Sashe 90
Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin kiɗima ta matso kusa da Bintu, ta taɓata tare da cewa Laila kece da gaske? Bintu dai ido tasa musu saboda ita bata fahimci abinda hakan ke nufi ba ta daiji suna ambatar sunan mahaifiyar ta, Asma'u ta jawo hannun Bintu tare da cewa Hajjo wannan ba Laila bece"sai dai idan yarinyar Lailace!'Hajjo ta kamo Bintu cikin wani irin kuka mai tsanani da ban tausai,ta rungume ta,tana cewa tabbas wannan jinina ce,ko aduhu na laluba naji wannan halittar sai nagane jinina ce saboda tsarin halitta da komai babu inda ta baro Laila,ta wani bangaren kuma sak Umaru!'Bintu jin an ambaci mahaifinta yasa taji wani kuka ya ƙwace mata, Allah sarki ko a wane hali yake yanzu,tunda ta san Nafisa tana nan tana shirin kashe shi,jin hon daga waje yasa Asma'u tace"kai Hajjo ko dai tare suke da yaya Umar ne?bari na da naje na gani tunda har yanzu baya iya shigowa gidan nan kai tsaye!'ta faɗa tana figar mayafi akan igiya,ta fita cikin sauri,Hajjo kuwa kama hannun Bintu tayi ta kaita har kan tabarmar datake zaune,tare da saka ta gaba tana kallo bata fata ace mata Bintu ba jikarta bace,
Sallamar Abdallah yasa Hajjo ta dawo da hankalin ta kan bakin ƙofar tare da amsa sallamar,zubawa Abdallah ido tayi saboda hango kamannin Umar atare da shi,wani tabarmar Asma'u ta shimfiɗa masa ya zauna,idanun sa kan Bintu da yake son gano halin da take ciki, ji yake kamar bashi da lafiya saboda rashin walwalar Bintu, yarinyar da bata da batabarin damuwa tayi tasirin da zata hanata farinciki da walwala amma yanzu gaba ɗaya duk ta sauya,babu kunya Bintu ta matsa kusa dashi tare da langaɓe wuyanta a kafaɗar sa,tana ci gaba da yiwa su inno kallon rashin sani, cikin girmamawa Abdallah ya gaishe da Hajjo kana suka kuma gaisawa da Asma'u,Hajjo tace"bawan Allah daga ina duk da cewa ina maka kallon sani amma ina so kayi min bayani,amma dan Allah kar kace min wannan yarinyar ba ɗiyar Laila bace!'ta ƙarasa maganar cikin matso hawayen da suke kwarin idanunta, Asma'u ma shuru tayi ta zubawa Abdallah ido da kuma fatan jin kyakykyawan labari daga bakin sa,ɗan ajiyar numfashi Abdallah yaja tare da fesar da iskar da yacika bakin sa da ita,kana cikin nutsuwar sa da kuma salon maganarsa mai ratsa zuciya ya fara bawa Hajjo labari tun daga farkon zuwan Bintu ESTATE da irin gwagwarmayar da tasha da na nasa labarin da irin abubuwan da suka fuskan ta har kawo wannan rana da suka samu kuɓutar da Dady Abubakar daga cikin wannan ɗakin.
