Sashe 57
Sakayyah Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Gashin kanta dake tubke ta zubawa ido.
Sai kuma ta kalli Khausar ɗin dake tsane jikinta tare da miƙa mata.
Man shafawa, da dauko handdryer kana ta dawo ta bayanta.
Tare da fara busar mata da gashin dan ya ɗan jike. yaje mata tayi tare shafa mata mai.
Ita kuwa Khausar mai take shafawa a jikinta kusan a tare suka gama.
Ajiye handdryer ɗin Ummi tayi tare da juyowa gefen gadon inda akwatuna set ke jere, ɗaya pink ɗaya blue, wanda Ummi ce ta bada aka haɗawa Khausar ɗin Kayan lefe, kana kuma shine aka kai gidansu dangi da abokan arziƙi suka gani.
Wanda suma Hajia Bunayyah dai bata samu abin kushewa ba.
Na forkon ta buɗe wanda tun a gida Asma'u ta haɗa dukkan abin buƙata da kuma kayan da Khausar ɗin zata saka har gama bikin.
Wata Dubai Abaya Ummi ta zaro mata, Black color sai kuma zare golding color da aka yiwa rigar aiki zuɓi na musamman mai masifar kyau da ratsin fari kaɗan rigar irin mai ɗan faɗin nanne musamman daga sama. sai kuma ta zaro mata wani tattausan mondo Wanda bazai wuce iya guiwarta ba, sai bra su duka fararare, turare ta zaro kusan kala uku ta feshesu dashi. Kana ta ɗauko Kulaccar sirri wacce ta saya wurin AYSHA ALIYU GARKUWA, miƙa mata tayi tare da cewa.
Gashi ki shafa wannan.
Amsa Khausar ɗin tayi tare da cewa.
“Ayyah Ummi a tubke min gashin nan”.
To Ummin tace tare da fara tubke mata shin.
Tana gama ta nufi falo tare da cewa.
In kin gama kizo, kai kawai Khausar ɗin ta gyaɗa mata.
A can Falo kuwa Hajia Bunayyah ce ta miƙe jiki a salube ta shige ɗakin da nanne masauƙinsa inta da Aunty Hajara da kuma Aunty Ruƙayya.
Da sauri ta maida ƙofar ɗakin ta rufe tare da dannawa Hajia Lami kira a wayarta.
Bugu ɗaya ana biyu Hajia Lami ta ɗauka tare da cewa.
“Mutanen Marocco yaya akayi?”.
Cikin fesar da numfashi mai zafi Hajia Bunayyah tayi kwafa tare da cewa.
“Wllhi Allah Hajia Lami munyi babbar asara daba Samira wannan yaron ya auraba. Na rantse miki da Allah munyi asarar samun daular duniya.
Wannan shegiyar yarinya mai idanu kamar na mujiya ko yaushe suna lunshe kamar mai jin bacci anya ma kuwa ba idanun dunane da ita ba.
Kinga tayi nisa ta barmu da Naseer ɗin da ubansa ko Sarkin tasha bai taɓa samuba, ke kuwa ta bar miki ƴa da wari da yoyon ƙazanta”.
Nannauyan numfashi Hajia Lami ta fesar tare da cewa.
“Toh yanzu me abinyi?".
Cikin tsananin hasada Hajia Bunayyah ta buga hannunta da jikin gini tare da cewa.
“Wallahi Allah ni dai na rantse da Allah, sai na kashe auren nan, koda zan tafi tsirarane sai na watsa aurenan, muddin ina raye wlh Khausar bazata ji daɗin rayuwarta a gidan nan ba, idan zaki zo mu haɗa hannun da ƙarfe mu tumɓuke auren nan, mu shiga da Samira gidan to ki fara shiri, domin ina dawowa zamu bazama".
Cikin ƙeƙashewae zuciya Hajia Lami tace.
“Ai ke dai Allah ya dawo dake lafiya, Ƙawata na sama mana labarin wani ƙasurgumin boka a ƙasar Niger cikin dajin Damagaran ance min aikinshi kamar yankan wuƙane, babu haufi shi bazama ka biyaba sai buƙatar ka ta biya”.
Cikin yaƙini tace.
“Ke dai ki shirya ina dawowa zamu tafi”.
Daga nan suka katse kiran kana ta fito.
A falon kuwa da sauri su Ummi suka ƙali ƙofar falon jin sallamar Jakadiya da kuma su Lalla Khadijah da Hafsat.
Cikin sakin fuska Ummi da Innayi suka amsa tare da nuna musu wurin zama.
Zama sukayi cikin sakin fuska da cikekken fulatancinsu da suka iya ta sanadin Didi suka kalli su gaisa cikin mutumtaka.
