Sashe 6
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin raunin murya Innayi ta kalli Asma'u tare da cewa.
“Na rasa yanda zanyi da Moddibo ɗazun nan ma Abban Jameel ya fita dalilin zuwansa da yayi masa.
Nasiyya da kwantar masa da hankali shine ma muka samu ɗazun yasha kunu”.
Numfashi mai zafi Asma'u ta fesar tare da kallon Innayi tace.
“Ummi ma tace tana som ganinsa baki ɗaya ta damu da rashin zuwansa kuma koda ta kira wayarsa baya shiga bare taji muryarsa, Innayi barin shiga wajensa”.
Kai Innayi ta gyaɗa kana tace.
“Shikenan ba matsala muje”.
Miƙewa Asma'u tayi tare da nufar Sashen sa Innayi na biye da ita.
Innayin ce ta tura ƙofar falon suka shiga ahankali Idanun Asma'u suka sauƙa akan Moddibo dake zaune kan 1sitter Ƙirjinsa Rungume da Alkur'ani yayinda idanunsa ke lumshe suna tsiyayar da hawaye kana dashash-shiyar muryarsa na rera karatun Alkur'ani.
Cikin mutuwar jiki Asma'u ta zauna daga gefen ƙafafunsa Innayi kuma ta zauna daga saman kujeran.
Ganin yanda hawaye ke fita Shar-shar-shar a idanunsa yasa Asma'u fashewa da kuka mai gunji hadda sheshsheƙa.
Jin sheshsheƙan Kukan Asma'u yasa Moddibo da idanunsa ke lumshe saurin buɗewa ganin yanda Asma'u ke kuka da sheshsheƙa yasa yayi saurin sanya tafin hannunsa yashiga goge hawayen dake saman kuncinsa.
Cikin sanyi Innayi ta kallesa tare da cewa.
“Moddibo!, Moddibo!!, Moddibo!!!”.
Ahankali ya ɗago kumburarrun Idanun sa da suka jiƙe da hawaye kana Eyelashes ɗinsa sun kwanta cikin sanyi ya kalleta.
Innayi kuwa cikin tsaresa da Ido tace.
“Moddibo za kayi fushi da hukuncin Ubangiji ne?”.
Cikin sauri ya girgiza mata kai tare da cewa.
“Astagafirullah³”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe kana ta tsira masa Ido tace.
“Toh Meyesa Moddibo baka fita, baka cin abinci sannan baka walwala, kenan fushi kake da Ubangijin daya bamu Jameelu sannan ya ɗaukesa!?”.
Kai ya girgiza mata batare da yace Uffan ba!.
Cikin sanyi da rauni Innayi ta zuba masa Ido baki ɗaya Garin Jahar Taraba da maƙasar Nigeria yafi ta ranta, fesar da numfashi kana tace.
“Toh Meyesa sai dai ka ɗauki Kur'ani ka rungume kana karatu kana kuka”.
Cikin wata dashash-shiyar murya me cike da rauni da tashin hankali yace.
“Innayi mai zan fita nayi acikin garin Gembulan? Innayi da waye zan fita? Innayi baki ɗaya garin nan ya fita raina bana son garin nan na tsani garin nan garin nan ya fita min araina”.
Sai kuma ya runtse Idanunsa da ƙarfi yayin da jijiyoyin kansa suka tashi ruɗu ruɗu dasu kana zuciyarsa ta shiga bugawa da masifar ƙarfi cikin dauriya ya buɗe idanunsa da suka yi masifar Ja yace.
“Innayi duk inda na wulga acikin garin Gembulan zanga kamar J ɗina na akusa dani, shin Innayi taya zan fara fita da waye zanyi yawo da waye zanje masallaci da waye zanyi dariya da wa zan dawo gida da wa zan zauna inci abinci!?”.
Asma'u kuwa kife kanta jikin kushin ɗin da yake zaune tayi tare da fashewa da wani irin kuka tabbas sunyi rashin da baza su sake samun kwatankwacin saba sannan kuma anzalince su zalinci mai muni da raɗaɗi.
Jin yanda Asma'u ke kuka kamar ranta zai fita yasa Moddibo juyawa ya kalleta cikin sanyi da tausayinta yace.
“Asma'u ki daina kuka ki yiwa J addu'a domin shine abinda yake buƙata atare damu”.
