Sashe 12
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin tsawa yace.
“Ki fita ki bamu waje zamu ɗaura daga inda muka tsaya”.
Ya faɗa tare da kamo hannun Samira.
(Wa'iyazu Billah lalacacciyar uwa mai lalatacciyar tarbiya da ƙeƙyasashiyar zuciya).
Daga wannan rana haka Boka Kar'uzu ya cigaba da lalata rayuwar Samira Amma dake Hajiya Lami lalacacciyar Uwa ce da ba Allah da Manzonsa a ranta bare digon imani bata damu ba acikin kwanakin Hajiya Bunayya ta kawo musu ziyara sunanta hira, harda murnar gwara da suka canza Naseer da Jameel dan da shi suka riƙa gashi na ya rasu.
Kana tun ranan da Samira ta shiga ɗakin bata fita ba duk wani abu da suke buƙata Hajiya Lami na kai musu Boka Kar'uzu kuwa ko yaushe yana manne da ita yana addabarta a haka har ya cika satinsa da yace saida yayi gyaran kwana uku sannan ya koma gidansa bayan komawarsa da kwana biyar Baban Samira ya dawo.
*LITTAFIN SAKAYYAH DAI NA KUDINE KO KIN GANSHI A WASU WURAREN DA BA WURINA BA TOH NA SATANE KI BIYA KI KARANTA CIKIN AMINCI BABU HAƘƘIN WANI A GANKI LITTAFIN SAKAYYAH 1K NE KACAL DUK DA YAWANSA DA DAƊINSA DUBU ƊAYA NEFA KACAL, ki biya dubunki ɗaya ki karanta maimkyau ba sallake-sallake babu kin samu wasu PAGE ɗin baki samu wasuba ki karanta abinki one by one tura kuɗin samun damar karantawa ta asusuna na GTBank. 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 sai in tura miki karanta lfy lafiya. Mu guji yaƙin wani duk ƙanƙantarsa domin na watan nan dai na Allah ya isane atoh*
*Jauro Yaya*
Hajja Nana ce zaune da ƙoron Abincin agefenta yayinda Dije da bata daɗe da zuwa ba ke zaune gefenta cikin sauri Hajja Nana ta miƙe tsaye jin tsayuwar mota aƙofar gida kallon Dije tayi fuskarta ɗauke da murmushi tace.
“Ya naji kamar ƙaran mota?”.
Kai Dije ta gyaɗa tare da miƙewa kana tace.
“Nima Hajja Nana haka naji kamar ƙaran Mota”.
Cike da zaƙuwa tace.
“Maza je ki duba waye ne?”.
Kai Dije ta gyaɗa tare da fita tana ganin motar tayi dariya tare da ɗaga sautin Muryanta tace.
“Laaa Hajja Nana Baffa Jimeta ne”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Masha Allah dan albarka ya ɗauki abin da muhimmanci ne”.
Anutse Baffa Jimeta ya shigo cikin gidan.
Cikin sauri Dije ta shimfiɗa masa tabirma ya zauna suka gaisa ba daɗewa baki daya ƙannenta suka shigo.
Bayan sun gama gaishe-gaishe Hajja Nana ta kalli Baffa Jimeta fuskarta ɗauke da murmushi tace.
“Kazo kenan?”.
Kai Baffa Jimeta ya gyaɗa cike da ladabi yace.
“Nazo Hajja Nana”.
Murmushi tayi tare da gyara zamanta kana tace.
“Kazo batun Khausar ko?”.
Jinjina kai yayi cikin sanyin murya yace.
“Ai dole na inzo domin cika Umarnin ki”.
Kallon ƙannenta tayi cikin alamun jin daɗi tace.
“Toh Idan Allah ya kaimu gobe da safe zamu tafi can”.
Ahankali ya gyara zamansa sannan yace.
“Toh shikenan Allah ya kaimu lafiya”.
Da daddare Misalin karfe 7:30 malam Arɗo da Abba ne zaune acikin mota Kallon Abba dake tuƙi Malam Arɗo yayi tare da sauke ajiyar zuciya kana yace.
“Insha Allah yau zamuje mu isar da nufin Mu”.
Jinjina kai Abba yayi cikin sanyin Murya yace.