Jakadiyace ta kalli Lalla Hafsat tare da juyowa ta kalli innayi kana tace.
“Dama yayun Aliyu ne suka zo ganin ƙanwar tasu tare da marabtanta.
Cikin jin dadi Ummi tace.
“Ayyah to babu laifi barin in kirawota”.
Sai kuma ta mike ta nufi dakin da Khausar take.
“Masha Allah diyata kinga yadda kikayi kyau kuwa". Murmushi tayi tare da rufe fuskarta da tafukan hannunta.
Ita kuwa Ummi kamo hannunta tayi ta ajiyeta tare da cewa.
Zo mu je ki gaisa da yayun Modibbo.
Da sauri ta sunkuyar da kai ganin yadda Ummi ke gyara mata tarhan da tayi da gyalen abayar sosai tayi masifar kyau ta fito cas da ita a matashiyar budurwar yar kimanin shekaru 19 zuwa 20. Duk da rigar nada faɗi bai hana kyan surar jikinta bayyana ba.
A hankali suka fito falon.
Khausar kam kanta a ƙasa take wani irin amintaccen taku mai cike da nitsuwa.
Da sauri Lalla Khadijah ta miƙe tsaye lokacin da suka iso tsakiyar falon.
Hannunta ta buɗewa Khausar tare da faɗin.
“Wow Masha Allah, Didi dai ta samu ƙarin diya wannan ai in an ganta da Rahama kai kace tagwayene". Murmushi mai yelwa Lalla Hafsat ma tayi tare da miƙawa Khausar hannun a hankali Khausar ta ɗan janye jikinta dan jikin Lalla Khadijah ta ɗan saketa.
Ruggumeta Hafsat tayi tare da cewa.
“Masha Allah, Khausar muna farin ciki da shigarki Mouley family. Allah ya baki hikima da basirar zama tsakiyar wannan Fada”.
Kusan a tare suka amsa da Amin ita kuwa Khausar yatsun hannunta take ɗan murza tare da ɗan rusunawa kana ta gaidasu.
Amsawa sukayi suna mai ƙare mata kallo. Cikin ɗan sakin fuska Hafsat tace.
“Ai wannan komai nata kamar na Rahama zaiyi mata dai-dai”.
Cikin girmamawa Jakadiyarsu tace.
“Sosai ma kuwa”. Ita kuwa Hafsat hannun Khausar ta kamo tare da cewa.
“Takalmi sise nawa kike sawa”.
Cikin sanyin murya tace.
“37”. Da sauri Khadijah tace.
“uhm jinjina sise ɗin Rahama kenan”.
Sai kuma ita Khadijah ta kamo hannun Khausar tare da ajiyeta gefen Innayi kana tace.
“Zauna abinki. Didi da Niyna sunyi miki Barka da zuwa, masarautar Mouley. Yanzu mu zamu fita ne.”
A hankali tace.
“Allah ya kiyaye hanya."
Amin sukace a tare sai kuma suka ɗan kalli Asma'u tare dayi mata murmushi suke.
“Ke me sunanki?”.
“Asma'u”.
Murmushi Khadijah tayi kana tace.
“Yauwa toh in ba matsala innayi zamu tafi da ita, ai kin san sise ɗin Khausar da kalanta ko?”.
Cikin fara'a Asma'u tace.
“Sosai ma kuwa, Nama fita sanin abinda yake mata kyau”.
Dariya sukayi ganin hararar da Khausar ta cilla mata..
Ummi kuwa murmushi kawai tayi.
Daga nan suka fita da Asma'u.
Sune basu dawoba sai gab da Maggarib.
Acan Side din da Modibbo yake kuwa.
Zaune yake shi da Ibrahim da Dr Jameel.
Cikin tsuke fuska ya kalli Dr Jameel dake zoro wayarsa daga aljihu.
“Baby”. Ya faɗa a saman lips enshi.
Sai kuma ya tsaida idonsa kan Modibbo da ya wani irin tsaresa da idanu.
A hankali yace.
“Yah dai Malam kallon nan fa?”.
Fuska Modibbo ya kuma tsukewa tare da cewa.
“Kaji tsoron Allah, Dr J kasani. Abinda kakeyi kana tafiya cikin fushin Ubangiji ne, kuma masifar zunubinka zaiyi ta bibiyarka tun anan gidan duniya, kasan cewa abinda kayiwa ƴaƴan wasu za'ayiwa ƴaƴan ka, shin me ribarka a cikin in har ka jazawa ahlinka. Ka tuna shifa zina tsananin muninsa yasa Allah baice kada kuyi zinaba, cewa yayi kadama ku kusaceshi fa. Shifa mazinaci baya zina har sai an zare mishi imaninshi. Kasan kuwa abinda Allah ya tanadarwa mazinata abinsha a cikin jahannama?”.