Innayi kuwa kallonsa tayi har zuwa lokacin hawaye na zuba daga idanunsa ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.
“Toh Moddibo kaima fa kukan kake ya za ayi Asma'u ba zatayi kuka ba”.
Kallon Innayi yayi tare da lumshe idanunsa wasu hawaye masu masifar zafi suka zubo masa.
Anutse ya goge tare da cewa.
“Innayi idan har bana samu na rungume Kur'ani ina karatu ba bana samun damar hawaye suna zubo min, sannan aduk lokacin da hawayena ke zuba inaji kamar ana zare min wani abu mai nauyi ne acikin ƙoƙon raina, shiyasa nake rufe kaina ni kaɗai nayi ta kuka”.
A tausashe ya kalli Innayi data tsaresa da ido ya cije Lip ɗinsa kana yace.
“Innayi idan har banyi kuka ba menene amfanin Idanuna da hawayena? idan ban zubar dasu arashin J ba J fa Innayi J ɗina”.
Numfashi Innayi ta fesar cikin sanyi tace.
“To ai addu'a zaka yi masa Moddibo”.
Cikin dashash-shiyar muryarsa daya dishe da kuka da tashin hankali yace.
“Innayi to ai ina masa addu'a”.
Asma'u kuwa ahankali ta ɗago Idanunta dake jiƙe da ruwan hawaye ta kallesa cikin sanyi tace.
“Yah Moddibo Meyesa ka daina zuwa wajen Ummi?.
Baki ɗaya hankalinta ya tashi ta dawo kamar mara lafiya?”.
Girgiza kai yayi tare da kallonta kana cikin sanyi yace.
“Asma'u ki cewa Ummi tayi haƙuri insha Allah zan zo amma ina jin wanin irin yanayi ne taya zan kalli al'amarin tayaya zan iya zuwa wajen Ummi ba tare da J na kusa dani ba?”.
Numfashi mai zafi ya fesar da karfi kana yace.
“Baki ɗaya rayuwa tayi min ƙunci na rasa madafa, komai ya min duhu acikin duniyar nan na rasa yanda zanyi da kaina baki ɗaya na rasa yanda zan fuskanci al'amarin”.
Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe tare da fesar da nunfashi ta kallesa tare da faɗin.
“Ni dai Yah Moddibo mu tafi, idan har baka jeba Ummi na cikin tashin hankali da damuwar rashinka, koda magana da Ummi ba tayi idan ba mun matsa mata ba amma sai ta zauna shiru ita kadai afalo baki ɗaya gidan ya daina yi mana daɗi”.
Ahankali Moddibo ya taune Lip ɗinsa kana yace.
“Insha Allah zan zo ki cewa Ummi tayi haƙuri”.
Girgiza kai Asma'u tayi kana tace.
“A'a Yah Moddibo nidai gaskiya Ummi tace sai dai muje tare”.
Gyara zama Innayi tayi tare da fuskantar Moddibo cike da kulawa tace.
“Toh ka tashi kuje matuƙar kana son farin ciki da kwanciyar hankalin Ummin ka, kada ka haɗa mata ciwo biyu Moddibo kasan rashin ka awajen Ummi babban matsala ne”.
Cikin sauri Asma'u tace.
“Wallahi kuwa Yah Moddibo baki daya ƙuncin ya mana yawa, ba kai babu Yah Jameel. Baki ɗaya zuciyarmu acunkushe yake da damuwa amma ganinka zai ɗebe mana kewa”.
Cikin sanyi da rarrashi Innayi tace.
“Ka daure kaje ko hankalinsu zai kwanta kuma kaima za kaji sauki acikin ranka”.
Ta ida Maganar tare da miƙa masa key tsohuwar motar data fara saya mishi.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da karɓa kana ya miƙe cikin sanyi ya Murɗa handle din ƙofar
tare da fitowa wajen, cikin sauri ya lumshe idanunsa rabonsa da ganin haske irin haka ko kuma ya taka kofar falon yau tsawon kwana biyar kenan ko da sallah agida yake baya fita jam'i kai tsaye inda Motarsa yake ya nufa ya shiga sannan yaja suka tafi.
Innayi kuwa na ganin tafiyarsu ta kira Number Malam Arɗo bayan ya ɗaga tace.
