Sashe 40
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Acan Gembila kuwa adai-dai wannan lokacin Mommy ce zaune abakin gadon Khausar yayinda Khausar da Asma'u ke tsakiyar gadon cikin dariya Mommy ta gyara zaman wayar dake kunnenta kana tace.
“Yau dai Ummi kiyi haƙuri nice na hana Asma'u dawowa kuma Khausar ce ta hana dan Allah kiyi haƙuri ki barta ta kwana, kinsan abokin kuka shi ake faɗawa mutuwa”.
Murmushi Khausar tayi tana kallon Mommy.
Still Mommy na Dariya tace.
“Shiyasa nace bari in kiraki in Faɗa miki kuma ɗazu nayi ta kiran wayarki yana shiga ba'a ɗauka sai yanzun”.
Acan ɓangaren Ummi kuwa murmushi tayi cikin yanayin sakin fuska da jin daɗi tace.
“Laa bakomai ai lokacin da kika kira ina tare da Babansu ne kuma nabar wayar aɗakina muna tatauna batun Khausar ne sai yanzu dana shiga ɗaki naga miss call ɗinki na kira”.
Murmushi Mommy tayi cikin jin daɗi tace.
“Toh Nagode Insha Allah zamu kwana gobe zata dawo”.
Khausar dake gefe tayi ƙasa da murya kana tace.
“Mommy kice mata dan Allah goben ma sai da daddare zata dawo zamu sake yini”.
Dariya Ummi dake jiyo sautin muryar Khausar tayi kana tace.
“Ai kwana ya isa basai anyini ba”.
Karɓan wayar Khausar tayi tare da langwaɓar da kai tace.
“Dan Allah Ummi idan mun kwana mu yini”.
Murmushi Ummi tayi tare da gyara rikon wayar tace.
“Ku kwana dai sannan kuzo da wuri Ina son tattaunawa dake”.
Kai Khausar ta gyaɗa kana tace.
“Toh Ummi”.
Sannan ta katse wayar.
Miƙewa Mommy tayi kasancewar girkinta bisa duk kan Alamu cikin shirin tafiya side ɗin Lamiɗo take kallon Khausar tayi kana tace.
“Toh kizo ki rufe muku ƙofa”.
Kai suka gyaɗa atare suka miƙe da Asma'u suka bi bayanta kana suka rufe kofar.
Zama Asma'u tayi akan 2sitter kallonta Khausar tayi ta shafa cikinta kana tace.
“Asma'u mai za muci ne?”.
Kai Asma'u ta girgiza kana tace.
“Wani abinci zanci Khausar bayan kinsan Maganar daya kawoni nake so muyi amma tun yamma kin ƙi ki zauna muyi”.
Langwaɓar da kai Khausar tayi cikin sanyin murya tace.
“Shiyasa nake so mukwana kinga yanzu ma Mommy Bata nan zamu sake muyi maganar mu”.
Jinjina kai Asma'u tayi tare da cewa.
“Toh shikenan”.
Ahankali Khausar ta shafa cikin tace.
“Gaskiya yunwa nake ji kema kuma naga ɗazu bakici abincin sosai ba”.
Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe kana tace.
“Toh shikenan muje kichen ɗin muga mai zamuyi”.
Suna shiga kichen Asma'u ta buɗe freezer Khausar kuwa na tsaye gefenta ganin ɗanyen kifi yasa Asma'u juyawa ta kalli Khausar kana tace.
“Toh muyi Marghi special mana”.
Kai Khausar ta gyaɗa cike da gamsuwa tace.
“Toh shikenan muyi”.
Suna aikin suna taɓa hira cikin awa ɗaya suka gama kana suka soya chips aplate Asma'u ta zuba musu sannan Khausar ta zuba musu Tea cup biyu afalo suka zauna suna ci suna kurɓan tea suna cikin ci suka ji Knowking ahankali Khausar ta kalli ƙofar tace.
