← Book details Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 63 OF 150

Sashe 63

Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Asma'u kuwa hannu ta miƙawa Dije dake gefenta suka tafa cikin yanayin farin ciki Dije tace.
“Asmeey kinga wata Madarar soyayya kamar a Indi'a muke, lallai na yarda cewa Ustazan nan sunfi kowa iya soyayya”.
Kai Asma'u ta jinjina tana mai binsu da kallon sha'awa yayin da aranta take musu addu'ar samun dawwa-Mam-miyar farin ciki tace.
“Ai kam ko tattabaru bazasu gwadawa su Khausy zama da junaba, kinaga wani irin mayataccen kallon da Yah Modibbo keyi mata, ko me yake gaya mata?”.
Da sauri Aseeya tace.
“Sai Allah gashi dai tun ɗazu suketa wani ƙus-ƙus ji Khausar yadda take lumshe ido”.
Dariya sukayi dukansu

Zakariyya kuwa cikin sarawa salon Modibbo ya ɗan sunkuyo daf da kunne Moddibo kana yace.
“Dan Allah ka riƙa tunawa, cikin mutane da kuke.
Na lura gaba ɗaya ka zauce ƙa kauce hanya baki ɗaya, ka wani gigice daga ganin yarinya kana ƙoƙarin taɓarewa acikin tsakiyar taron al'umma duk kuma wani narkewa”.
Khausar kam kanta na ƙasa Zakariyya kuwa cike da sheƙiyanci ya cigaba da cewa.
“A cikin Family fa kake ba cikin falonku kuke ba”.
Shi kuwa Modibbo Numfashi ya sauƙe mai nauyi A ransa yace.
ohhh ni Aliyu na lura Zakariyya magana ne abakinsa shida. Dr Jameel sai dai Allah ya shirye su.

Hannunsa na dama yasa ya damƙe nata da ƙarfi, sai ya zama na kamar sunayin musabaha ne.
Sai kuma yayi shiru tare da rintse idanunsa da sanya haƙoransa ya cije gefen lips ɗinsa na ƙasa kana ya sunkuyar da kansa ƙasa, wani irin abu yake ji tun daga tsakiyan maɗigan ƙwaƙwalwar kansa, har zuwa tsakiyar tafin ƙafarsa, lokaci ɗaya yaji gangar jikinsa ya fara tsuma baki ɗaya jikinsa ya fara tsuma amma ta ciki yanda babu wanda zai fahimta sai shi...

Ibraahim ne ya tsugunna kansa tare da faɗin.
“Bismillah Yah Aleey, Continue”.
Jin muryan Ibraahim yasa ya fesar da sanyayyan numfashi sai alokacin ya fara dawowa hayyacinsa.
Ahankali ya buɗe Idanunsa da suka kaɗa sukayi Jawur ya kalli Khausar yana mai jan wani dogon numfashi da ɗan ƙarfi ya sauƙe numfashin kana ya ɗago idanu ya kalleta.
Da sauri ta fito da idanunta waje ganin yanda ƙwayar idanunsa suka sauya launi baki ɗaya.
Khausar kuwa ahankali tace.
“Ayyah kasake min hannu na zafi”.
Numfashi ya fesar tare da sakin hannu kana ya kamo yatsunta.
Didi dake tsaye ta dauki wani ƙyalle me kyau kamar farko ta miƙa masa karɓa yayi kana ya goge mata tafin hannun zuwan ƴan saffa-saffa yatsunta.

Rahma kuwa kaskon turaren wuta dake fitar da wani Masifeffen ƙamshi ta miƙa masa.
Ƙamshin da ya fara gigita masa tunaninsa lokaci ɗaya ya fara jin wani irin yanayi yana game masa gangar jikinsa da ruhinsa baki ɗaya.
Kaskon turaren wutan ya ɗaura akansa kasancewar gindin Kaskon nada faɗi sai ya kamo hannayenta ya kife akai.
Ahankali hayaƙin turaren wutan ke ratsa yatsunta yana buga fuskanta.