Wani Irin mamaki da al'ajabi da kuma tsoron duniya shi ne abinda ya riski Hajjo da Asma'u ko magana sun kasayi sai taraddadi da kuma hawayen tausayin ƴaƴan ta dakuma jikokin ta,cikin zubar hawaye tace"zo nan Batula naji ɗumin ki , ki maye min gurbin kewar mahaifanki Sulaiman da Laila!'da gudu Bintu ta waɗa jikin ta saboda yanzu ta fuskanci komai,wato wajen kakarta mahaifiyar ummin ta da fafinta Yah Abdallah ya kawota,kwanciya tayi ajikin matar da takeji kamar ta kwanta A jikin ummin ta ne,wasu hawaye masu dumi suke ta sararowa bisa kyakykyawar fuskarta,goge fuskarta Hajjo tayi kana ta gyara zaman ta cikin nuna jinjina tace"Abdallah kayi ƙoƙari kunyi ƙoƙari kuma zamu cigaba da addu'a da sadaka domin Allah ya kuma ɗora mu akan maƙiya insha Allah nasarar na garemu kamar yadda kuka kuɓutar da Abubakar da taimakon Ubangiji suma su Laila zaku kuɓutar da su da izinin Ubangiji,Ni ai yanzu hankalina yafi kwanciya kan da, saboda yanzu ina ji ajikina kamar yadda Allah ya baiyana min Bintu to zai baiyana min Sulaiman da Laila!'Asma'u ta ɗora da cewa insha Allahu rabbi ya nuna mana wannan rana!'gaba ɗaya suka amsa da Amin,Hajjo tace"yanzu mai zamu baku irin naku na ƴan gayu? ta faɗa tana kallon Abdallah da murmushi akan fuskarta,shima dan murmushin yayi tare da cewa ai Hajjo sai dai ko Bint Amma yanzu nake son juyawa ina da aiyukan da zan gabatar dasu yanzu!'Hajjo ta riƙe baki kai ɗan nan da wuri haka? amma dai ko furar garin mu ka bari na dama maka zata rage maka wani abu inyaso ko tafiya sai kayi da ita!'shuru yayi bai ce komai ba sai murmushi da ya ɗan yi,yana duban Bintu da tayi zuru tana binsu da ido,kafin Hajjo tayi magana ma tuni Asma'u ta tafi dama furar dan haka sai ta kuma dawo da duban ta kan Abdallah tana cewa, amma dai anan zaka barmin kishiyata mudan kwana biyu ko?jin jina kai yayi tare da cewa gobe zanzo mu tafi idan Allah ya kaimu!'to goben nan to babu damuwa Allah ya nuna mana ai ganin ku yafi min komai!'ganin kamar Hajjon bataji daɗi ba yasa shi cewa Hajjo karki damu indai Bint ce har sai kun gaji da ganin ta, insha Allah baza mu dawo muku nan ba sai da fafi da Ummi Laila,Kinga yanzu zaman bint bazai yuwu ba saboda akwai abubuwan dake gaban mu!'cikin gamsuwa da bayanin Abdallah Hajjo tace"karka damu na gamsu da maganarka, Allah ya baku nasara akan aiyukan ku na alheri ya kuma baiyana mana su cikin aminci shi kuma Abubakar Allah ya tashi kaɗunsa ya bashi lafiya!'amsawa sukayi da Amin cikin rangwamen damuwar da tayi kaka gida A zukatansu.
Lokacin da sukayi sallama har zai fita sai kuma ya ɗan yi jim da alamu dai akwai abinda yake son faɗa, inno tace" da akwai wani abu ne Abdullahi?cikin kwantar da murya yace"alfarma ce nake so kiyi min!'Hajjo tace"faɗi matsalar ka tsakanina da kai babu alfarma!'cikin ƙara tausasa murya yace"dan Allah Hajjo karki faɗawa Abba Umar komai kiyi shiru da bakin ki saboda ayanzu sanin sa zai iya haifar da wata babbar matsalar wan nan yazama sirrin mu har zuwa lokacin da Allah zai kawo mana ƙarshen komai!'Hajjo ta ɗan yi jim kana kuma tace" idan kana ganin hakan zaifi to babu damuwa game da hakan kuma wannan tunani ne mai kyau, insha Allah bazai san komai ba!'yauwa Hajjo na gode da fahimta!'daga haka sukayi sallama ya fita,Hajjo tace"kije kuyi sallama mana Batula!'cikin sanyin jiki Bintu tabi Abdallah wanda har ya shiga mota.