“Waye”.
Haiydar dake tsaye yace.
“Nine”.
Kurɓan tea Khausar tayi tace.
“Toh lafiya har mun rufe kofa zaka zo kana mana Knowking?”.
Murmushi yayi kana yace.
“Naji ƙamshi yana ta buɗewa ne ta ko ina shiyasa nasan wani abu kuka girka Ni dai Ku sammin kawai yunwa nake ji dan nayi dogon hira”.
Hararan ƙofar Khausar tayi tare da cewa.
“Shegen kwaɗayi mutum yana nan da hanci kamar Mage duk abinda akayi baka ciki ma sai an baka”.
Dariya Asma'u tayi tare da miƙewa tashiga kichen ta ɗauki Plate ta zuba masa sauran kana ta buɗe ƙofar ta miƙa masa har ta juya yayi saurin cewa.
“Toh ni baza abani shayin bane”.
Harara Khausar ta watsa masa kana tace.
“Ohh Haiydar kinga Ni Ko Asma'u da ba kin fara bashiba”.
Murmushi Asma'u tayi tare da juyawa ta koma kichen Haiydar kuwa gwalo yayiwa Khausar kana yace.
“Oho dai abani”.
Miƙa masa Asma'u tayi bayan ta zuba.
Bayan sun kammala Asma'u tace.
“Khausar mu dan watsa ruwa mana”.
“Eh to ki fara shiga".
Cewar Khausar dake gyara zamanta.
Miƙewa Asma'u tayi tare da tattare Plate ɗin ta kai kichen kana ta dawo ta watsa ruwa bayan ta fito Khausar ma tashiga ta watsa tana fitowa ta bude Siff ta ɗauka musu sleeping dress riga da wando masu duhu ta miƙawa Asma'u ja sannan ita ta sanya fari.
Kai tsaye falon suka fito Khausar ta kunna Tv ta rage Volume Anutse Asma'u ta juya ta kalli Khausar kana cikin sanyin Murya tace.
“Khausar”.
Ahankali Khausar ta juya tare da tattara duk kan nutsuwarta zuwa gareta tace.
“Na'am”.
Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe kana tace.
“Khausar wai Maganar da naji gaskiya ne abu ya kankama wai har an ɗaura aurenku?”.
Numfashi Khausar ta fesar kana ta sunkuyar da kanta ƙasa cikin rauni ta riƙo hannun Asma'u ta mannasu da kumatunta ga mamakin Asma'u sai taga hawaye na zuba Shar-shar-shar akuncinta.
Cikin sanyi da rauni Asma'u tace.
“Haba Khausar daga na miki magana sai ki fara kuka ai mu abun farin cikine”.
Ƙasa cewa komai Khausar tayi sai hawaye da take ahankali ta fara sheshsheƙa dake fita daga ainihin zuciyarta.
Araunane Asma'u tace.
“Haba Khausar kina kuka Ni kuma ya kikeso inyi kawai daga nazo muyi magana ta tsakanin mu sai ki fara kuka ai wannan abin farin cikine ba abin kuka ba”.
Kai Khausar ta girgiza cikin rawan murya tare da ƙoƙarin hana kanta kuka tace.
“Asma'u na amince ne saboda wasiyyar da Yah Jameel ya barmin kenan, amma ke kinsani kinsan waye Moddibo kinsan yanda tsakanina dashi yake kuma ni wlh banyi zaton da sauri-sauri haka zasu liƙa mishi niba”.
Hawaye na bin kuncinta ta cigaba da cewa.
“Bansan wace irin rayuwa zanyi atare dashi ba bansan wani iri zama zanyi ba bansan wani irin ƙakubalen zan fuskanta ba amma ina cikin taraddadi da tashin hankali Asmau”.
Atake idanun Asma'u suka cika da hawaye cike da tausayin Khausar.
Araunane Khausar ta cigaba da cewa.