Mai busa Algaita ne ya cigaba da busawa dare da haɗawa da kirari.
Sarkin Zaƙi kuwa hura Microphone yayi tare da cewa.
“Idan akwai ƙanin Amarya ko ƙanwar amarya ta fito, ta amshi kaskon bisa al'adarmu”.
Cikin sauri Haiydar dake ta faman Video ya miƙe ya fita kana ya zare Kaskon turaren wutan kasancewar haka Al'adarsu take.
Shi kuwa Haiydar sunkuyowa kan Khausar yaui tare da faɗin.
“Kai Addah Khausi kunyi kyau.
Kinga yanda kika zama kamar wata acikin taurari baki ɗaya ke kike haska wajen nan”.
Kallonsa tayi cikin yanayi gajiya, sai kuma ta ɗan hararesa kana tace.
“Dole mana kace haka tunda ni kaɗai ce ƴar Uwarka”.
Murmushi yayi kana cikin gaskiya da gaskiya yace.
“Wallahi ba haka bane Addah Khausy kinyi masifar kyau fa”.
Ya ida maganar tare da miƙawa Jakadiya Kaskon.
Jakadiya kuwa da ido ta yiwa Moddibo alamar ya tashi ya koma kan kujera.
Kai ya gyaɗa tare da komawa mazauninsa.
Haka ma Didi da yayunsa suka koma wajen zamansu...
Sarkin Zaƙi kuwa cike da rakaɗi yace.

“Alhamdulillah da wannan al'adar tamu mu kazo ƙarshen wannan taro na yau, sai kuma gobe idan Allah ya kaimu bisa dai da lafiya, za'a fitar da Aleeyu Youseep Muhammad Mouley atsakiyar fada, domin gabatar dashi atsakiyan Fada a matsayinsa na sarki mai jiran gado”.
Daga nan aka tashi kasancewar ƙofofine da dama cikin falon, yasa lokaci ɗaya duk aka fita cikin nutsuwa batare da wani cunkuso ba duk da kuwa yawan mutanen.

Acan ɓangaren Innayi kuwa cikin sauri ta nufi wajensu Moddibo tare da riƙe hannun Khausar ta juya.
Moddibo kuwa baki ɗaya Cousing Brother's ɗin sa ne suka riƙa bashi hannu suna rungumesa cike da ƙaunarsa tare da gabatar mishi da sunayensu da dangatakar su.
Shima cikin yalwataccen farin ciki yake rungunarsu.
Kafaɗarsa Zakariyya ya dafa tare da faɗin.

Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta abinki cikin Salamah 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP NUMBER'N 09097853276, in tura miki ki karanta abinki salamun Salam.

By
*GARKUWAR MARUBUTA**SAKAYYAH book 2... Page 17*

Na
*Aysha Aliyu Garkuwa*

Assalamu alaikum mutanan arziki masoya kamshi ma abota kamshi Amaren kamshi masu jargon kamshi Yammata wadanda sukasan darajar kamshi ni Aysha Aliyu Garkuwa na kawo muku tallan wasu Amintattun turarukana masu matukar kamshi da Kama jiki
Masu saukin farashi sannan ga biyan bukata
Yarhjya_incense_and_more
Ta shirya tsaf domin ta gwangwajeku da Turaruka na alfarma
Farar khumrah
Bakar khumrah
Turaren Wanka
Oil 6ml 1
Oil 12ml 1
Turaren fesawa 100ml 24 hours guda 1
Duka Akan 8k kacal
Sannan kayanta suna tafiyane da guarantee duk wacce tasiya taji babu kamshin nan na alfarma ko kuma basuda lasting to tayi alkawarin mayar muku da kudinku
Wannan garabasar zata kare on 5th September insha Allah
Ku hanzarta ku mallaki naku domin kayan yarhjya babu Danasani a cikinsa saidai kuyi alfahri da siyan kayanta
Account number 1419787445 Amina Umar usman access bank
Kitura evidence of payment to
08092664954
Kuyi saving number TA domin ci gaba da ganin Turaruka Kala Kala
Normal price
Bakar khumrah 1500
Farar khumrah 2k
Turaren Wanka 1500
Oils 6ml 800
Oils 12ml 1500
Turaren fesawa 100ml 3500
Turaren fesawa 50ml 2k
Kayanmu available ne a koda Yaushe
Akwai turarukan wuta na jiki na Kaya Dana daki duka sai Wanda kika zaba