“Dan Allah Malam Arɗo idan babu damuwa kazo ina da magana da kai”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Toh badamuwa Insha Allah zan zo”.
Modibbo kuwa suna isa memory sa ya shiga tariyo masa hoton fuskar J ɗin sa cikin sauri ya juya gefen damansa jin kamar sautin murya J ɗinsa cikin dariya yana cewa A.J tsayuwar me kakeyi Please kazo mu shiga inga Ummina kasan dai nayi missing dinta da yawa.
afili ya furta.
“J kai ko nima ainayi kewarta kuma dan na tsaya jiranka ne da tuni na taho”.
Murmushi yaga M Jameel ya sakar masa sannan ya janye hannunsa daga cikin nasa ya juya ya fara tafiya yana jujjuya masa hannu alamar Byebye.
Da sauri Moddibo ya juya tare da cewa.
“J ina kuma zaka je ba kace ka matsu kaga Ummi ba?”.
Cikin sauri Asma'u dake Kallonsa ta tashare hawayen dake kwaranya a Idanunta kana tace.
“Yah Moddibo Yah Jameel fa baya nan sannan bazai taɓa zuwa inda muke ba”.
Moddibo kuwa ido ya tsirawa Asma'u kamar mai son fahimtar abinda take faɗa sai kuma yayi saurin dafe kansa tare da maimaita Kalmar Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n shi kansa yasan zuwa zuwa yanzu dai kamar zautacce yake.
Numfashin ya fesar sannan ya nufi falon bakinsa ɗauke da Sallama Asma'u na biye dashi.
Ahankali idanunsa suka sauƙa akan Ummi dake zaune kan 3sitter ta daura guiwar hannunta duka biyu akan cinyarta tayi tagumi tare ta tsirawa waje ɗaya Ido baki ɗaya ta rame fuskarta yayi fayau.
Cikin sauri Moddibo ya ƙarasa shiga falon tare da zama agefenta kana ya janye tagumin da tayi ya maida hannunta kan gwiwoyinta.
Ummi kuwa cikin sauri ta sunkuyar da kanta nan take hawaye suka fara zuba Shar-shar-shar cikin sanyin murya ya kalleta kana yace.
“Ummi dan Allah kiyafemin. Insha Allahu bazan sake nesa dake ba, kinji Ummina ki daina zubar da hawayenki, dan baza mu iya juran. Kallon hawayen ki na zuba ba”.
Kallonsa Ummi tayi cikin wata raunan'niyar murya tace.
“Babana idan har baka zuwa wajena ya zanyi?Kana so ka haɗa min zafi biyu alokaci ɗaya ne?
Babu Jameeluna sannan kaima baka kusa dani mekake tunanin zanji arayuwata, kana so inshiga wani hali ne?”.
Cikin sauri ya girgiza mata kai kana muryarsa na rawa yace.
“Insha Allahu bazan sake nesa da keba, zan kasance atare daku tamkar yanda J ke kasancewa atare daku, zan sanya ku farin ciki tamkar yanda J ɗina ke saku insha Allah zan kiyaye”.
Ya kalli Ummi da har zuwa lokacin hawaye ke zuba a Idanunta ya ɗaura tafin hannunsa akan nata cikin rawan murya yace.
“Insha Allah zan zame muku farin ciki kuma Garkuwa kamar yanda J ɗina ya kasance agareku Ummi. Asma'u Bashir Insha Allah bazan bari hawayenku ya zuba ba tamkar yanda J ɗina baya bari su zubo ba nayi al'ƙawarin zan zame muku farin ciki zan maye muku gurbin J ɗina”.
Ya ƙarasa maganar tare da fashewa da kuka kasa rarrashin sa Ummi tayi kawai itama hawaye ya cigaba da zuba daga idanunta haka Asma'u da Bashir suka riƙa kuka harda sheshsheƙa baki daya Moddibo baya jin zai iya hana kansa kuka bare kuma ya samu kuzarin rarrashinsu hakan yasa aka rasa wanda zai rarrashi wani acikinsu.
Malam Ahmad da dawowansa kenan ya zuba musu ido cike da tausayinsu ganin yanda suke kukan kasan daga ainihin zuciyarsu yake fitowa.
Cikin sanyi malam Ahmad ya zauna gefen Ummi ya zamana yana fuskantar Moddibo, Asma'u da Bashir dake ƙasa cike da tausayawa da kuma rinƙa rarrashisu da basu baki.