“Ranar ma abinda ya kaini gidanku kenan naje ne muyi maganar amma sai in rasa ta yanda zan fara maganar ta ina zan kama mgnar ma”.
Cikin matsanancin kuka da tashin hankali tace.
“Asma'u shin menene makomata Yah Jameel ya barni da nauyi mai tarin yawa inaso in wanzar masa da wasiyyar sa gashi ya kasantu to amman ni menene makomata”.
Cikin rauni da tarin damuwa Asmau tace.
“Khausar ki daina kuka in dai kin gamsu Saboda farin cikin Yah Jameel amakwancinsa kikayi to ki daina kuka na tabbatar da Yah Jameel yana raye ba zaiso kukan kiba”.
Kasa da kai Khausar tayi hawaye na cigaba da zuba daga idanunta cikin zubda hawaye Asma'u ta cigaba da cewa.
“In dai har kinyi haka saboda farin ciki da kuma Wasiyyar Yah Jameel ya bar miki toh kada kiyi Kuka Yah Moddibo ai Namiji, ke kuma macece, kuma zuciya tana son mai kyau tata mata ke kuma mace cefa cikekkiya mai ababen muradin dukkan namiji”.
Ta sauƙe Ajiyar zuciya still Hawaye na bin fuskarta ta cigaba da cewa.
“Ina da tabbaci Khausar ko Yah Moddibo muddin yaji wasiyya ce Yah Jameel ya bar miki sannan saboda wasiyyar sa kika ce kinji kin gani zaki auresa nasan bazai zalunceki ba muddin bai kyautata miki ba to bazai zalunceki ba”.
Kai Khausar ta girgiza ta tare da ƙara danne sheshsheƙan Kukan ta haka ma Asma'u cikin sauri Khausar ta fara share mata hawayen fuskarta murya na rawa Asma'u tace.
“Khausar ban san da wani irin baki zan miki godiya ba, Ubangiji Allah ya biya ki da mafi kyawun sakamako saboda wasiyyar ɗan uwana kika amince da mgnar duk da ba yayanki bane”.
Cikin sauri Khausar ta sa hannu ta rufe mata baki muryan ta na rawa tace.
“Asma'u meyesa zaki ce haka Yah Jameel kike cewa ba Yayana bane?”.
Kai Asma'u ta girgiza kana cikin raunin murya tace.
“Ba haka nake nufi ba Khausar”.
Araunane Khausar tace.
“Toh meyesa haka Yah Jameel Yayana ne kuma Malami nane sannan Al'farma ya nema ya haɗani da Allah da Manzon ranan rabuwa ta na ƙarshe da Yah Jameel”.
Sai kuma tayi saurin rufe fuskarta da tafin hannunta kana cikin rauni ta cigaba da cewa.
“Yah Jameel Yana Kuka fa Asma'u yake cemin Khausar nasa zaiyi wuya inyi tsawon rayuwa alokacin daya faɗa min hankalina ya tashi na gigice bansan lokacin da hawaye ya fara zubo minba”.
Asma'u kuwa lumshe idonta tayi tana mai jin ƙaunar Khausar aranta.
Cikin sheshsheƙa Khausar ta cigaba da cewa.
“Ganin ina kuka sai ya fara yimin dariya yana cewa dan yace min zai mutu shine xan fara kuka ai bawai dan ya faɗa yana nufin mutuwa zaiyi ba, sannan yace min akwai Alfarma da temakon da yake nema awajena”.
Ta lumshe Idanunta hawaye masu zafi suka zubo kana ta cigaba da cewa.
“Yasa na mishi al'ƙawari koda bayan ransa zan cika masa wasiyyar Asma'u kuma nayi nasa al'ƙawarin idan har ban auri Moddibo ba kenan ban cikawa Yah Jameel Wasiyyar sa banyi masa taimakonba shiyasa nace Moddibo zan aura amma ke kin sani tsoron Moddibo nake hasalima babu wacce Moddibo ya tsana arayuwar sa sama dani kinsan shi baya sona ni kuma ina tsoronsa”.