“Insha Allah yau zamu ida Wasiyyar Jameelu na sai muji abinda mahaifin yarinyar zai faɗa”. daga nan suka nufi gidan Ummi
Washe gari da safe Misalin ƙarfe tara Hajja Nana da Baffa Jimeta tare da Malam Liman suka isa gidan Lamiɗo kai tsaye Sashen Mommy ta nufa Dije na biye da ita.
Malam Liman da Baffa Jimeta kuma suka nufi falon Lamiɗo.
Cike sauri Mommy dake shirya dining table ta juya jin Sallamar Hajja Nana cike da girmamawa tace.
“Hajja lale marhaba kece”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da faɗin.
“Wallahi kuwa”.
Murmushi Mommy tayi tare da miƙewa bayan sun gaisa ta nufi dining table ta kawo musu Flaks din tea da soyayyan ƙwai da buredi da kuma ɗumamen tuwon shinkafa miyar taushe ta ajiye musu sannan ta basu waje dake basuyi breakfast suka taho nan suka ci.
Bayan sun gama Mommy na murmushi tace.
“Amma kunyi saurin isowa”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tana gyara zaman Flaks din tace.
“Eh ai bani kaɗai bace da Malam Liman da kuma Baffa Jimeta muka zo akan dai Maganar Auren Khausar dana miki ne”.
Khausar dake zuba chips afaranti tayi saurin kallon Hajja Nana babu walwala atare da ita tace.
“Wai dan Allah Hajja Nana mena tsare miki ne arayuwar duniyar nan?”.
Kallonta Hajja Nana tayi cikin sassauta murya tace.
“Ni ba abinda kika tsare min, kawai dai gata nake so na Miki domin Aure shine rufin asiri da kuma gatan ƴa mace, sannan ga ɗan uwanki zai riƙe ki da Amana da gaskiya”.
Ta dire ayar mgnar tare da murmushi ta kallon Khausar data tsareta da ido kana ta sassauta murya ta cigaba da cewa.
“Ga Babansa ma munzo tare, dan in muka gama magana ma, shi yau zai wuce mu kuma motar Kasuwa zamu hau kawai”.
Kallonta kawai Khausar keyi Muryanta na rawa tace.
“Wai dan Allah Hajja Nana Meyesa kike min haka ne?.
Agaskiya ni banason abinda kike min?”.
Taɓe baki Hajja Nana tayi tare da tsira mata ido tace.
“Ko bakyaso dole sai anyi”.
Cikin sauri Khausar tace.
“Wallahi Ni dai baza ayimin dole ba”.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe da alamun ɓacin rai ta kalli Khausar tace.
“Wai Khausar Meyesa haka ne bana son abinda kike min fa banaso kifa kiyayi kanki ki barni inji da abu ɗaya”.
Dai-dai lokacin Lamiɗo ya shigo falon tare da zama aƙasa kana cike da ladabi ya Marabci Hajja Nana.
juyawa yayi ya kalli matarsa tuni ya gano ɓacin ran dake fuskarta kawai kawaici takeyi shiyasa bata nunawa amman wani lokaci ma daɗi takeji in Khausar na titse kakartata.
Anutse ya gyara zamansa kana yayi ƙasa da kansa cike da ladabi da kuma mutuntawa yace.
“Addah Nana yanzu mukayi magana da Alhj Muhammadu da kuma Malam Liman mun gama magana dasu”.
Murmushi Hajja Nana tayi tare da jinjina kai kana tace.
“Yawwa sun maka bayani ko?”.
Jinjina kai yayi cike da ladabi yace.
“Eh sunyi min”.
Miƙewa Khausar tayi tare da kallon Dije tace.
“Dija mu tafi”.
Numfashi Lamiɗo ya fesar kana yace.
“A'a Khausar zauna”.
Kai ta gyaɗa tare da komawa ta zauna kana ta sunkuyar da kanta ƙasa hawaye na ciko mata ido.
Ahankali Lamiɗo ya sake yin ƙasa da kansa kana yace.
“Toh Hajja Nana naji abinda yake tafe daku, akan batun Khausar da ɗan Uwanta Aliyu”.
Cikin sauri Khausar ta ɗago kanta tare da kallon Lamiɗo sai kuma tayi saurin sunkuyar da kanta hawaye na kwaranyo mata kana zuciyarta na bugawa da masifar ƙarfi.