“Kazo mu koma ciki Maghriba tayi muje muyi alwala mu tafi masallaci”.
Cikin gamsuwa ya gyaɗa kai,
Ibraahim kuwa hannun Moddibo ya riƙe tare da faɗin.
“Yah Aleey daga yanzu zaka riƙa zuwa jam'i yanda kake buri da fata da marari”.
Sanyayyan numfashi Moddibo ya fesar kana yace.
“Alhamdulillah, dan babu abinda nafi bege kamar zuwa sallah jam'i da kuma Innayi na”.
Ya ida maganar tare da bin bayan Ibraahim suka fara tafiya.
Tuni ƴan Uwa sun fiffita falon ya rage babu mutane sai ɗaɗ-ɗaya.
Innayi dake riƙe da hannu Khausar ta nufi wajensu Ummi tare da faɗin.
“Kuzo mu koma masauƙinmu sai kuma gobe idan Allah ya kaimu, za'a cigaba da hidima”.

Sheikh Jabeer kuwa da kansa ya nufi inda su Abban Jameel ke zaune yace.
“Kuzo mu tafi Maghriba ta ƙara to”.
Kai suka gyaɗa kana suka miƙe suka bi ta ɗaya ƙofar suka tafi.
Moddibo da su Ibraahim kuwa a hankali suke tafiya cikin nitsuwa auka shiga Corridor da zai sada su da falon Side da suke.

Su Khausar kuwa sun fara haurawa kan steps din.
Asma'u ta juya da sauri ta kalli Ummi tare da faɗin.
“Ayyah Ummi bari inje na gaida Yah Moddibo in faɗa masa saƙon Bashir”.
Ƴar dariya Ummi tayi kana tace.
“Bismillah keda ɗan Uwanki”.

Kai ta gyaɗa cikin sauri ta juya ta nufi wajensu Moddibo tana faɗin.
“Yah Moddibo! Yah Modibbo”.
Moddibo kuwa Already sun riga sun shiga falon da Dr Jameel ke ciki.

Shi kuwa Dr Jameel jiyo motsinsu ne yasa ya sassauta murya cikin wani irin yanayi da yake ciki bisa ga duk kan alamu hirar batsa suke awayar cikin lumshe idanu yace.
“Please Baby kiyi haƙuri muna cikin wani Uzuri ne fa na Fada”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Ok bye bye Amma please kazo Ina jiranka, kasan cewa kwana biyu bamu haɗu ba ina kewarka”.
Ta ida maganar tare da katse kiran.
Dr Jameel na miƙewa su Moddibo na shiga....

Cikin yanayin takaicin halayyarsa Zakariyya ya maka masa harara tare da cewa.
“Wallahi kai dai kam Jameel kayi asara, komai aka shirya da kai da zaran mace tashiga ciki saita ware ka cikin mu, musamman wannan shegiyar Baby na rasa yanda zanyi in raba ka da ita”.
Moddibo dake jinsu ne ya girgiza kai kana yace.
“Alhamdulillahi kaima kenan abin na damunka Zakariyya?”.
Kai Zakariyya ya gyaɗa yana mai cigaba da hararan Dr Jameel dake murmushi yace.
“Sosai ma kaga an tsara fitan nan dashi amma dayake shi Mamajone mayen mata, ni wlh ban na lura da lokacin daya zame ya dawo ciki ba, sai da muka shiga na gane baya tare damu”.

Sai kuma Moddibo yayi saurin juyawa jin muryan Asma'u na cewa.
“Yah Moddibo”.
Da murmushi afuskarsa yace.
“A'a Asma'u”.
Asma'u kuwa idanunta ta zare tare da ɗaura hannunta ɗaya akai kana ta buga ɗaya hannunta a ƙirjinta tare da faɗin.
“Yah Jameel”.
Tayi maganar idanunta na kan Dr Jameel dashi ma ita yake kallo.
Cikin sauri Moddibo ya juya ya kalli Asma'u sai kuma ya juya ya kalli Dr Jameel.
Chapter 63 · 0% Book details