A cikin motar ta same shi shi kaɗai,sai ta tsaya daga bakin ƙofar tana kallon sa idanuwan ta har sun cicciko da ƙwalla,miƙa mata hannun sa yayi alamar ta taho a hankali ta taka ta saka hannunta cikin nasa,janyo ta yayi cikin motar,yasa hannu ya rufe kana ya juyo da fuskarta gareshi,hmm gayamin wannan kuma na meye?ya faɗa yana lakato hawayen da suka zubo mata,fadawa jikin shi tayi tana ɗan sakin wata ƴar sheshsheƙa tare da ajiyar zuciya,shafa bayan ta ya shiga yi cikin ƙoƙarin samar mata da nutsuwa yace" ko bazaki iya zama ba mutafi?ɗan tura ƙaramin bakinta tayi tana ɗan bugun saitin zuciyar sa tace"kaima ka zauna mana sai goben mu tafi tare!'zaro idanuwan sa yayi tare da cewa kai Bint ya za ayi gan sameme dani na kwanar musu agida sai kace wanda mukazo wani garin!'shuru tayi batace komai ba,ɗago fuskarta yayi tare da ɗora bakinshi kan nata,A Hankali ya shiga tsotsa kamar mayunwacin da ya kwana baici ba,sun ɗau tsawon mintuna biyu kafin ya saketa,cikin muryar sa da ta sauya yace"maza shiga gida ina kallon ki!'cikin sanyin jiki kamar bata so, haka ta fita ta shige cikin gidan tana waiwayen sa, saida yaga shigar ta kana ya kira Daniyal,yazo su tafi,sai da suka fara tafiya kana yace"gidan sirri zaka kaini!'ok sir Daniyal ya faɗa yana ƙarawa motar gudu.
Sosai fa Anty Nafisa tasa ake mata bincike akan shiga da fitar Abba Umar, wanda garin haka ne aka binciko mata gidan su Hajjo,daga nan tace yaran da tasa su aikin su duba tanaso agano mata suwaye acikin gidan,to wannan aikin ne dai ya ɗan dauki lokaci dan har yanzu jiran sakamako take,sai kuma yau katsaham da aka tashi da gobarar wan can ɗakin da itama ta daɗe tana son kai masa ziyara dan sanin ko me aka ɓoye acikin sa,ana cikin wannan jimamin kuma sai ta samu kira daga yaran da tasa suyi mata bincike,suna tabbatar mata da cewa sunga baƙin fuska sunzo gidan har mutum uku,amma dai babu Abba Umar acikin su,cikin tashin hankali tace"wane jinsi ne?yaron ya sanar mata cewa mace guda ɗaya sai maza biyu take zuciyar ta ta hau bugu,cikin rawar baki tace"lallai kuma cikin gaggawa inaso ku turomin da fuskokin su,a yau ba sai gobe ba!'daga haka ta kashe wayar tare da yin jifa da ita,tana fitar da wani irin zazzafan hucin ta shin hankali, Allah dai yasa ba shegun nan ne suka dawo ba,duk da cewa bata tunanin hakan zai tabbata amma tana matuƙar jin tsoron faruwar hakan.
Yana yawan shiga ɓangaren inno dan kawai ya duba yaga ko su Abdallah sun dawo,sai dai kuma har yanzu da lokacin ranar ya kusa wucewa shuru kake ji babu alamar dawowar su,har inno sai da taso gane wani abu atare da shi saboda yawan shigo mata yake yi duk minti bayan minti,a shigowar sa ta wajen biyar ne inno tace" wai kai lafiyar ka kuwa ɗan nan ko dai da wani abu da kake jira ko kake nema?yace"ba wani abu inno kawai dai ina ɗan duba lafiyarki ne!'ya faɗa tare da ficewa daga falon,inno ta bishi da wani mugun kallo tare da fidda wani ɗan sauti kamar irin ƙwafa ɗin nan,a bayyane ta furta cewa komai ya kusa zuwa ƙarshe ayi dai mu gani!'
Sallamar Abdallah yasa Hajjo ta dawo da hankalin ta kan bakin ƙofar tare da amsa sallamar,zubawa Abdallah ido tayi saboda hango kamannin Umar atare da shi,wani tabarmar Asma'u ta shimfiɗa masa ya zauna,idanun sa kan Bintu da yake son gano halin da take ciki, ji yake kamar bashi da lafiya saboda rashin walwalar Bintu, yarinyar da bata da batabarin damuwa tayi tasirin da zata hanata farinciki da walwala amma yanzu gaba ɗaya duk ta sauya,babu kunya Bintu ta matsa kusa dashi tare da langaɓe wuyanta a kafaɗar sa,tana ci gaba da yiwa su inno kallon rashin sani, cikin girmamawa Abdallah ya gaishe da Hajjo kana suka kuma gaisawa da Asma'u,Hajjo tace"bawan Allah daga ina duk da cewa ina maka kallon sani amma ina so kayi min bayani,amma dan Allah kar kace min wannan yarinyar ba ɗiyar Laila bace!'ta ƙarasa maganar cikin matso hawayen da suke kwarin idanunta, Asma'u ma shuru tayi ta zubawa Abdallah ido da kuma fatan jin kyakykyawan labari daga bakin sa,ɗan ajiyar numfashi Abdallah yaja tare da fesar da iskar da yacika bakin sa da ita,kana cikin nutsuwar sa da kuma salon maganarsa mai ratsa zuciya ya fara bawa Hajjo labari tun daga farkon zuwan Bintu ESTATE da irin gwagwarmayar da tasha da na nasa labarin da irin abubuwan da suka fuskan ta har kawo wannan rana da suka samu kuɓutar da Dady Abubakar daga cikin wannan ɗakin.