Cikin tsananin sanyin jiki Dr Jameel ya rumtse idanunsu tare da cewa.
“Nifa shiyasa badon Abualeey da kansa yace min dole in kasance kusa da kaina wlh bazanzoba sabida na lura kai mutumne mai tsaraɓe-tsaraɓen halal da haram”.
Cikin takaici Modibbo yace.
“Koda baka zo inda nakeba kasa a ranka in dai ina cikin ƙasarnan, sai na kasance tare da kai, na kuma yi al’ƙawari zan ƴaƙi shsiɗanin dake tare da kai, in Sha Allah sai ka dawo managarci tamkar J na”.
Murmushi Dr Jameel yayi tare da kallon hadimai guda huku da suka shigo da manyan jakukkuna guda biyar masu ɗauke da tambarin Anfaplace mall Marocco.
Da sauri Ibraahim ya miƙe tare da cewa.
“Ku shigo dasu cikin bedroom kada ku barsu a nan”.
Jin hakane yasa suka bishi a baya.
Kusan a tare suka shirya kayan cikin wodurob.
Daga bisani suka fito falon, a tsaye ya samu Dr Jameel.
“Mujeko Ibraahim”. Cewar Dr Jameel.
Kai Ibraahim ya gyaɗa tare da bin bayanshi sai kuma ya juyo ya kalli.
Moddibo dake cewa.
“Wai dan Allah Ibraahim sai yaushe za'a buɗeni in samu zuwa jam'in salla, wlh abinfa yana damuna.
Sassan numfashi Ibraahim ya fesar kana a hankali ya juyo ya dawo gaban Modibbo tare da cewa.
“Kayi haƙuri Yah Aleey in Sha Allah gobe dai a jam'i zakayi sallan magarib. Akwai babban dalilin ne da yasa ba'a barka ka fitoba.
Ƙwaffa Modibbo yayi tare da lumshe idonsa Allah ya sani suna ƙona mishi rai da batun hanashi jam'i da wotoyinsa.
Shi kuwa Ibraahim juyawa yayi yabi bayan Dr Jameel suka tafi.
Sai kuma ta kalli Khausar ɗin dake tsane jikinta tare da miƙa mata.
Man shafawa, da dauko handdryer kana ta dawo ta bayanta.
Tare da fara busar mata da gashin dan ya ɗan jike. yaje mata tayi tare shafa mata mai.
Ita kuwa Khausar mai take shafawa a jikinta kusan a tare suka gama.
Ajiye handdryer ɗin Ummi tayi tare da juyowa gefen gadon inda akwatuna set ke jere, ɗaya pink ɗaya blue, wanda Ummi ce ta bada aka haɗawa Khausar ɗin Kayan lefe, kana kuma shine aka kai gidansu dangi da abokan arziƙi suka gani.
Wanda suma Hajia Bunayyah dai bata samu abin kushewa ba.
Na forkon ta buɗe wanda tun a gida Asma'u ta haɗa dukkan abin buƙata da kuma kayan da Khausar ɗin zata saka har gama bikin.
Wata Dubai Abaya Ummi ta zaro mata, Black color sai kuma zare golding color da aka yiwa rigar aiki zuɓi na musamman mai masifar kyau da ratsin fari kaɗan rigar irin mai ɗan faɗin nanne musamman daga sama. sai kuma ta zaro mata wani tattausan mondo Wanda bazai wuce iya guiwarta ba, sai bra su duka fararare, turare ta zaro kusan kala uku ta feshesu dashi. Kana ta ɗauko Kulaccar sirri wacce ta saya wurin AYSHA ALIYU GARKUWA, miƙa mata tayi tare da cewa.
Gashi ki shafa wannan.
Amsa Khausar ɗin tayi tare da cewa.
“Ayyah Ummi a tubke min gashin nan”.
To Ummin tace tare da fara tubke mata shin.
Tana gama ta nufi falo tare da cewa.
In kin gama kizo, kai kawai Khausar ɗin ta gyaɗa mata.
A can Falo kuwa Hajia Bunayyah ce ta miƙe jiki a salube ta shige ɗakin da nanne masauƙinsa inta da Aunty Hajara da kuma Aunty Ruƙayya.
Da sauri ta maida ƙofar ɗakin ta rufe tare da dannawa Hajia Lami kira a wayarta.
