Sashe 1
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
*SAKAYYAH book 2... Page 1*
Spndeɗɗ. Baya Moddibo ya koma. Suuuuuu ya faɗi a sume, cikin sauri Lamiɗo ya tarosa, ya faɗa jikinsa cike da tashin hankali Lamiɗo yace.
“Innalillahi ya suma fa Subhanallah!”.
Cikin sauri Malam Arɗo ya ƙara sa kusa da Lamiɗo idanunsa akan Moddibo ya shiga kiran sunan sa yana faɗin.
“Moddibo!, Moddibo!!, Moddibo!!!”.
Ina tuni Moddibo ya sume babu alamar numfashi atare dashi.
Abba kuwa kansa ya ɗaga tare da kallon fuskar skeleton M Jameel kana ya maida Idanunsa ƙasa kan takalmin dake sanye aƙafarsa ahankali ya leƙa bayan idanunsa suka sauƙa akan guntun rigarsa da bai gama sauƙa daga jikin skeleton ba jinjina kansa yayi cikin wata dakakkiyar murya ya juya ya kalli Moddibo dake sume kai ya girgiza tare da sakin murmushin da yafi kuka ciwo murmushi da yafi ihu zafi, murmushin da yafi ciwo, Ciwo murmushin da yafi raɗaɗi zafi, ya saki kana ya juya ya kalli sauran mutanen dake tsaye sai ya kuma kalli fuskar skeleton tare da maida kallonsa kan yatsun hannunsa.
Cikin wata dakakkiyar murya me ɗauke da tarin raɗaɗi da ƙuna yace.
“Uhmmm Jameelu na ne”.
Kallonsa ya mayar kan Moddibo da har zuwa lokacin yake. Rungume a jikin Lamiɗo taune lips ɗinsa yayi tare da cewa.
“Kai kam Aliyu kahuta, inama ace nima zan sume ko kuma in mace ma gaba ɗaya da hakan yafi min sauƙi”.
Cikin sauri ɗaya police ɗin ya juya tare da isa gefen Abba ya riƙe sa cike da alhini da tarin tausayawa yace.
“Alhj Bashir kayi addu'a kaji”.
Kai Abba ya gyaɗa cikin wata dakakkiyar murya yace.
_“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n lahaula wala ƙuwwata Illah billahil aliyul Azhim Hasbunallahu wani'imal wakil Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha La'ilaha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal Zhalimin”_ sune Adduo'in da yake iya maimaitawa afili da kuma ransa.
Ori dake tsaye ciki ruɗu da tausayawa yayi saurin ƙarasawa gaban skeleton gawar M Jameel ya ɗauko goran ruwan kana ya dawo tare da miƙawa Lamiɗo yana mai cewa.
“Lamiɗo gashi ayayyafa masa”.
Karɓa Lamiɗo yayi kana ya buɗe tare da yayyafawa Moddibo dake kwance jikinsa amma ko kaɗan Moddibo bai motsa ba.
Kallon Buba Lamiɗo yayi kana yace.
“Ori taimaka min mu saka shi cikin Mota”.
Kai Buba ya gyaɗa.
Ɗaya daga cikin Folisawan ne yace.
“Ranka shi daɗe bari mu saka shi”.
Ya faɗa tare da kallon ɗan gidansa da Ido ya masa alamar yazo su kama Moddibo ƙarasawa yayi sannan suka ɗauki Moddibo suka sauƙa kasan dutsen, tare da sanya shi abayan Motar Malam Arɗo.
Folisawan kuwa ƙara sawa sukayi suka shiga ɗaukar hoton gawar skeleton M Jameel.
Bayan sun gama ɗauka tare yan dube-dubensu, da Babbansu da sauran suka saka handglove suka ƙarasa gaban gawar da niyyar sunjanye gawar Babbansun najan Igiyar da aka ɗauɗaureshi ƙasusuwan suka kakkarye tare da zubewa a ƙasa babu ta yanda zasu iya daukarsa Babban su ya umarci Coustable yaje ya ɗauko musu kwali abayan mota kana suka tattara gawar suka zuba acikin kwalin kana suka kwashe takalmansa da wayoyinsa suka saka awata leda.