Ahankali Abba ya cigaba da cewa.
“Ni babu wata matsala daga gareni, duk da da akwai ƙanina ɗan Yafendo na dake son Khausar tun tana ƙarama, toh amma sawun giwa ya take na raƙumi, abinda kuke ce shi za ayi domin koda inada power akan Khausar kun fini ƙarfi”.
Sai kuma ya ɗago kansa tare da kallon Hajja Nana data tsaresa da ido Ajiyar zuciya ya sauƙe kana ya cigaba da cewa.
“Amma Koda batun Naseer bazai kau da batun ku na kawo na Naseer ba, duk da cewa bamu ji ta bakin yarinya ba duk da naga alamun ta dai-dai-ta da ɗan Uwanta tun da yanzu bana ganinsu da Naseer”.
Ya kare mgnar tare da kallon Khausar da tayi ƙasa da kanta fuskarta cike da hawaye numfashin ya ɗan fesar kana yace.
“Sannan ba aji ra'ayin Khausar ba, domin yaran yanzu ba ayi musu dole sabida haka ya kamata aji ra'ayin Khausar idan tanason.
Ɗan Uwanta tofa sawun Giwa ya take na raƙumi idan kuma Naseer take so tou sai mu nemi al'farma a wurinku”.
Ƙankance ido Hajja Nana tayi kana ta shiga girgiza ƙafanta tare da kallon Lamiɗo tace.
“Lalle kam kamar yanda ka faɗa haka ne, sawun Giwa ya take na raƙumi, sannan batun so kuke ɓata ƴaƴanku mu da ai sai dai a aura maka ko kana so ko baka so, kuma hakan be hana zaman lafiya ba”.
Ahankali Lamiɗo ya sunkuyar da kansa cikin girmamawa da tausashi harshe yace.
“Ai zamani ne ya sauya Hajja Nana Da da yanzu ba ɗaya bane amman yanzu bari muji ta bakinta”.
Ya kare mgnar tare da gyara zamansa ya fuskanci Khausar cikin tausasawa yace.
“Khausar”.
Murya na rawa ta amsa, yayinda tuni hawaye ke kwaranya.
Mommy kam numfashi mai nauyi ta fesar tare da kauda kanta ranta cike da tausayin yarta.
Shi kuwa Lamido cikin kulawa yace.
“Ki dena kuka Khausar kada ki damu ki gaya min cikin mutun biyu Aliyu Dan uwanki da Naseer wa kikeso, kada kiji tsoro kinjiko Mamana gaya min”.
Jin hakane yasa Khausar ɗago kanta ahankali zuciyarta na cike da wani irin masifaffen rauni murya na rawa ido na kwaranyar da hawaye ta kalli Lamiɗo tare da cewa.
“Abba Ni dai bana sonsa”.
Cikin sauri Hajja Nana ta kalli Khausar tare da ƙankance Ido a faɗace tace.
“Don Ubanki to Naseerun kike so dangin Mayu!?”.
Sassayan kuka Khausar ta saki tare da cewa.
“Nikam shima bana sonsa”.
Kusan a tare Mommy da Hajja Nana da Lamiɗo duk suka kalleta.
Cikin tsawa da masifar isa da iko Hajja Nana tace.
“Toh wa kike so?, sannan me kike nufi ?,wa zaki Aura?, tunda kince bakyaso Aliyu ba kyason Naseerun?”.
Shiru batace komaiba, sai kuka.
Ganin haka yasa Lamido yin gyaran murya cikin Muryar lallashi yace.
“Toh wa kikeso Manana?”.
Kukan ne ya fara tsanantan mata kana a raunace ta ƙara sunkuyar da kanta.
Afusace Hajja Nana tace.
“Toh dan ubanki wa zaki Aura? Wa kikeso?”.
Cike da sanyi murya na rawa tace.
“Ni dai akwai wanda zan aura?”
Mommy kuwa da sauri ta kalli Khausar wacce tunda aka fara magana bata ce Uffan ba cike da mamaki tace.
“Khausar dawa ye kike soyyayya ban saniba wa kike so wa zaki Aura!?”.
Ahankali Khausar ta gyara zamanta tare da sun kuyar da kanta ƙasa kana tace.