“Yau dai Ummi kiyi haƙuri nice na hana Asma'u dawowa kuma Khausar ce ta hana dan Allah kiyi haƙuri ki barta ta kwana, kinsan abokin kuka shi ake faɗawa mutuwa”.
Murmushi Khausar tayi tana kallon Mommy.
Still Mommy na Dariya tace.
“Shiyasa nace bari in kiraki in Faɗa miki kuma ɗazu nayi ta kiran wayarki yana shiga ba'a ɗauka sai yanzun”.
Acan ɓangaren Ummi kuwa murmushi tayi cikin yanayin sakin fuska da jin daɗi tace.
“Laa bakomai ai lokacin da kika kira ina tare da Babansu ne kuma nabar wayar aɗakina muna tatauna batun Khausar ne sai yanzu dana shiga ɗaki naga miss call ɗinki na kira”.
Murmushi Mommy tayi cikin jin daɗi tace.
“Toh Nagode Insha Allah zamu kwana gobe zata dawo”.
Khausar dake gefe tayi ƙasa da murya kana tace.
“Mommy kice mata dan Allah goben ma sai da daddare zata dawo zamu sake yini”.
Dariya Ummi dake jiyo sautin muryar Khausar tayi kana tace.
“Ai kwana ya isa basai anyini ba”.
Karɓan wayar Khausar tayi tare da langwaɓar da kai tace.
“Dan Allah Ummi idan mun kwana mu yini”.
Murmushi Ummi tayi tare da gyara rikon wayar tace.
“Ku kwana dai sannan kuzo da wuri Ina son tattaunawa dake”.
Kai Khausar ta gyaɗa kana tace.
“Toh Ummi”.
Sannan ta katse wayar.
Miƙewa Mommy tayi kasancewar girkinta bisa duk kan Alamu cikin shirin tafiya side ɗin Lamiɗo take kallon Khausar tayi kana tace.
“Toh kizo ki rufe muku ƙofa”.
Kai suka gyaɗa atare suka miƙe da Asma'u suka bi bayanta kana suka rufe kofar.
Zama Asma'u tayi akan 2sitter kallonta Khausar tayi ta shafa cikinta kana tace.
“Asma'u mai za muci ne?”.
Kai Asma'u ta girgiza kana tace.
“Wani abinci zanci Khausar bayan kinsan Maganar daya kawoni nake so muyi amma tun yamma kin ƙi ki zauna muyi”.
Langwaɓar da kai Khausar tayi cikin sanyin murya tace.
“Shiyasa nake so mukwana kinga yanzu ma Mommy Bata nan zamu sake muyi maganar mu”.
Jinjina kai Asma'u tayi tare da cewa.
“Toh shikenan”.
Ahankali Khausar ta shafa cikin tace.
“Gaskiya yunwa nake ji kema kuma naga ɗazu bakici abincin sosai ba”.
Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe kana tace.
“Toh shikenan muje kichen ɗin muga mai zamuyi”.
Suna shiga kichen Asma'u ta buɗe freezer Khausar kuwa na tsaye gefenta ganin ɗanyen kifi yasa Asma'u juyawa ta kalli Khausar kana tace.
“Toh muyi Marghi special mana”.
Kai Khausar ta gyaɗa cike da gamsuwa tace.
“Toh shikenan muyi”.
Suna aikin suna taɓa hira cikin awa ɗaya suka gama kana suka soya chips aplate Asma'u ta zuba musu sannan Khausar ta zuba musu Tea cup biyu afalo suka zauna suna ci suna kurɓan tea suna cikin ci suka ji Knowking ahankali Khausar ta kalli ƙofar tace.
“Waye”.
Haiydar dake tsaye yace.
“Nine”.
Kurɓan tea Khausar tayi tace.