Abba kuwa cikin wani irin yanayi ya nufi cikin jejin yana tafiya ba tare da shi kansa yasan inda ya nufaba.
Cikin sauri Lamiɗo ya nufesa tare da riƙe hannunsa cike da tausayawa yace.
“Alhj banan zamu bi ba can baya ne, hanyar kazo innu na maka hanyar da zamu bi”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da bin bayan Lamiɗo baki ɗaya baya cikin nutsuwarsa ya kasa gane shin mafarki yake ko kuma azahirance komai ke faruwa.
Bayan sun isa Lamiɗo da kansa ya buɗe masa mota yashiga sannan shima yashiga.
Folisawan kuwa kwalin da gawar M Jameel ke ciki suka ɗauka tare da sawa abayan motarsu suka tafi gida.
Abba kuwa kallon hanya kawai yake baki ɗaya baya cikin hayyacinsa ganin yanayin da yake ciki ne yasa Malam Arɗo ya fara yi masa Adduo'i yana tofa masa kana yana faɗa afili.
Ahankali Abba ya fara sakin Ajiyar zuciya kana yashiga maimaita Adduo'in sannu Ahankali ya fara jin hankalinsa ya fara dawowa jikinsa.
Motar da Moddibo ke ciki Ori da police ɗaya ne aciki direct Asibiti suka nufa dashi.
Yayin da Motar dasu Abba da kuma gawar M Jameel ke ciki kai tsaye gida suka wuce, suna isa kai tsaye falonsa suka wuce police ɗin ne ya ɗauko kwalin Gawar M Jameel ya shigo dashi kana ya ajiye agabansu.
Hajiya Turai dake sashenta tana jin tsayuwar motoci ta fito zuwa falon Abba.
Ganin Abba zaune tare dasu Lamiɗo yasa ta nufi gefen Abba cikin yanayin damuwa tace.
“Alhj lafiya ya ake ciki Gawar waye kuka samu?”.
Ahankali ya ɗago Idanunsa da suka kaɗa sukayi jawur ya kalleta kana yayi ƙasa da kansa cikin raunin murya yace.
“Gawar Jameelu na ne!”.
Arazane Hajiya Turai ta kallesa zuciyarta na bugawa da masifar ƙarfi Idanunta akansa tace.
“Gawar Jameelu kuma!?”.
Kai ya gyaɗa mata Cikin tsananin tashin hankali da ruɗu ta fashe da kuka me tsuma zuciya tana furta.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ina gawar yake?”.
Da hannu ya nuna mata kwalin dake gabansa.
Da kallo tabi kwalin cikin sauri ta sake Kallonsa Idanunta cike da ruwan hawaye tace.
“Gawar Jameelu ne acikin kwali haka?”.
Kai ya gyaɗa batare daya ɗago kaiba yace.
“Shine”.
Wani sabon kuka ta fashe dashi tana Girgiza kai Kukanta ne ya fito da Hajiya Karima itama ganin abinda ke faruwa yasa ta fashe da kuka.
Acan Asibiti kuwa ana kai Moddibo likitoci suka shiga bashi temakon Gaggawa saidai koda wasa bai farfaɗo ba ganin haka yasa suka dauƙo wani na'ura mai kama da Iron akafara danna masa aƙirji.
Amman ina babu alamun zai motsa, sosai likitocin suka dugufa wurin ganin sun cetoshi, a karo na biyu suka kuma danna mishi a ƙirjunshi, amman ina, Dr Lukman ne ya karɓi aikin tare da goggoga jikin na'urar ya manna masa a kirjinsa da ƙarfi.
Cikin ikon Allah yaja wani dogon numfashin sake dannawa yayi da karfi wani irin maraitaccen numfashi ya sake ja amma still bai farfaɗo ba sake dannawa sukayi akaro na biyar ne yaja wani dogon numfashi tare da buɗe idanunsa kana yace.
“Jyyyyyyy”.
Malam Arɗo da bai daɗe da dawowa daga gidan Abba bane, yayi saurin riƙe hannunsa tare da cewa.
