel, ai tuwon girma miyansa nama, kuma in dai masauƙine koda Gambulan baki ɗaya zamuje bazata rasa masauƙiba. Kana kema zakije Asma'u, Abban Jameel Malam Arɗo, dama Lamiɗon kansa zaije”.
Murmushi mai cike da nazari Abban Jameel yayi tare da tuno abubuwan da Jameel ya gaya mishi akan tarihin Modibbo da yace Innayi ta bashi.
Cikin gamsuwa yace.
Kada ki damu Fatima a gayawa mahaifiyar Khausar a samu mutun goma daga gefen dangin kausar na uwa da uba da ni kuwa zan gayawa Lamiɗo”.
Kai kawai Ummi ta iya gyaɗa musu, domin abin ya bata mmki tunda Modibbo fa ya gaya mata kuɗin tickets insa na business class 1,303,000 suku tum toh fisa bilillahi wannan kudi ai yawa garesu ace kusan mutun goma.
Jin Malam Arɗo yace.
“Ai akwai economic tickets, kudinsa bazai kai hakaba ni dashi nake amfani duk inda nake zuwa”.
Jin hakane yasa ta gane ashe mgnar zuci da tayi ya fito fili.
Innayi kuwa kai ta jinjina tare da cewa.
“In sha Allah dai ba abinda zai gagara”.
Abba kuwa cikin nitsuwa yace.
“Kayan lefenta kuwa nasa matar aminina Dr Ahmad zata haɗa komai, wata ƙil ya iso kafin muje".
Da sauri innayi tace.
“A'a a barsu sai munje can mu haɗa ai tunda zamuje da zuriyarta duk zasu gani”.
Da sauri Ummu tace.
“Ayi haka kuwa innayi a tafi da amarya ba lefe, ai za'ayi ta surutai”.
Cikin jinjina kai innayi tace.
“Barsu suyi lokacin sune”.
Nan suka ci-gaba da tattaunawa yadda komai zai wakana.
Tun daga wannan rana suka fara shirye-shiryen biki babu kama ƙafan Yaro.
Aranan da daddare aka kawo kayan Auren Amina kaya sunyi kyau sosai su Hajiya Lami ne suka tarbi kayan Auren Bayan anwatse Amina ta kalli Samira dake gefenta tayi tagumi wacce baki ɗaya ta rame ta sauya ta dawo shiru-shiru.
Kallon Samira tayi kana tace.
“Samira wallahi da gaske kin fara wari dan ina jin warin”.
Cikin zubda hawaye Samira ta kalleta Muryanta na rawa tace.
“Allah Amina kina ji ko?”.
Kai Amina ta gyaɗa cikin gaskiya da tace.
“Wallahi Ina ji Amina sai kinji kamar warin Baragurbin ƙwai”.
Cikin raunin murya tace.
“Na sani dole za aji warin kawai Mommy na Idan na faɗa mata sai tace bata ji amma nasan dole za aji warin”.
Yamutse fuska Amina tayi kana tace.
“Gaskiya dai kam kina warin Baragurbin ƙwai wallahi ki dage ki koma wajen Boka ya baki magani”.
Kai Samira ta Girgiza.
Dai-dai lokacin Hajiya Bunayya ta shigo Harara ta watsawa Amina tace.
“Ke dai Wallahi Amina baki da hankali amaimakon ki kwantar mata da hankali sai ki ƙara tayar mata”.
Baki ta tura tare da kallon Hajiya Bunayya tace.
“Mommy wannan ba maganar tada hankali bane gaskiya ne kawai ku koma wajen Boka Kar'uzu yayi ƙoƙarin nemo mata magani”.
lokacin kuma Hajiya Lami ta fito daga toilet dake Bedroom din tace.
“Boka Kar'uzu har yau bai dawo ba daga tafiyar da yayi nima jira nake ya dawo Inje ko shekara jiya naje ban same shiba.
Cikin rauni Samira ta kallesu muryanta na rawa tace.
“Ni dai da an haƙura da neman Magani awajen Boka Kar'uzu kawai anema min maganin Islamic medicine ko Allah zaisa adace”.
Atare Hajiya Bunayya da Hajiya Lami suka ce me kike faɗa haka ki dai bari asake gwadawa agani.
Shiru tayi ba tare da tace musu uffan ba.
*Morocco*
Motar Moddibo ce tsaye abakin Mouley Yussef Hospital Rabat kusan kullum sai yazo amma da zaran security dake bakin gate din ya ga shine zai ki buɗe masa yau kwana biyu kenan yana sintirin zuwa cikin sanyi jiki ya juya ya koma gida yana so ya faɗawa Abba to amma ta ina zai fara faɗa masa zaice Jameel ɗinsa ko kuma yaya zuwa wannan lokacin hankalinsa ya gama tashi ya rasa shin wani irin tunani zaiyi cikin wannan tunanin ya koma gida.
