Sashe 51
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Washe gari da safe koda Sarki Youseef Mouley da Didi suka shiga wajen Moddibo suna tare da Jalaludden sai dai su basu da ikon ganinsa kasancewar bai bayyana musu kansa ba,
ko Moddibo ba ma asiffar mutum yazo masa wanda sukayi karatu dashi.
Bayan fitansu ya kalli Moddibo yace.
“Kana kama da Mahaifinka”.
Da mamaki Moddibo ke kallonsa kafin ahankali yace.
“Mahaifina ko?”.
Kai Jalaludden ya gyaɗa Fuskarsa ɗauke da murmushi yace.
“Eh Mahaifinka mana, shin ban taɓa faɗa maka cewa kai ba ɗan Nigeria bane, har kaita dariya kana tambayata to kai ɗan ina bane?”.
Kai Moddibo ya jinjina tuni lokacin suna Jami'atul Madina bayan sun fito daga darasi suna shan shayi Jalaludden ke sanar masa.
Still da murmushi afuskarsa ya cigaba da faɗin.
“Har kace min kai ɗan ina ne nace kai ɗan Morocco ne, kace ba haka bane.
Amma ni nasan hakane saboda nayi bincike ne akan Innayinka na kuma fahimci haka”.
Zazzafan ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe cikin tsira masa idanu yace.
“Kenan kana nufin nan ƙasatace?”.
Murmushi Jalaludden yayi ta gyaɗa masa kai kana yace.
“Sosai ma kuwa ƙasar kane, tsatsonkane, Mahaifarkane. Wa'annan kuma Mahaifanka ne”.
Cikin girmamawa lamuran Ubangji mabuwayi gagara misali Moddibo yace.
“Ya Salam shin taya akayi wanna al'amarin yakasance ya akayi abin ya faru a haka, abin ne yazo min tamkar amafarkaina na yau da kullum”.
Gyara zama Jalaludden yayi tare da faɗin.
“Kada kayi mamaki,Ka cire al'ajabi da mamaki acikin lamarin Ubangji ya wuce mamaki. Kai dai kawai kayi godiya ga Allah”.
Ahankali Moddibo ya motsa laɓɓansayace.
“Alhamdulillah Allah kulli halin”.
Kai Jalaludden ya jinjina haka suka cigaba da hira kafin daga bisani Jalaludden ya kalli Moddibo da murmushi afuskarsa yace.
“Sannan kuma akwai al'amarin da naje na samu ranan juma'a ya kasance amma bazan faɗa maka ba sai ka ganin da idonka”.
Ware idanu Moddibo yayi kana ya langwaɓar da kai tare da cewa.
“Jalaluddeen nawa dan Allah ka faɗa min mana”.
Ƴar dariya Jalaludden yayi wanda ya bayyanar da fararen haƙoransa yace.
“Ok naje na samu Ummi ta shiga damuwa sosai akan tsawon kwana uku kenan tana kiran wayar ka amma bai shiga har Abban Jameel yazo da kanshi dan Maganar dana samu suna tattaunawa da Innayi kenan”.
Lumshe idanu Moddibo yayi yasan dole hakan zai kasance rashin jinsa awaya zai ɗaga musu hankali musamman Innayi da Ummi shima Abba sai dai kawai yayi dauriyar maza.
Da murmushi Jalaludden ya cigaba da cewa.
“Ya faɗawa Innayi shima ya kira wayarka baya shiga tsawon kwana uku kenan, amma kuma Innayi sai dariya take tana ce musu kada su damu kawai afara shirin kawo maka”...
Sai kuma yayi shiru tare da yin mgnar zuci. Alhamdulillah gwara da ban faɗa masa ba saboda naji suna faɗin cewa Moddibo bai san anyi masa Aure ba..
Ɗan ware idanu Moddibo yace.
“Ana shirin kawo min me?”.
Buɗe hannu Jalaludden yayi kana yace.
“Kai dai ana shiri kawai abinda naji sun faɗa kenan”.
Langwaɓar da kai Moddibo yayi cikin Muryansa mai cike da sanyi yace.
“Kai dai Jalaludden baza ka faɗa min ba kawai”.
Kai Jalaludden ya girgiza kana yace.
“Um-um iya abinda naji kenan, kasan na faɗa maka bansan gaibu ba Allah ne kaɗai mafi sanin gaibu”.
Kai Moddibo ya jinjina cikin gamsuwa da maganarsa yace.
“Toh shikenan”.