Bugu ɗaya ana biyu Hajia Lami ta ɗauka tare da cewa.
“Mutanen Marocco yaya akayi?”.
Cikin fesar da numfashi mai zafi Hajia Bunayyah tayi kwafa tare da cewa.
“Wllhi Allah Hajia Lami munyi babbar asara daba Samira wannan yaron ya auraba. Na rantse miki da Allah munyi asarar samun daular duniya.
Wannan shegiyar yarinya mai idanu kamar na mujiya ko yaushe suna lunshe kamar mai jin bacci anya ma kuwa ba idanun dunane da ita ba.
Kinga tayi nisa ta barmu da Naseer ɗin da ubansa ko Sarkin tasha bai taɓa samuba, ke kuwa ta bar miki ƴa da wari da yoyon ƙazanta”.
Nannauyan numfashi Hajia Lami ta fesar tare da cewa.
“Toh yanzu me abinyi?".
Cikin tsananin hasada Hajia Bunayyah ta buga hannunta da jikin gini tare da cewa.
“Wallahi Allah ni dai na rantse da Allah, sai na kashe auren nan, koda zan tafi tsirarane sai na watsa aurenan, muddin ina raye wlh Khausar bazata ji daɗin rayuwarta a gidan nan ba, idan zaki zo mu haɗa hannun da ƙarfe mu tumɓuke auren nan, mu shiga da Samira gidan to ki fara shiri, domin ina dawowa zamu bazama".
Cikin ƙeƙashewae zuciya Hajia Lami tace.
“Ai ke dai Allah ya dawo dake lafiya, Ƙawata na sama mana labarin wani ƙasurgumin boka a ƙasar Niger cikin dajin Damagaran ance min aikinshi kamar yankan wuƙane, babu haufi shi bazama ka biyaba sai buƙatar ka ta biya”.
Cikin yaƙini tace.
“Ke dai ki shirya ina dawowa zamu tafi”.
Daga nan suka katse kiran kana ta fito.
A falon kuwa da sauri su Ummi suka ƙali ƙofar falon jin sallamar Jakadiya da kuma su Lalla Khadijah da Hafsat.
Cikin sakin fuska Ummi da Innayi suka amsa tare da nuna musu wurin zama.
Zama sukayi cikin sakin fuska da cikekken fulatancinsu da suka iya ta sanadin Didi suka kalli su gaisa cikin mutumtaka.
Jakadiyace ta kalli Lalla Hafsat tare da juyowa ta kalli innayi kana tace.
“Dama yayun Aliyu ne suka zo ganin ƙanwar tasu tare da marabtanta.
Cikin jin dadi Ummi tace.
“Ayyah to babu laifi barin in kirawota”.
Sai kuma ta mike ta nufi dakin da Khausar take.
“Masha Allah diyata kinga yadda kikayi kyau kuwa". Murmushi tayi tare da rufe fuskarta da tafukan hannunta.
Ita kuwa Ummi kamo hannunta tayi ta ajiyeta tare da cewa.
Zo mu je ki gaisa da yayun Modibbo.
Da sauri ta sunkuyar da kai ganin yadda Ummi ke gyara mata tarhan da tayi da gyalen abayar sosai tayi masifar kyau ta fito cas da ita a matashiyar budurwar yar kimanin shekaru 19 zuwa 20. Duk da rigar nada faɗi bai hana kyan surar jikinta bayyana ba.
A hankali suka fito falon.
Khausar kam kanta a ƙasa take wani irin amintaccen taku mai cike da nitsuwa.
Da sauri Lalla Khadijah ta miƙe tsaye lokacin da suka iso tsakiyar falon.
Hannunta ta buɗewa Khausar tare da faɗin.
“Wow Masha Allah, Didi dai ta samu ƙarin diya wannan ai in an ganta da Rahama kai kace tagwayene". Murmushi mai yelwa Lalla Hafsat ma tayi tare da miƙawa Khausar hannun a hankali Khausar ta ɗan janye jikinta dan jikin Lalla Khadijah ta ɗan saketa.
Ruggumeta Hafsat tayi tare da cewa.
“Masha Allah, Khausar muna farin ciki da shigarki Mouley family. Allah ya baki hikima da basirar zama tsakiyar wannan Fada”.
Kusan a tare suka amsa da Amin ita kuwa Khausar yatsun hannunta take ɗan murza tare da ɗan rusunawa kana ta gaidasu.
Amsawa sukayi suna mai ƙare mata kallo. Cikin ɗan sakin fuska Hafsat tace.
“Ai wannan komai nata kamar na Rahama zaiyi mata dai-dai”.
Cikin girmamawa Jakadiyarsu tace.