“Moddibo kayi addu'a”.
Duk da cewa baya Cikin nutsuwarsa hakan bai hanashi maimaita duk wata addu'a da tazo bakinsa ba ahankali ya ɗago kansa tare da kallon Malam Arɗo yace.
“Malam J ɗina nefa!”.
Jinjina kai Malam Arɗo yayi cike da tausayawa yace.
“Eh shine Moddibo Allah ya karɓi Jameelu muyi masa addu'a Allah ya karɓi shahadarsa”.
Girgiza kai Moddibo yayi tare da cije lips ɗin sa duka biyu, kana ya runtse Idanunsa cikin wani irin yanayi mai wuya yace.
“Malam Arɗo mutuwar azaba suka masafa, ɗaure sa sukayi suka ajiye masa goran ruwan agabansa ta yanda yana ji yana gani bashi da damar sha sun barshi da azabar ƙishi”.
Kallonsa Malam Arɗo keyi cike da tausayawa yana ganin yanda zuciyarsa ke bugawa da ƙarfi.
Cikin wata raunan'niyar murya Moddibo ya cigaba da cewa.
“Malam ɗaure sa sukayi suka ajiye masa wayoyinsa agabansa ta yanda yana kallon muna kiransa bashi da damar ɗauka bare yace mukawo masa ɗauki”.
Sai kuma ya rintse idanunsa da masifan ƙarfi zuciyarsa na cigaba da buguwa da masifaffen ƙarfi kana yace.
“Ɗaure sa sukayi ta yanda yana ganin ga hanyar tsira sai dai bashi da damar kiran wani ya kawo masa ɗauki ɗaure sa fa sukayi ta yanda yana ganin kiran mu amma bashi da damar ɗauka”.
Jujjuya kansa ya farayi kamar zautacce hawaye na bin gefe da gefen idanunsa har suna shiga kunnensa cikin Muryan kuka yace.
“Ɗauresa fa sukayi ta yanda yana ganin kiran Abbansa bashi da damar ɗauka,Mutuwar azaba da raɗaɗi suka masa da ƙishi fa suka kasheshi”.
Kasa ƙarasa maganar yayi kawai ya fashe da matsanancin kuka mai tafiya da numfashi Atake numfashinsa ya ɗauke ya sake sumewa!.
Cikin sauri Malam Arɗo ya miƙe tare da kiran likitoci kana ya sanar dasu ya sake suma taruwa likitocin sukayi akansa kana suka shiga bashi temakon Gaggawa da kyar da temakon Allah suka samu ya farfaɗo ganin ya farfaɗo yasa Dr ya masa Alluran bacci Atake baccin wahala ya ɗauke sa.
Ajiyar zuciya Malam Arɗo ya sauƙe tare da miƙewa ya fita kana yayi dearling number Lamiɗo yana ɗauka yace.
“Ranka shi daɗe yaron nan fa gashi agigice yake baki ɗaya da zaran ya farfaɗo sunan Marigayi Jameelu yake kira, yana kiran sunan kuma zai sake suma!”.
Acan gidan Abba kuwa zaune yake afalonsa hannunsa riƙe da waya tunda suka dawo yake zaune awajen ya kasa koda motsawa se kwalin Gawar Jameelu daya zubawa Ido yana jujjuya wayar hannunsa ajiyar zuciya ya sauƙe tare da kiran number Ummi Yana Jin tayi picking ya fesar da numfashi kana yace.
“Fatima”.
Cike da mamaki Ummi tace.
“Abban Jameel”. Jin muryansa.
Cikin raunin murya ya sake cewa.
“Fatima”.
Anutse Ummi ta amsa da.
“Na'am”.
Runtse Idanunsa yayi kana yasake cewa.
“Fatima”.
Cikin dakiya Ummi da taji zuciyarta ya tsinke da Masifar ƙarfi tace.
“Na'am Abban Jameel ka faɗa min me yasamu Jameelu na sun kira ne ko kuma yaya!?”.
Cikin rauni yace.
“Hmmm”.
ya faɗa tare da katse kiran kana ya fito da Number Malam Ahmad.