“Toh lafiya har mun rufe kofa zaka zo kana mana Knowking?”.
Murmushi yayi kana yace.
“Naji ƙamshi yana ta buɗewa ne ta ko ina shiyasa nasan wani abu kuka girka Ni dai Ku sammin kawai yunwa nake ji dan nayi dogon hira”.
Hararan ƙofar Khausar tayi tare da cewa.
“Shegen kwaɗayi mutum yana nan da hanci kamar Mage duk abinda akayi baka ciki ma sai an baka”.
Dariya Asma'u tayi tare da miƙewa tashiga kichen ta ɗauki Plate ta zuba masa sauran kana ta buɗe ƙofar ta miƙa masa har ta juya yayi saurin cewa.
“Toh ni baza abani shayin bane”.
Harara Khausar ta watsa masa kana tace.
“Ohh Haiydar kinga Ni Ko Asma'u da ba kin fara bashiba”.
Murmushi Asma'u tayi tare da juyawa ta koma kichen Haiydar kuwa gwalo yayiwa Khausar kana yace.
“Oho dai abani”.
Miƙa masa Asma'u tayi bayan ta zuba.
Bayan sun kammala Asma'u tace.
“Khausar mu dan watsa ruwa mana”.
“Eh to ki fara shiga".
Cewar Khausar dake gyara zamanta.
Miƙewa Asma'u tayi tare da tattare Plate ɗin ta kai kichen kana ta dawo ta watsa ruwa bayan ta fito Khausar ma tashiga ta watsa tana fitowa ta bude Siff ta ɗauka musu sleeping dress riga da wando masu duhu ta miƙawa Asma'u ja sannan ita ta sanya fari.
Kai tsaye falon suka fito Khausar ta kunna Tv ta rage Volume Anutse Asma'u ta juya ta kalli Khausar kana cikin sanyin Murya tace.
“Khausar”.
Ahankali Khausar ta juya tare da tattara duk kan nutsuwarta zuwa gareta tace.
“Na'am”.
Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe kana tace.
“Khausar wai Maganar da naji gaskiya ne abu ya kankama wai har an ɗaura aurenku?”.
Numfashi Khausar ta fesar kana ta sunkuyar da kanta ƙasa cikin rauni ta riƙo hannun Asma'u ta mannasu da kumatunta ga mamakin Asma'u sai taga hawaye na zuba Shar-shar-shar akuncinta.
Cikin sanyi da rauni Asma'u tace.
“Haba Khausar daga na miki magana sai ki fara kuka ai mu abun farin cikine”.
Ƙasa cewa komai Khausar tayi sai hawaye da take ahankali ta fara sheshsheƙa dake fita daga ainihin zuciyarta.
Araunane Asma'u tace.
“Haba Khausar kina kuka Ni kuma ya kikeso inyi kawai daga nazo muyi magana ta tsakanin mu sai ki fara kuka ai wannan abin farin cikine ba abin kuka ba”.
Kai Khausar ta girgiza cikin rawan murya tare da ƙoƙarin hana kanta kuka tace.
“Asma'u na amince ne saboda wasiyyar da Yah Jameel ya barmin kenan, amma ke kinsani kinsan waye Moddibo kinsan yanda tsakanina dashi yake kuma ni wlh banyi zaton da sauri-sauri haka zasu liƙa mishi niba”.
Hawaye na bin kuncinta ta cigaba da cewa.
“Bansan wace irin rayuwa zanyi atare dashi ba bansan wani iri zama zanyi ba bansan wani irin ƙakubalen zan fuskanta ba amma ina cikin taraddadi da tashin hankali Asmau”.
Atake idanun Asma'u suka cika da hawaye cike da tausayin Khausar.
Araunane Khausar ta cigaba da cewa.
“Ranar ma abinda ya kaini gidanku kenan naje ne muyi maganar amma sai in rasa ta yanda zan fara maganar ta ina zan kama mgnar ma”.