“Ni Moddibo nake so”...!
“Ki fita ki bamu waje zamu ɗaura daga inda muka tsaya”.
Ya faɗa tare da kamo hannun Samira.
(Wa'iyazu Billah lalacacciyar uwa mai lalatacciyar tarbiya da ƙeƙyasashiyar zuciya).
Daga wannan rana haka Boka Kar'uzu ya cigaba da lalata rayuwar Samira Amma dake Hajiya Lami lalacacciyar Uwa ce da ba Allah da Manzonsa a ranta bare digon imani bata damu ba acikin kwanakin Hajiya Bunayya ta kawo musu ziyara sunanta hira, harda murnar gwara da suka canza Naseer da Jameel dan da shi suka riƙa gashi na ya rasu.
Kana tun ranan da Samira ta shiga ɗakin bata fita ba duk wani abu da suke buƙata Hajiya Lami na kai musu Boka Kar'uzu kuwa ko yaushe yana manne da ita yana addabarta a haka har ya cika satinsa da yace saida yayi gyaran kwana uku sannan ya koma gidansa bayan komawarsa da kwana biyar Baban Samira ya dawo.
*LITTAFIN SAKAYYAH DAI NA KUDINE KO KIN GANSHI A WASU WURAREN DA BA WURINA BA TOH NA SATANE KI BIYA KI KARANTA CIKIN AMINCI BABU HAƘƘIN WANI A GANKI LITTAFIN SAKAYYAH 1K NE KACAL DUK DA YAWANSA DA DAƊINSA DUBU ƊAYA NEFA KACAL, ki biya dubunki ɗaya ki karanta maimkyau ba sallake-sallake babu kin samu wasu PAGE ɗin baki samu wasuba ki karanta abinki one by one tura kuɗin samun damar karantawa ta asusuna na GTBank. 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 sai in tura miki karanta lfy lafiya. Mu guji yaƙin wani duk ƙanƙantarsa domin na watan nan dai na Allah ya isane atoh*
*Jauro Yaya*
Hajja Nana ce zaune da ƙoron Abincin agefenta yayinda Dije da bata daɗe da zuwa ba ke zaune gefenta cikin sauri Hajja Nana ta miƙe tsaye jin tsayuwar mota aƙofar gida kallon Dije tayi fuskarta ɗauke da murmushi tace.
“Ya naji kamar ƙaran mota?”.
Kai Dije ta gyaɗa tare da miƙewa kana tace.
“Nima Hajja Nana haka naji kamar ƙaran Mota”.
Cike da zaƙuwa tace.
“Maza je ki duba waye ne?”.
Kai Dije ta gyaɗa tare da fita tana ganin motar tayi dariya tare da ɗaga sautin Muryanta tace.
“Laaa Hajja Nana Baffa Jimeta ne”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Masha Allah dan albarka ya ɗauki abin da muhimmanci ne”.
Anutse Baffa Jimeta ya shigo cikin gidan.
Cikin sauri Dije ta shimfiɗa masa tabirma ya zauna suka gaisa ba daɗewa baki daya ƙannenta suka shigo.
Bayan sun gama gaishe-gaishe Hajja Nana ta kalli Baffa Jimeta fuskarta ɗauke da murmushi tace.
“Kazo kenan?”.
Kai Baffa Jimeta ya gyaɗa cike da ladabi yace.
“Nazo Hajja Nana”.
Murmushi tayi tare da gyara zamanta kana tace.
“Kazo batun Khausar ko?”.
Jinjina kai yayi cikin sanyin murya yace.
“Ai dole na inzo domin cika Umarnin ki”.
Kallon ƙannenta tayi cikin alamun jin daɗi tace.
“Toh Idan Allah ya kaimu gobe da safe zamu tafi can”.
Ahankali ya gyara zamansa sannan yace.
“Toh shikenan Allah ya kaimu lafiya”.
Da daddare Misalin karfe 7:30 malam Arɗo da Abba ne zaune acikin mota Kallon Abba dake tuƙi Malam Arɗo yayi tare da sauke ajiyar zuciya kana yace.
“Insha Allah yau zamuje mu isar da nufin Mu”.
Jinjina kai Abba yayi cikin sanyin Murya yace.