Spndeɗɗ. Baya Moddibo ya koma. Suuuuuu ya faɗi a sume, cikin sauri Lamiɗo ya tarosa, ya faɗa jikinsa cike da tashin hankali Lamiɗo yace.
“Innalillahi ya suma fa Subhanallah!”.
Cikin sauri Malam Arɗo ya ƙara sa kusa da Lamiɗo idanunsa akan Moddibo ya shiga kiran sunan sa yana faɗin.
“Moddibo!, Moddibo!!, Moddibo!!!”.
Ina tuni Moddibo ya sume babu alamar numfashi atare dashi.
Abba kuwa kansa ya ɗaga tare da kallon fuskar skeleton M Jameel kana ya maida Idanunsa ƙasa kan takalmin dake sanye aƙafarsa ahankali ya leƙa bayan idanunsa suka sauƙa akan guntun rigarsa da bai gama sauƙa daga jikin skeleton ba jinjina kansa yayi cikin wata dakakkiyar murya ya juya ya kalli Moddibo dake sume kai ya girgiza tare da sakin murmushin da yafi kuka ciwo murmushi da yafi ihu zafi, murmushin da yafi ciwo, Ciwo murmushin da yafi raɗaɗi zafi, ya saki kana ya juya ya kalli sauran mutanen dake tsaye sai ya kuma kalli fuskar skeleton tare da maida kallonsa kan yatsun hannunsa.
Cikin wata dakakkiyar murya me ɗauke da tarin raɗaɗi da ƙuna yace.
“Uhmmm Jameelu na ne”.
Kallonsa ya mayar kan Moddibo da har zuwa lokacin yake. Rungume a jikin Lamiɗo taune lips ɗinsa yayi tare da cewa.
“Kai kam Aliyu kahuta, inama ace nima zan sume ko kuma in mace ma gaba ɗaya da hakan yafi min sauƙi”.
Cikin sauri ɗaya police ɗin ya juya tare da isa gefen Abba ya riƙe sa cike da alhini da tarin tausayawa yace.
“Alhj Bashir kayi addu'a kaji”.
Kai Abba ya gyaɗa cikin wata dakakkiyar murya yace.
_“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n lahaula wala ƙuwwata Illah billahil aliyul Azhim Hasbunallahu wani'imal wakil Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha La'ilaha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal Zhalimin”_ sune Adduo'in da yake iya maimaitawa afili da kuma ransa.
Ori dake tsaye ciki ruɗu da tausayawa yayi saurin ƙarasawa gaban skeleton gawar M Jameel ya ɗauko goran ruwan kana ya dawo tare da miƙawa Lamiɗo yana mai cewa.
“Lamiɗo gashi ayayyafa masa”.
Karɓa Lamiɗo yayi kana ya buɗe tare da yayyafawa Moddibo dake kwance jikinsa amma ko kaɗan Moddibo bai motsa ba.
Kallon Buba Lamiɗo yayi kana yace.
“Ori taimaka min mu saka shi cikin Mota”.
Kai Buba ya gyaɗa.
Ɗaya daga cikin Folisawan ne yace.
“Ranka shi daɗe bari mu saka shi”.
Ya faɗa tare da kallon ɗan gidansa da Ido ya masa alamar yazo su kama Moddibo ƙarasawa yayi sannan suka ɗauki Moddibo suka sauƙa kasan dutsen, tare da sanya shi abayan Motar Malam Arɗo.
Folisawan kuwa ƙara sawa sukayi suka shiga ɗaukar hoton gawar skeleton M Jameel.
Bayan sun gama ɗauka tare yan dube-dubensu, da Babbansu da sauran suka saka handglove suka ƙarasa gaban gawar da niyyar sunjanye gawar Babbansun najan Igiyar da aka ɗauɗaureshi ƙasusuwan suka kakkarye tare da zubewa a ƙasa babu ta yanda zasu iya daukarsa Babban su ya umarci Coustable yaje ya ɗauko musu kwali abayan mota kana suka tattara gawar suka zuba acikin kwalin kana suka kwashe takalmansa da wayoyinsa suka saka awata leda.