Washe gari Litinin ya kama kwanan Moddibo biyar kenan acikin Masarautar Mouley.
Misalin ƙarfe tara na safe Moddibo ne zaune acikin tangamemen Falon kamar yanda ya saba ko yaushe yaji an buɗe ƙofar falon anutse ya ɗaga kyawawan idanunsa tare da kallon ƙofar.
Idanunsa suka sauƙa akan.
Didi da Sarki Youseef Mouley sai wani kyakykyawan Matashi mai masifar kama dashi kallo ɗaya ya masa ya fahimci shine Ibraahim ƙaninsa ne da Didi ke yawan bashi labarinsa duba da kamannin dake tsakanin su. Sai kuma Lalla Khadijah da Lalla Hafsat, sai ƴar auta Rahama.
Ibraahim kuwa yalwataccen murmushi ya sakar masa domin shi yakasance mutum ne mai fara'a da son Mutane kana da abin dariya
Suna haɗa ido da Moddibo ya ƙara fara'ar fuskarsa kana ya tafi cikin sassarfa ya rungumeshi yana mai jin farin ciki da nutsuwa agaba ɗaya ilahirin jikinsa cike da shauƙi ya ɗago kansa kana yace.
“Yaya zance maka? Ko kuma Usaini? ko kuma Hassan ɗina?”.
Moddibo kuwa lokaci ɗaya ya tsinci kansa da ƙaunar yaron aransa rungumesa yayi kana cikin ɗan sakin fuska yace.
“Koma me ka kirani dashi zan amsa”.
Sai kuma suka sake rungume juna yayin da ƙaunar junansu ke ratsa ko wani lungu da saƙon dake jikinsu...
Cikin tsanananin so da ƙauna Lalla Khadijah tace.
“Kai Ibraahim ka sakeshi haka mana”.
Kalla Hafsat dake ruggume da ɗiyarta ce tayi dariya tare da zama tana kiciniyar bawa baby nono, tace.
“Ai dai kam ya maƙaleshi kamar ya fimu sonshi”.
Didi da Abualeey kam kallonsu kawai suke cike da jin daɗi mata misaltawa.
Rahama kuwa cikin tura baki ta harari Ibrahim cikin yanayin tsamar saƙo-da saƙo tace.
“Ai shi haka yake ga yadda ya maƙaleshi kamar shine auta”.
Cikin jin daɗi Abualeey yace.
“Toh mu zauna dai kafin ai ta yiwa Ibraahim ƙorafi”.
Shiko Ibraahim signal yayiwa Rahama tare da cewa.
“Ai shi nawane ni kaɗai ba dama cewa kike nine bani da ɗan uwaba toh Allah ya dawo min da ƴaƴana dama yafi Yayunki kyau”.
Lalla Khadijah ce ta ɗan zuggure ƙayarsa.
Ɗan tsalle yayi tare da
ɗago kansa ya kallin Moddibo kana yace.
“Kaga abinda suke minko ko Yah Aleey”.
Murmushi Modibbo yayi tare da ɗan janye jikinshi gefe yana mai kallonsu ɗaya bayan ɗaya yakejin sonsu da ƙaunarsu na ratsa mishi zuciya.
Shi kuwa Ibraahim baki ya ɗan tura tare da cewa.
“Kayi haƙuri ɗan uwana”.
“A kan me?”. Modibbo ya jefa mishi tambayar.
da sauri yace.
“Sabida rashin dawowata da wuri, sabida ranar da kazo ranar na tafi Turkiyya dan daga nan muke kai musu dabino, toh nike wakiltan lamarin, koda Lalla Hafsat ta gaya min ji nayi kamar inyi fiffige in dawo gashi naga dan ban dawo da wuriba kamar kafi sonsu a kaina”.
Dariya sukayi baki daya.
Sai kuma duk suka tsagaita tare da zubawa Modibbo ido ganin yadda yake dariya tare da shafa kan Ibraahim dan ganinshi yake kamar Bashir.
Didi kuwa da su Kalla Hafsat murmushi dukeyi ganin yadda ya jawo Ibraahim ya ruggumeshi yana mai cewa.
“Waya ce maka nafi sonsu, suda zasu koma gidajensu su barmu tare”.
Cikin dariya yayi musu gwala.
Rahama kuwa ɗan rawa tayi tare da faɗin.
“Ni dai muna tare”.
Shi kuwa Ibraahim
juyowa ya kalli Didi da Abualeey tare da cewa.