“Na rasa yanda zanyi da Moddibo ɗazun nan ma Abban Jameel ya fita dalilin zuwansa da yayi masa.
Nasiyya da kwantar masa da hankali shine ma muka samu ɗazun yasha kunu”.
Numfashi mai zafi Asma'u ta fesar tare da kallon Innayi tace.
“Ummi ma tace tana som ganinsa baki ɗaya ta damu da rashin zuwansa kuma koda ta kira wayarsa baya shiga bare taji muryarsa, Innayi barin shiga wajensa”.
Kai Innayi ta gyaɗa kana tace.
“Shikenan ba matsala muje”.
Miƙewa Asma'u tayi tare da nufar Sashen sa Innayi na biye da ita.
Innayin ce ta tura ƙofar falon suka shiga ahankali Idanun Asma'u suka sauƙa akan Moddibo dake zaune kan 1sitter Ƙirjinsa Rungume da Alkur'ani yayinda idanunsa ke lumshe suna tsiyayar da hawaye kana dashash-shiyar muryarsa na rera karatun Alkur'ani.
Cikin mutuwar jiki Asma'u ta zauna daga gefen ƙafafunsa Innayi kuma ta zauna daga saman kujeran.
Ganin yanda hawaye ke fita Shar-shar-shar a idanunsa yasa Asma'u fashewa da kuka mai gunji hadda sheshsheƙa.
Jin sheshsheƙan Kukan Asma'u yasa Moddibo da idanunsa ke lumshe saurin buɗewa ganin yanda Asma'u ke kuka da sheshsheƙa yasa yayi saurin sanya tafin hannunsa yashiga goge hawayen dake saman kuncinsa.
Cikin sanyi Innayi ta kallesa tare da cewa.
“Moddibo!, Moddibo!!, Moddibo!!!”.
Ahankali ya ɗago kumburarrun Idanun sa da suka jiƙe da hawaye kana Eyelashes ɗinsa sun kwanta cikin sanyi ya kalleta.
Innayi kuwa cikin tsaresa da Ido tace.
“Moddibo za kayi fushi da hukuncin Ubangiji ne?”.
Cikin sauri ya girgiza mata kai tare da cewa.
“Astagafirullah³”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe kana ta tsira masa Ido tace.
“Toh Meyesa Moddibo baka fita, baka cin abinci sannan baka walwala, kenan fushi kake da Ubangijin daya bamu Jameelu sannan ya ɗaukesa!?”.
Kai ya girgiza mata batare da yace Uffan ba!.
Cikin sanyi da rauni Innayi ta zuba masa Ido baki ɗaya Garin Jahar Taraba da maƙasar Nigeria yafi ta ranta, fesar da numfashi kana tace.
“Toh Meyesa sai dai ka ɗauki Kur'ani ka rungume kana karatu kana kuka”.
Cikin wata dashash-shiyar murya me cike da rauni da tashin hankali yace.
“Innayi mai zan fita nayi acikin garin Gembulan? Innayi da waye zan fita? Innayi baki ɗaya garin nan ya fita raina bana son garin nan na tsani garin nan garin nan ya fita min araina”.
Sai kuma ya runtse Idanunsa da ƙarfi yayin da jijiyoyin kansa suka tashi ruɗu ruɗu dasu kana zuciyarsa ta shiga bugawa da masifar ƙarfi cikin dauriya ya buɗe idanunsa da suka yi masifar Ja yace.
“Innayi duk inda na wulga acikin garin Gembulan zanga kamar J ɗina na akusa dani, shin Innayi taya zan fara fita da waye zanyi yawo da waye zanje masallaci da waye zanyi dariya da wa zan dawo gida da wa zan zauna inci abinci!?”.
Asma'u kuwa kife kanta jikin kushin ɗin da yake zaune tayi tare da fashewa da wani irin kuka tabbas sunyi rashin da baza su sake samun kwatankwacin saba sannan kuma anzalince su zalinci mai muni da raɗaɗi.
Jin yanda Asma'u ke kuka kamar ranta zai fita yasa Moddibo juyawa ya kalleta cikin sanyi da tausayinta yace.
“Asma'u ki daina kuka ki yiwa J addu'a domin shine abinda yake buƙata atare damu”.