Abba kuwa cikin wani irin yanayi ya nufi cikin jejin yana tafiya ba tare da shi kansa yasan inda ya nufaba.
Cikin sauri Lamiɗo ya nufesa tare da riƙe hannunsa cike da tausayawa yace.
“Alhj banan zamu bi ba can baya ne, hanyar kazo innu na maka hanyar da zamu bi”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da bin bayan Lamiɗo baki ɗaya baya cikin nutsuwarsa ya kasa gane shin mafarki yake ko kuma azahirance komai ke faruwa.
Bayan sun isa Lamiɗo da kansa ya buɗe masa mota yashiga sannan shima yashiga.
Folisawan kuwa kwalin da gawar M Jameel ke ciki suka ɗauka tare da sawa abayan motarsu suka tafi gida.
Abba kuwa kallon hanya kawai yake baki ɗaya baya cikin hayyacinsa ganin yanayin da yake ciki ne yasa Malam Arɗo ya fara yi masa Adduo'i yana tofa masa kana yana faɗa afili.
Ahankali Abba ya fara sakin Ajiyar zuciya kana yashiga maimaita Adduo'in sannu Ahankali ya fara jin hankalinsa ya fara dawowa jikinsa.
Motar da Moddibo ke ciki Ori da police ɗaya ne aciki direct Asibiti suka nufa dashi.
Yayin da Motar dasu Abba da kuma gawar M Jameel ke ciki kai tsaye gida suka wuce, suna isa kai tsaye falonsa suka wuce police ɗin ne ya ɗauko kwalin Gawar M Jameel ya shigo dashi kana ya ajiye agabansu.
Hajiya Turai dake sashenta tana jin tsayuwar motoci ta fito zuwa falon Abba.
Ganin Abba zaune tare dasu Lamiɗo yasa ta nufi gefen Abba cikin yanayin damuwa tace.
“Alhj lafiya ya ake ciki Gawar waye kuka samu?”.
Ahankali ya ɗago Idanunsa da suka kaɗa sukayi jawur ya kalleta kana yayi ƙasa da kansa cikin raunin murya yace.
“Gawar Jameelu na ne!”.
Arazane Hajiya Turai ta kallesa zuciyarta na bugawa da masifar ƙarfi Idanunta akansa tace.
“Gawar Jameelu kuma!?”.
Kai ya gyaɗa mata Cikin tsananin tashin hankali da ruɗu ta fashe da kuka me tsuma zuciya tana furta.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ina gawar yake?”.
Da hannu ya nuna mata kwalin dake gabansa.
Da kallo tabi kwalin cikin sauri ta sake Kallonsa Idanunta cike da ruwan hawaye tace.
“Gawar Jameelu ne acikin kwali haka?”.
Kai ya gyaɗa batare daya ɗago kaiba yace.
“Shine”.
Wani sabon kuka ta fashe dashi tana Girgiza kai Kukanta ne ya fito da Hajiya Karima itama ganin abinda ke faruwa yasa ta fashe da kuka.
Acan Asibiti kuwa ana kai Moddibo likitoci suka shiga bashi temakon Gaggawa saidai koda wasa bai farfaɗo ba ganin haka yasa suka dauƙo wani na'ura mai kama da Iron akafara danna masa aƙirji.
Amman ina babu alamun zai motsa, sosai likitocin suka dugufa wurin ganin sun cetoshi, a karo na biyu suka kuma danna mishi a ƙirjunshi, amman ina, Dr Lukman ne ya karɓi aikin tare da goggoga jikin na'urar ya manna masa a kirjinsa da ƙarfi.
Cikin ikon Allah yaja wani dogon numfashin sake dannawa yayi da karfi wani irin maraitaccen numfashi ya sake ja amma still bai farfaɗo ba sake dannawa sukayi akaro na biyar ne yaja wani dogon numfashi tare da buɗe idanunsa kana yace.
“Jyyyyyyy”.
Malam Arɗo da bai daɗe da dawowa daga gidan Abba bane, yayi saurin riƙe hannunsa tare da cewa.