Cikin matsanancin kuka da tashin hankali tace.
“Asma'u shin menene makomata Yah Jameel ya barni da nauyi mai tarin yawa inaso in wanzar masa da wasiyyar sa gashi ya kasantu to amman ni menene makomata”.
Cikin rauni da tarin damuwa Asmau tace.
“Khausar ki daina kuka in dai kin gamsu Saboda farin cikin Yah Jameel amakwancinsa kikayi to ki daina kuka na tabbatar da Yah Jameel yana raye ba zaiso kukan kiba”.
Kasa da kai Khausar tayi hawaye na cigaba da zuba daga idanunta cikin zubda hawaye Asma'u ta cigaba da cewa.
“In dai har kinyi haka saboda farin ciki da kuma Wasiyyar Yah Jameel ya bar miki toh kada kiyi Kuka Yah Moddibo ai Namiji, ke kuma macece, kuma zuciya tana son mai kyau tata mata ke kuma mace cefa cikekkiya mai ababen muradin dukkan namiji”.
Ta sauƙe Ajiyar zuciya still Hawaye na bin fuskarta ta cigaba da cewa.
“Ina da tabbaci Khausar ko Yah Moddibo muddin yaji wasiyya ce Yah Jameel ya bar miki sannan saboda wasiyyar sa kika ce kinji kin gani zaki auresa nasan bazai zalunceki ba muddin bai kyautata miki ba to bazai zalunceki ba”.
Kai Khausar ta girgiza ta tare da ƙara danne sheshsheƙan Kukan ta haka ma Asma'u cikin sauri Khausar ta fara share mata hawayen fuskarta murya na rawa Asma'u tace.
“Khausar ban san da wani irin baki zan miki godiya ba, Ubangiji Allah ya biya ki da mafi kyawun sakamako saboda wasiyyar ɗan uwana kika amince da mgnar duk da ba yayanki bane”.
Cikin sauri Khausar ta sa hannu ta rufe mata baki muryan ta na rawa tace.
“Asma'u meyesa zaki ce haka Yah Jameel kike cewa ba Yayana bane?”.
Kai Asma'u ta girgiza kana cikin raunin murya tace.
“Ba haka nake nufi ba Khausar”.
Araunane Khausar tace.
“Toh meyesa haka Yah Jameel Yayana ne kuma Malami nane sannan Al'farma ya nema ya haɗani da Allah da Manzon ranan rabuwa ta na ƙarshe da Yah Jameel”.
Sai kuma tayi saurin rufe fuskarta da tafin hannunta kana cikin rauni ta cigaba da cewa.
“Yah Jameel Yana Kuka fa Asma'u yake cemin Khausar nasa zaiyi wuya inyi tsawon rayuwa alokacin daya faɗa min hankalina ya tashi na gigice bansan lokacin da hawaye ya fara zubo minba”.
Asma'u kuwa lumshe idonta tayi tana mai jin ƙaunar Khausar aranta.
Cikin sheshsheƙa Khausar ta cigaba da cewa.
“Ganin ina kuka sai ya fara yimin dariya yana cewa dan yace min zai mutu shine xan fara kuka ai bawai dan ya faɗa yana nufin mutuwa zaiyi ba, sannan yace min akwai Alfarma da temakon da yake nema awajena”.
Ta lumshe Idanunta hawaye masu zafi suka zubo kana ta cigaba da cewa.
“Yasa na mishi al'ƙawari koda bayan ransa zan cika masa wasiyyar Asma'u kuma nayi nasa al'ƙawarin idan har ban auri Moddibo ba kenan ban cikawa Yah Jameel Wasiyyar sa banyi masa taimakonba shiyasa nace Moddibo zan aura amma ke kin sani tsoron Moddibo nake hasalima babu wacce Moddibo ya tsana arayuwar sa sama dani kinsan shi baya sona ni kuma ina tsoronsa”.