“Dan Allah Didi ku aurar da ita ta bar mana gida mu sake".
Baki ta tura tare da cewa.
“Ba ruwanka da ni”.
ko Moddibo ba ma asiffar mutum yazo masa wanda sukayi karatu dashi.
Bayan fitansu ya kalli Moddibo yace.
“Kana kama da Mahaifinka”.
Da mamaki Moddibo ke kallonsa kafin ahankali yace.
“Mahaifina ko?”.
Kai Jalaludden ya gyaɗa Fuskarsa ɗauke da murmushi yace.
“Eh Mahaifinka mana, shin ban taɓa faɗa maka cewa kai ba ɗan Nigeria bane, har kaita dariya kana tambayata to kai ɗan ina bane?”.
Kai Moddibo ya jinjina tuni lokacin suna Jami'atul Madina bayan sun fito daga darasi suna shan shayi Jalaludden ke sanar masa.
Still da murmushi afuskarsa ya cigaba da faɗin.
“Har kace min kai ɗan ina ne nace kai ɗan Morocco ne, kace ba haka bane.
Amma ni nasan hakane saboda nayi bincike ne akan Innayinka na kuma fahimci haka”.
Zazzafan ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe cikin tsira masa idanu yace.
“Kenan kana nufin nan ƙasatace?”.
Murmushi Jalaludden yayi ta gyaɗa masa kai kana yace.
“Sosai ma kuwa ƙasar kane, tsatsonkane, Mahaifarkane. Wa'annan kuma Mahaifanka ne”.
Cikin girmamawa lamuran Ubangji mabuwayi gagara misali Moddibo yace.
“Ya Salam shin taya akayi wanna al'amarin yakasance ya akayi abin ya faru a haka, abin ne yazo min tamkar amafarkaina na yau da kullum”.
Gyara zama Jalaludden yayi tare da faɗin.
“Kada kayi mamaki,Ka cire al'ajabi da mamaki acikin lamarin Ubangji ya wuce mamaki. Kai dai kawai kayi godiya ga Allah”.
Ahankali Moddibo ya motsa laɓɓansayace.
“Alhamdulillah Allah kulli halin”.
Kai Jalaludden ya jinjina haka suka cigaba da hira kafin daga bisani Jalaludden ya kalli Moddibo da murmushi afuskarsa yace.
“Sannan kuma akwai al'amarin da naje na samu ranan juma'a ya kasance amma bazan faɗa maka ba sai ka ganin da idonka”.
Ware idanu Moddibo yayi kana ya langwaɓar da kai tare da cewa.
“Jalaluddeen nawa dan Allah ka faɗa min mana”.
Ƴar dariya Jalaludden yayi wanda ya bayyanar da fararen haƙoransa yace.
“Ok naje na samu Ummi ta shiga damuwa sosai akan tsawon kwana uku kenan tana kiran wayar ka amma bai shiga har Abban Jameel yazo da kanshi dan Maganar dana samu suna tattaunawa da Innayi kenan”.
Lumshe idanu Moddibo yayi yasan dole hakan zai kasance rashin jinsa awaya zai ɗaga musu hankali musamman Innayi da Ummi shima Abba sai dai kawai yayi dauriyar maza.
Da murmushi Jalaludden ya cigaba da cewa.
“Ya faɗawa Innayi shima ya kira wayarka baya shiga tsawon kwana uku kenan, amma kuma Innayi sai dariya take tana ce musu kada su damu kawai afara shirin kawo maka”...
Sai kuma yayi shiru tare da yin mgnar zuci. Alhamdulillah gwara da ban faɗa masa ba saboda naji suna faɗin cewa Moddibo bai san anyi masa Aure ba..
Ɗan ware idanu Moddibo yace.
“Ana shirin kawo min me?”.
Buɗe hannu Jalaludden yayi kana yace.
“Kai dai ana shiri kawai abinda naji sun faɗa kenan”.
Langwaɓar da kai Moddibo yayi cikin Muryansa mai cike da sanyi yace.
“Kai dai Jalaludden baza ka faɗa min ba kawai”.
Kai Jalaludden ya girgiza kana yace.
“Um-um iya abinda naji kenan, kasan na faɗa maka bansan gaibu ba Allah ne kaɗai mafi sanin gaibu”.
Kai Moddibo ya jinjina cikin gamsuwa da maganarsa yace.
“Toh shikenan”.
Washe gari Litinin ya kama kwanan Moddibo biyar kenan acikin Masarautar Mouley.