“Moddibo kayi addu'a”.
Duk da cewa baya Cikin nutsuwarsa hakan bai hanashi maimaita duk wata addu'a da tazo bakinsa ba ahankali ya ɗago kansa tare da kallon Malam Arɗo yace.
“Malam J ɗina nefa!”.
Jinjina kai Malam Arɗo yayi cike da tausayawa yace.
“Eh shine Moddibo Allah ya karɓi Jameelu muyi masa addu'a Allah ya karɓi shahadarsa”.
Girgiza kai Moddibo yayi tare da cije lips ɗin sa duka biyu, kana ya runtse Idanunsa cikin wani irin yanayi mai wuya yace.
“Malam Arɗo mutuwar azaba suka masafa, ɗaure sa sukayi suka ajiye masa goran ruwan agabansa ta yanda yana ji yana gani bashi da damar sha sun barshi da azabar ƙishi”.
Kallonsa Malam Arɗo keyi cike da tausayawa yana ganin yanda zuciyarsa ke bugawa da ƙarfi.
Cikin wata raunan'niyar murya Moddibo ya cigaba da cewa.
“Malam ɗaure sa sukayi suka ajiye masa wayoyinsa agabansa ta yanda yana kallon muna kiransa bashi da damar ɗauka bare yace mukawo masa ɗauki”.
Sai kuma ya rintse idanunsa da masifan ƙarfi zuciyarsa na cigaba da buguwa da masifaffen ƙarfi kana yace.
“Ɗaure sa sukayi ta yanda yana ganin ga hanyar tsira sai dai bashi da damar kiran wani ya kawo masa ɗauki ɗaure sa fa sukayi ta yanda yana ganin kiran mu amma bashi da damar ɗauka”.
Jujjuya kansa ya farayi kamar zautacce hawaye na bin gefe da gefen idanunsa har suna shiga kunnensa cikin Muryan kuka yace.
“Ɗauresa fa sukayi ta yanda yana ganin kiran Abbansa bashi da damar ɗauka,Mutuwar azaba da raɗaɗi suka masa da ƙishi fa suka kasheshi”.
Kasa ƙarasa maganar yayi kawai ya fashe da matsanancin kuka mai tafiya da numfashi Atake numfashinsa ya ɗauke ya sake sumewa!.
Cikin sauri Malam Arɗo ya miƙe tare da kiran likitoci kana ya sanar dasu ya sake suma taruwa likitocin sukayi akansa kana suka shiga bashi temakon Gaggawa da kyar da temakon Allah suka samu ya farfaɗo ganin ya farfaɗo yasa Dr ya masa Alluran bacci Atake baccin wahala ya ɗauke sa.
Ajiyar zuciya Malam Arɗo ya sauƙe tare da miƙewa ya fita kana yayi dearling number Lamiɗo yana ɗauka yace.
“Ranka shi daɗe yaron nan fa gashi agigice yake baki ɗaya da zaran ya farfaɗo sunan Marigayi Jameelu yake kira, yana kiran sunan kuma zai sake suma!”.
Acan gidan Abba kuwa zaune yake afalonsa hannunsa riƙe da waya tunda suka dawo yake zaune awajen ya kasa koda motsawa se kwalin Gawar Jameelu daya zubawa Ido yana jujjuya wayar hannunsa ajiyar zuciya ya sauƙe tare da kiran number Ummi Yana Jin tayi picking ya fesar da numfashi kana yace.
“Fatima”.
Cike da mamaki Ummi tace.
“Abban Jameel”. Jin muryansa.
Cikin raunin murya ya sake cewa.
“Fatima”.
Anutse Ummi ta amsa da.
“Na'am”.
Runtse Idanunsa yayi kana yasake cewa.
“Fatima”.
Cikin dakiya Ummi da taji zuciyarta ya tsinke da Masifar ƙarfi tace.
“Na'am Abban Jameel ka faɗa min me yasamu Jameelu na sun kira ne ko kuma yaya!?”.
Cikin rauni yace.
“Hmmm”.
ya faɗa tare da katse kiran kana ya fito da Number Malam Ahmad.