Washe gari: alhamis haka ya tashi cikin matsanancin kasala saboda yanda aka kwana ana zuga ruwan sama gari yayi sanyi cikin damuwa da ciwon kasala da jin bugun zuciya ya kwana adaddafe ya tashi ya shirya kai tsaye Company ya nufa ya dudduba aikin da akayi zuwa yanzu gaba ɗaya angama daddasa Injinan da za ayi aiki dasu alissafinsu Insha Allah ranan Monday za afara bubbuga Nauikan, Abaya, Laffa, Jallabiya, Sallayu, blankets, Jakankuna, takalma za a cigaba da sarrafa kaya.
Kai tsaye motarsa ya shiga har ya nufi gida sai kuma ya sinci kansa da juya alamar motarsa kai tsaye Mouley Youssef Hospital Rabat ya nufa yana isa bakin gate ɗin dai-dai lokacin da security ya buɗe wa wata mota gate wannan damar Moddibo ya samu yayi saurin cinna hancin motarsa ciki.
Yana isa yayi Parking security na ganinsa yace.
“You again”.
Iya abinda ya iya faɗa kenan domin haiba da ƙwarjinsa yasa ba zai iya korinsa ba cike da nutsuwa Moddibo ya nufa cikin reception duk ido mutanen da Norses ɗin suka zuba masa suna kallon baiwar kyau nutsuwa da kamala da kuma ƙwarjini da yake dashi.
Kai tsaye Office ɗin Dr Jameel ya nufa yana isa yayi Knowking ahankali idanunsa suka sauƙa akan Dr Jameel dake tsaye Atsakiyar office Rungume da wata Norse Yana kissing din sassan jikinta cikin sauri ya runtse Idanunsa tare da faɗin.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin,J wai wani irin sauyi ne yazo maka arayuwar ka”.
Yayi mgnar cikin cushewar tunani duk da ɗabi'in wanda ake kira da Dr Jameel suna bashi cikekken yaƙinin cewa ba J dinsa bane wannan tsananin kamanceceniya ne. Toh amman kamanin da hatta muryarsu mgnar tafiyarsu komai iri ɗaya ne da na J ɗinsa yasa ya kasa amincewa kansa cewa ba J ɗinsa bane wannan.
Cikin fushi Dr Jameel ya ɗago kansa ya kalli Moddibo kana yace.
“Wai kai wani irin mutum ne tunda nace maka ba J ɗin da kake nema bane ka barni mana Meyesa zakayi ta bibiyar rayuwata?”.
Cikin sanyi Moddibo ya kallesa kana yace.
“Kaji tsoron Allah J! Shin wace irin rayuwa kasa kanka aciki J!? J mata ka fara bi ka maida kanka kamar kare wanda baisan abinda yake ba J yada ilimin ka zaka maida kanka haka cikin fushin Ubangiji kake so ka faɗa”.
Cike da ɓacin rai Dr Jameel ya juya ya kallesa kana yace.
“Anyi ɗin idan kana da iko ka hana nace maka Ni ba J ɗin ka ba kabarni inji daɗin rayuwata mana, jikinka ko jikina rayuwarka ko rayuwata matane dole in bisu inji daɗin rayuwata yoh akwai abinda ya kaisu daɗi ne”.
Cikin takaici Moddibo yace.
“J baka ji tsoron Allah ba da bakinka kake jaddada min aikin ka cewa zina kakeyi?”.
Harara Dr Jameel ya watsa masa cike da gadara yace.
“Anyi ɗin”.
Dafe kai Moddibo yayi tare da faɗin.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.
Cike da takaici Dr Jameel ya fisgo Norse din Wacce da alama ba musulma bace yana janyota ya manna bakinshi da nata.
Cikinta sauri Moddibo ya runtse Idanunsa da ƙarfi ya kifa kansa da jikin bango yana karanta duk wata addu'a da tazo bakinsa cikin sauri ya juya ya fita cikin motarsa ya zauna kasa tabuka komai yayi sai hawaye dake kwaranyo masa cikin ransa yace.
“Na gamsu wannan ba J na bane haƙiƙa ba Jameel ɗin Ummi bane.
Amman wallahi nayi al'ƙawarin in Sha Allah, zan gyara masa rayuwarsa da yardar Allah zai zama tamkar J dina na baya in sha Allah zaici albarkacin kamaninsa da J ɗina”.
Dr Jameel kuwa bayan sun gama aikata masha'arsu da wannan Arniyar ya shiga toilet yayi wanka yana fitowa yaji wayarsa na ringing Yana ɗaga wayar yayi Picking tare da kaiwa Kunnensa cike da girmamawa yace.
“Hello Unclee da kanka kuma?”.
Shiru yayi na wasu sekonni sai kuma yace.
“Toh shikenan ba matsala yanzun nan kuwa ganin zuwa.
Yana katse kiran ya gyara rigarsa tare da gyara zaman Necktie wuyansa.
Juyawa yayi ya kalli Norse din cikin bada umarni yace.
“Idan kin gama ki gyara min office ki rufe”.
Cike da yauƙi tace.
“Ok sir”.
Yana fita yashiga motarsa yaja.
Cikin sauri Moddibo dake zubda hawaye yabi bayansa duk inda ya juya akalar motarsa nan Moddibo yake bi shi kansa Moddibo baisan inda zaije ba kuma baisan me zaice masa ba, kuma baisan abinda zaiyiba.