Misalin ƙarfe tara na safe Moddibo ne zaune acikin tangamemen Falon kamar yanda ya saba ko yaushe yaji an buɗe ƙofar falon anutse ya ɗaga kyawawan idanunsa tare da kallon ƙofar.
Idanunsa suka sauƙa akan.
Didi da Sarki Youseef Mouley sai wani kyakykyawan Matashi mai masifar kama dashi kallo ɗaya ya masa ya fahimci shine Ibraahim ƙaninsa ne da Didi ke yawan bashi labarinsa duba da kamannin dake tsakanin su. Sai kuma Lalla Khadijah da Lalla Hafsat, sai ƴar auta Rahama.
Ibraahim kuwa yalwataccen murmushi ya sakar masa domin shi yakasance mutum ne mai fara'a da son Mutane kana da abin dariya
Suna haɗa ido da Moddibo ya ƙara fara'ar fuskarsa kana ya tafi cikin sassarfa ya rungumeshi yana mai jin farin ciki da nutsuwa agaba ɗaya ilahirin jikinsa cike da shauƙi ya ɗago kansa kana yace.
“Yaya zance maka? Ko kuma Usaini? ko kuma Hassan ɗina?”.
Moddibo kuwa lokaci ɗaya ya tsinci kansa da ƙaunar yaron aransa rungumesa yayi kana cikin ɗan sakin fuska yace.
“Koma me ka kirani dashi zan amsa”.
Sai kuma suka sake rungume juna yayin da ƙaunar junansu ke ratsa ko wani lungu da saƙon dake jikinsu...
Cikin tsanananin so da ƙauna Lalla Khadijah tace.
“Kai Ibraahim ka sakeshi haka mana”.
Kalla Hafsat dake ruggume da ɗiyarta ce tayi dariya tare da zama tana kiciniyar bawa baby nono, tace.
“Ai dai kam ya maƙaleshi kamar ya fimu sonshi”.
Didi da Abualeey kam kallonsu kawai suke cike da jin daɗi mata misaltawa.
Rahama kuwa cikin tura baki ta harari Ibrahim cikin yanayin tsamar saƙo-da saƙo tace.
“Ai shi haka yake ga yadda ya maƙaleshi kamar shine auta”.
Cikin jin daɗi Abualeey yace.
“Toh mu zauna dai kafin ai ta yiwa Ibraahim ƙorafi”.
Shiko Ibraahim signal yayiwa Rahama tare da cewa.
“Ai shi nawane ni kaɗai ba dama cewa kike nine bani da ɗan uwaba toh Allah ya dawo min da ƴaƴana dama yafi Yayunki kyau”.
Lalla Khadijah ce ta ɗan zuggure ƙayarsa.
Ɗan tsalle yayi tare da
ɗago kansa ya kallin Moddibo kana yace.
“Kaga abinda suke minko ko Yah Aleey”.
Murmushi Modibbo yayi tare da ɗan janye jikinshi gefe yana mai kallonsu ɗaya bayan ɗaya yakejin sonsu da ƙaunarsu na ratsa mishi zuciya.
Shi kuwa Ibraahim baki ya ɗan tura tare da cewa.
“Kayi haƙuri ɗan uwana”.
“A kan me?”. Modibbo ya jefa mishi tambayar.
da sauri yace.
“Sabida rashin dawowata da wuri, sabida ranar da kazo ranar na tafi Turkiyya dan daga nan muke kai musu dabino, toh nike wakiltan lamarin, koda Lalla Hafsat ta gaya min ji nayi kamar inyi fiffige in dawo gashi naga dan ban dawo da wuriba kamar kafi sonsu a kaina”.
Dariya sukayi baki daya.
Sai kuma duk suka tsagaita tare da zubawa Modibbo ido ganin yadda yake dariya tare da shafa kan Ibraahim dan ganinshi yake kamar Bashir.
Didi kuwa da su Kalla Hafsat murmushi dukeyi ganin yadda ya jawo Ibraahim ya ruggumeshi yana mai cewa.
“Waya ce maka nafi sonsu, suda zasu koma gidajensu su barmu tare”.
Cikin dariya yayi musu gwala.
Rahama kuwa ɗan rawa tayi tare da faɗin.
“Ni dai muna tare”.
Shi kuwa Ibraahim
juyowa ya kalli Didi da Abualeey tare da cewa.
“Dan Allah Didi ku aurar da ita ta bar mana gida mu sake".
Baki ta tura tare da cewa.
“Ba ruwanka da ni”.