“Insha Allah yau zamu ida Wasiyyar Jameelu na sai muji abinda mahaifin yarinyar zai faɗa”. daga nan suka nufi gidan Ummi
Washe gari da safe Misalin ƙarfe tara Hajja Nana da Baffa Jimeta tare da Malam Liman suka isa gidan Lamiɗo kai tsaye Sashen Mommy ta nufa Dije na biye da ita.
Malam Liman da Baffa Jimeta kuma suka nufi falon Lamiɗo.
Cike sauri Mommy dake shirya dining table ta juya jin Sallamar Hajja Nana cike da girmamawa tace.
“Hajja lale marhaba kece”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da faɗin.
“Wallahi kuwa”.
Murmushi Mommy tayi tare da miƙewa bayan sun gaisa ta nufi dining table ta kawo musu Flaks din tea da soyayyan ƙwai da buredi da kuma ɗumamen tuwon shinkafa miyar taushe ta ajiye musu sannan ta basu waje dake basuyi breakfast suka taho nan suka ci.
Bayan sun gama Mommy na murmushi tace.
“Amma kunyi saurin isowa”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tana gyara zaman Flaks din tace.
“Eh ai bani kaɗai bace da Malam Liman da kuma Baffa Jimeta muka zo akan dai Maganar Auren Khausar dana miki ne”.
Khausar dake zuba chips afaranti tayi saurin kallon Hajja Nana babu walwala atare da ita tace.
“Wai dan Allah Hajja Nana mena tsare miki ne arayuwar duniyar nan?”.
Kallonta Hajja Nana tayi cikin sassauta murya tace.
“Ni ba abinda kika tsare min, kawai dai gata nake so na Miki domin Aure shine rufin asiri da kuma gatan ƴa mace, sannan ga ɗan uwanki zai riƙe ki da Amana da gaskiya”.
Ta dire ayar mgnar tare da murmushi ta kallon Khausar data tsareta da ido kana ta sassauta murya ta cigaba da cewa.
“Ga Babansa ma munzo tare, dan in muka gama magana ma, shi yau zai wuce mu kuma motar Kasuwa zamu hau kawai”.
Kallonta kawai Khausar keyi Muryanta na rawa tace.
“Wai dan Allah Hajja Nana Meyesa kike min haka ne?.
Agaskiya ni banason abinda kike min?”.
Taɓe baki Hajja Nana tayi tare da tsira mata ido tace.
“Ko bakyaso dole sai anyi”.
Cikin sauri Khausar tace.
“Wallahi Ni dai baza ayimin dole ba”.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe da alamun ɓacin rai ta kalli Khausar tace.
“Wai Khausar Meyesa haka ne bana son abinda kike min fa banaso kifa kiyayi kanki ki barni inji da abu ɗaya”.
Dai-dai lokacin Lamiɗo ya shigo falon tare da zama aƙasa kana cike da ladabi ya Marabci Hajja Nana.
juyawa yayi ya kalli matarsa tuni ya gano ɓacin ran dake fuskarta kawai kawaici takeyi shiyasa bata nunawa amman wani lokaci ma daɗi takeji in Khausar na titse kakartata.
Anutse ya gyara zamansa kana yayi ƙasa da kansa cike da ladabi da kuma mutuntawa yace.
“Addah Nana yanzu mukayi magana da Alhj Muhammadu da kuma Malam Liman mun gama magana dasu”.
Murmushi Hajja Nana tayi tare da jinjina kai kana tace.
“Yawwa sun maka bayani ko?”.
Jinjina kai yayi cike da ladabi yace.
“Eh sunyi min”.
Miƙewa Khausar tayi tare da kallon Dije tace.
“Dija mu tafi”.
Numfashi Lamiɗo ya fesar kana yace.
“A'a Khausar zauna”.
Kai ta gyaɗa tare da komawa ta zauna kana ta sunkuyar da kanta ƙasa hawaye na ciko mata ido.
Ahankali Lamiɗo ya sake yin ƙasa da kansa kana yace.
“Toh Hajja Nana naji abinda yake tafe daku, akan batun Khausar da ɗan Uwanta Aliyu”.
Cikin sauri Khausar ta ɗago kanta tare da kallon Lamiɗo sai kuma tayi saurin sunkuyar da kanta hawaye na kwaranyo mata kana zuciyarta na bugawa da masifar ƙarfi.