Innayi kuwa kallonsa tayi har zuwa lokacin hawaye na zuba daga idanunsa ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.
“Toh Moddibo kaima fa kukan kake ya za ayi Asma'u ba zatayi kuka ba”.
Kallon Innayi yayi tare da lumshe idanunsa wasu hawaye masu masifar zafi suka zubo masa.
Anutse ya goge tare da cewa.
“Innayi idan har bana samu na rungume Kur'ani ina karatu ba bana samun damar hawaye suna zubo min, sannan aduk lokacin da hawayena ke zuba inaji kamar ana zare min wani abu mai nauyi ne acikin ƙoƙon raina, shiyasa nake rufe kaina ni kaɗai nayi ta kuka”.
A tausashe ya kalli Innayi data tsaresa da ido ya cije Lip ɗinsa kana yace.
“Innayi idan har banyi kuka ba menene amfanin Idanuna da hawayena? idan ban zubar dasu arashin J ba J fa Innayi J ɗina”.
Numfashi Innayi ta fesar cikin sanyi tace.
“To ai addu'a zaka yi masa Moddibo”.
Cikin dashash-shiyar muryarsa daya dishe da kuka da tashin hankali yace.
“Innayi to ai ina masa addu'a”.
Asma'u kuwa ahankali ta ɗago Idanunta dake jiƙe da ruwan hawaye ta kallesa cikin sanyi tace.
“Yah Moddibo Meyesa ka daina zuwa wajen Ummi?.
Baki ɗaya hankalinta ya tashi ta dawo kamar mara lafiya?”.
Girgiza kai yayi tare da kallonta kana cikin sanyi yace.
“Asma'u ki cewa Ummi tayi haƙuri insha Allah zan zo amma ina jin wanin irin yanayi ne taya zan kalli al'amarin tayaya zan iya zuwa wajen Ummi ba tare da J na kusa dani ba?”.
Numfashi mai zafi ya fesar da karfi kana yace.
“Baki ɗaya rayuwa tayi min ƙunci na rasa madafa, komai ya min duhu acikin duniyar nan na rasa yanda zanyi da kaina baki ɗaya na rasa yanda zan fuskanci al'amarin”.
Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe tare da fesar da nunfashi ta kallesa tare da faɗin.
“Ni dai Yah Moddibo mu tafi, idan har baka jeba Ummi na cikin tashin hankali da damuwar rashinka, koda magana da Ummi ba tayi idan ba mun matsa mata ba amma sai ta zauna shiru ita kadai afalo baki ɗaya gidan ya daina yi mana daɗi”.
Ahankali Moddibo ya taune Lip ɗinsa kana yace.
“Insha Allah zan zo ki cewa Ummi tayi haƙuri”.
Girgiza kai Asma'u tayi kana tace.
“A'a Yah Moddibo nidai gaskiya Ummi tace sai dai muje tare”.
Gyara zama Innayi tayi tare da fuskantar Moddibo cike da kulawa tace.
“Toh ka tashi kuje matuƙar kana son farin ciki da kwanciyar hankalin Ummin ka, kada ka haɗa mata ciwo biyu Moddibo kasan rashin ka awajen Ummi babban matsala ne”.
Cikin sauri Asma'u tace.
“Wallahi kuwa Yah Moddibo baki daya ƙuncin ya mana yawa, ba kai babu Yah Jameel. Baki ɗaya zuciyarmu acunkushe yake da damuwa amma ganinka zai ɗebe mana kewa”.
Cikin sanyi da rarrashi Innayi tace.
“Ka daure kaje ko hankalinsu zai kwanta kuma kaima za kaji sauki acikin ranka”.
Ta ida Maganar tare da miƙa masa key tsohuwar motar data fara saya mishi.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da karɓa kana ya miƙe cikin sanyi ya Murɗa handle din ƙofar
tare da fitowa wajen, cikin sauri ya lumshe idanunsa rabonsa da ganin haske irin haka ko kuma ya taka kofar falon yau tsawon kwana biyar kenan ko da sallah agida yake baya fita jam'i kai tsaye inda Motarsa yake ya nufa ya shiga sannan yaja suka tafi.
Innayi kuwa na ganin tafiyarsu ta kira Number Malam Arɗo bayan ya ɗaga tace.
“Dan Allah Malam Arɗo idan babu damuwa kazo ina da magana da kai”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Toh badamuwa Insha Allah zan zo”.