“Sosai ma kuwa”. Ita kuwa Hafsat hannun Khausar ta kamo tare da cewa.
“Takalmi sise nawa kike sawa”.
Cikin sanyin murya tace.
“37”. Da sauri Khadijah tace.
“uhm jinjina sise ɗin Rahama kenan”.
Sai kuma ita Khadijah ta kamo hannun Khausar tare da ajiyeta gefen Innayi kana tace.
“Zauna abinki. Didi da Niyna sunyi miki Barka da zuwa, masarautar Mouley. Yanzu mu zamu fita ne.”
A hankali tace.
“Allah ya kiyaye hanya."
Amin sukace a tare sai kuma suka ɗan kalli Asma'u tare dayi mata murmushi suke.
“Ke me sunanki?”.
“Asma'u”.
Murmushi Khadijah tayi kana tace.
“Yauwa toh in ba matsala innayi zamu tafi da ita, ai kin san sise ɗin Khausar da kalanta ko?”.
Cikin fara'a Asma'u tace.
“Sosai ma kuwa, Nama fita sanin abinda yake mata kyau”.
Dariya sukayi ganin hararar da Khausar ta cilla mata..
Ummi kuwa murmushi kawai tayi.
Daga nan suka fita da Asma'u.
Sune basu dawoba sai gab da Maggarib.
Acan Side din da Modibbo yake kuwa.
Zaune yake shi da Ibrahim da Dr Jameel.
Cikin tsuke fuska ya kalli Dr Jameel dake zoro wayarsa daga aljihu.
“Baby”. Ya faɗa a saman lips enshi.
Sai kuma ya tsaida idonsa kan Modibbo da ya wani irin tsaresa da idanu.
A hankali yace.
“Yah dai Malam kallon nan fa?”.
Fuska Modibbo ya kuma tsukewa tare da cewa.
“Kaji tsoron Allah, Dr J kasani. Abinda kakeyi kana tafiya cikin fushin Ubangiji ne, kuma masifar zunubinka zaiyi ta bibiyarka tun anan gidan duniya, kasan cewa abinda kayiwa ƴaƴan wasu za'ayiwa ƴaƴan ka, shin me ribarka a cikin in har ka jazawa ahlinka. Ka tuna shifa zina tsananin muninsa yasa Allah baice kada kuyi zinaba, cewa yayi kadama ku kusaceshi fa. Shifa mazinaci baya zina har sai an zare mishi imaninshi. Kasan kuwa abinda Allah ya tanadarwa mazinata abinsha a cikin jahannama?”.
Cikin tsananin sanyin jiki Dr Jameel ya rumtse idanunsu tare da cewa.
“Nifa shiyasa badon Abualeey da kansa yace min dole in kasance kusa da kaina wlh bazanzoba sabida na lura kai mutumne mai tsaraɓe-tsaraɓen halal da haram”.
Cikin takaici Modibbo yace.
“Koda baka zo inda nakeba kasa a ranka in dai ina cikin ƙasarnan, sai na kasance tare da kai, na kuma yi al’ƙawari zan ƴaƙi shsiɗanin dake tare da kai, in Sha Allah sai ka dawo managarci tamkar J na”.
Murmushi Dr Jameel yayi tare da kallon hadimai guda huku da suka shigo da manyan jakukkuna guda biyar masu ɗauke da tambarin Anfaplace mall Marocco.
Da sauri Ibraahim ya miƙe tare da cewa.
“Ku shigo dasu cikin bedroom kada ku barsu a nan”.
Jin hakane yasa suka bishi a baya.
Kusan a tare suka shirya kayan cikin wodurob.
Daga bisani suka fito falon, a tsaye ya samu Dr Jameel.
“Mujeko Ibraahim”. Cewar Dr Jameel.
Kai Ibraahim ya gyaɗa tare da bin bayanshi sai kuma ya juyo ya kalli.
Moddibo dake cewa.
“Wai dan Allah Ibraahim sai yaushe za'a buɗeni in samu zuwa jam'in salla, wlh abinfa yana damuna.
Sassan numfashi Ibraahim ya fesar kana a hankali ya juyo ya dawo gaban Modibbo tare da cewa.
“Kayi haƙuri Yah Aleey in Sha Allah gobe dai a jam'i zakayi sallan magarib. Akwai babban dalilin ne da yasa ba'a barka ka fitoba.
Ƙwaffa Modibbo yayi tare da lumshe idonsa Allah ya sani suna ƙona mishi rai da batun hanashi jam'i da wotoyinsa.
Shi kuwa Ibraahim juyawa yayi yabi bayan Dr Jameel suka tafi.