Ahankali Abba ya cigaba da cewa.
“Ni babu wata matsala daga gareni, duk da da akwai ƙanina ɗan Yafendo na dake son Khausar tun tana ƙarama, toh amma sawun giwa ya take na raƙumi, abinda kuke ce shi za ayi domin koda inada power akan Khausar kun fini ƙarfi”.
Sai kuma ya ɗago kansa tare da kallon Hajja Nana data tsaresa da ido Ajiyar zuciya ya sauƙe kana ya cigaba da cewa.
“Amma Koda batun Naseer bazai kau da batun ku na kawo na Naseer ba, duk da cewa bamu ji ta bakin yarinya ba duk da naga alamun ta dai-dai-ta da ɗan Uwanta tun da yanzu bana ganinsu da Naseer”.
Ya kare mgnar tare da kallon Khausar da tayi ƙasa da kanta fuskarta cike da hawaye numfashin ya ɗan fesar kana yace.
“Sannan ba aji ra'ayin Khausar ba, domin yaran yanzu ba ayi musu dole sabida haka ya kamata aji ra'ayin Khausar idan tanason.
Ɗan Uwanta tofa sawun Giwa ya take na raƙumi idan kuma Naseer take so tou sai mu nemi al'farma a wurinku”.
Ƙankance ido Hajja Nana tayi kana ta shiga girgiza ƙafanta tare da kallon Lamiɗo tace.
“Lalle kam kamar yanda ka faɗa haka ne, sawun Giwa ya take na raƙumi, sannan batun so kuke ɓata ƴaƴanku mu da ai sai dai a aura maka ko kana so ko baka so, kuma hakan be hana zaman lafiya ba”.
Ahankali Lamiɗo ya sunkuyar da kansa cikin girmamawa da tausashi harshe yace.
“Ai zamani ne ya sauya Hajja Nana Da da yanzu ba ɗaya bane amman yanzu bari muji ta bakinta”.
Ya kare mgnar tare da gyara zamansa ya fuskanci Khausar cikin tausasawa yace.
“Khausar”.
Murya na rawa ta amsa, yayinda tuni hawaye ke kwaranya.
Mommy kam numfashi mai nauyi ta fesar tare da kauda kanta ranta cike da tausayin yarta.
Shi kuwa Lamido cikin kulawa yace.
“Ki dena kuka Khausar kada ki damu ki gaya min cikin mutun biyu Aliyu Dan uwanki da Naseer wa kikeso, kada kiji tsoro kinjiko Mamana gaya min”.
Jin hakane yasa Khausar ɗago kanta ahankali zuciyarta na cike da wani irin masifaffen rauni murya na rawa ido na kwaranyar da hawaye ta kalli Lamiɗo tare da cewa.
“Abba Ni dai bana sonsa”.
Cikin sauri Hajja Nana ta kalli Khausar tare da ƙankance Ido a faɗace tace.
“Don Ubanki to Naseerun kike so dangin Mayu!?”.
Sassayan kuka Khausar ta saki tare da cewa.
“Nikam shima bana sonsa”.
Kusan a tare Mommy da Hajja Nana da Lamiɗo duk suka kalleta.
Cikin tsawa da masifar isa da iko Hajja Nana tace.
“Toh wa kike so?, sannan me kike nufi ?,wa zaki Aura?, tunda kince bakyaso Aliyu ba kyason Naseerun?”.
Shiru batace komaiba, sai kuka.
Ganin haka yasa Lamido yin gyaran murya cikin Muryar lallashi yace.
“Toh wa kikeso Manana?”.
Kukan ne ya fara tsanantan mata kana a raunace ta ƙara sunkuyar da kanta.
Afusace Hajja Nana tace.
“Toh dan ubanki wa zaki Aura? Wa kikeso?”.
Cike da sanyi murya na rawa tace.
“Ni dai akwai wanda zan aura?”
Mommy kuwa da sauri ta kalli Khausar wacce tunda aka fara magana bata ce Uffan ba cike da mamaki tace.
“Khausar dawa ye kike soyyayya ban saniba wa kike so wa zaki Aura!?”.
Ahankali Khausar ta gyara zamanta tare da sun kuyar da kanta ƙasa kana tace.
“Ni Moddibo nake so”...!