Modibbo kuwa suna isa memory sa ya shiga tariyo masa hoton fuskar J ɗin sa cikin sauri ya juya gefen damansa jin kamar sautin murya J ɗinsa cikin dariya yana cewa A.J tsayuwar me kakeyi Please kazo mu shiga inga Ummina kasan dai nayi missing dinta da yawa.
afili ya furta.
“J kai ko nima ainayi kewarta kuma dan na tsaya jiranka ne da tuni na taho”.
Murmushi yaga M Jameel ya sakar masa sannan ya janye hannunsa daga cikin nasa ya juya ya fara tafiya yana jujjuya masa hannu alamar Byebye.
Da sauri Moddibo ya juya tare da cewa.
“J ina kuma zaka je ba kace ka matsu kaga Ummi ba?”.
Cikin sauri Asma'u dake Kallonsa ta tashare hawayen dake kwaranya a Idanunta kana tace.
“Yah Moddibo Yah Jameel fa baya nan sannan bazai taɓa zuwa inda muke ba”.
Moddibo kuwa ido ya tsirawa Asma'u kamar mai son fahimtar abinda take faɗa sai kuma yayi saurin dafe kansa tare da maimaita Kalmar Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n shi kansa yasan zuwa zuwa yanzu dai kamar zautacce yake.
Numfashin ya fesar sannan ya nufi falon bakinsa ɗauke da Sallama Asma'u na biye dashi.
Ahankali idanunsa suka sauƙa akan Ummi dake zaune kan 3sitter ta daura guiwar hannunta duka biyu akan cinyarta tayi tagumi tare ta tsirawa waje ɗaya Ido baki ɗaya ta rame fuskarta yayi fayau.
Cikin sauri Moddibo ya ƙarasa shiga falon tare da zama agefenta kana ya janye tagumin da tayi ya maida hannunta kan gwiwoyinta.
Ummi kuwa cikin sauri ta sunkuyar da kanta nan take hawaye suka fara zuba Shar-shar-shar cikin sanyin murya ya kalleta kana yace.
“Ummi dan Allah kiyafemin. Insha Allahu bazan sake nesa dake ba, kinji Ummina ki daina zubar da hawayenki, dan baza mu iya juran. Kallon hawayen ki na zuba ba”.
Kallonsa Ummi tayi cikin wata raunan'niyar murya tace.
“Babana idan har baka zuwa wajena ya zanyi?Kana so ka haɗa min zafi biyu alokaci ɗaya ne?
Babu Jameeluna sannan kaima baka kusa dani mekake tunanin zanji arayuwata, kana so inshiga wani hali ne?”.
Cikin sauri ya girgiza mata kai kana muryarsa na rawa yace.
“Insha Allahu bazan sake nesa da keba, zan kasance atare daku tamkar yanda J ke kasancewa atare daku, zan sanya ku farin ciki tamkar yanda J ɗina ke saku insha Allah zan kiyaye”.
Ya kalli Ummi da har zuwa lokacin hawaye ke zuba a Idanunta ya ɗaura tafin hannunsa akan nata cikin rawan murya yace.
“Insha Allah zan zame muku farin ciki kuma Garkuwa kamar yanda J ɗina ya kasance agareku Ummi. Asma'u Bashir Insha Allah bazan bari hawayenku ya zuba ba tamkar yanda J ɗina baya bari su zubo ba nayi al'ƙawarin zan zame muku farin ciki zan maye muku gurbin J ɗina”.
Ya ƙarasa maganar tare da fashewa da kuka kasa rarrashin sa Ummi tayi kawai itama hawaye ya cigaba da zuba daga idanunta haka Asma'u da Bashir suka riƙa kuka harda sheshsheƙa baki daya Moddibo baya jin zai iya hana kansa kuka bare kuma ya samu kuzarin rarrashinsu hakan yasa aka rasa wanda zai rarrashi wani acikinsu.
Malam Ahmad da dawowansa kenan ya zuba musu ido cike da tausayinsu ganin yanda suke kukan kasan daga ainihin zuciyarsu yake fitowa.
Cikin sanyi malam Ahmad ya zauna gefen Ummi ya zamana yana fuskantar Moddibo, Asma'u da Bashir dake ƙasa cike da tausayawa da kuma rinƙa rarrashisu da basu baki.