Wani Irin mamaki da al'ajabi da kuma tsoron duniya shi ne abinda ya riski Hajjo da Asma'u ko magana sun kasayi sai taraddadi da kuma hawayen tausayin ƴaƴan ta dakuma jikokin ta,cikin zubar hawaye tace"zo nan Batula naji ɗumin ki , ki maye min gurbin kewar mahaifanki Sulaiman da Laila!'da gudu Bintu ta waɗa jikin ta saboda yanzu ta fuskanci komai,wato wajen kakarta mahaifiyar ummin ta da fafinta Yah Abdallah ya kawota,kwanciya tayi ajikin matar da takeji kamar ta kwanta A jikin ummin ta ne,wasu hawaye masu dumi suke ta sararowa bisa kyakykyawar fuskarta,goge fuskarta Hajjo tayi kana ta gyara zaman ta cikin nuna jinjina tace"Abdallah kayi ƙoƙari kunyi ƙoƙari kuma zamu cigaba da addu'a da sadaka domin Allah ya kuma ɗora mu akan maƙiya insha Allah nasarar na garemu kamar yadda kuka kuɓutar da Abubakar da taimakon Ubangiji suma su Laila zaku kuɓutar da su da izinin Ubangiji,Ni ai yanzu hankalina yafi kwanciya kan da, saboda yanzu ina ji ajikina kamar yadda Allah ya baiyana min Bintu to zai baiyana min Sulaiman da Laila!'Asma'u ta ɗora da cewa insha Allahu rabbi ya nuna mana wannan rana!'gaba ɗaya suka amsa da Amin,Hajjo tace"yanzu mai zamu baku irin naku na ƴan gayu? ta faɗa tana kallon Abdallah da murmushi akan fuskarta,shima dan murmushin yayi tare da cewa ai Hajjo sai dai ko Bint Amma yanzu nake son juyawa ina da aiyukan da zan gabatar dasu yanzu!'Hajjo ta riƙe baki kai ɗan nan da wuri haka? amma dai ko furar garin mu ka bari na dama maka zata rage maka wani abu inyaso ko tafiya sai kayi da ita!'shuru yayi bai ce komai ba sai murmushi da ya ɗan yi,yana duban Bintu da tayi zuru tana binsu da ido,kafin Hajjo tayi magana ma tuni Asma'u ta tafi dama furar dan haka sai ta kuma dawo da duban ta kan Abdallah tana cewa, amma dai anan zaka barmin kishiyata mudan kwana biyu ko?jin jina kai yayi tare da cewa gobe zanzo mu tafi idan Allah ya kaimu!'to goben nan to babu damuwa Allah ya nuna mana ai ganin ku yafi min komai!'ganin kamar Hajjon bataji daɗi ba yasa shi cewa Hajjo karki damu indai Bint ce har sai kun gaji da ganin ta, insha Allah baza mu dawo muku nan ba sai da fafi da Ummi Laila,Kinga yanzu zaman bint bazai yuwu ba saboda akwai abubuwan dake gaban mu!'cikin gamsuwa da bayanin Abdallah Hajjo tace"karka damu na gamsu da maganarka, Allah ya baku nasara akan aiyukan ku na alheri ya kuma baiyana mana su cikin aminci shi kuma Abubakar Allah ya tashi kaɗunsa ya bashi lafiya!'amsawa sukayi da Amin cikin rangwamen damuwar da tayi kaka gida A zukatansu.
Lokacin da sukayi sallama har zai fita sai kuma ya ɗan yi jim da alamu dai akwai abinda yake son faɗa, inno tace" da akwai wani abu ne Abdullahi?cikin kwantar da murya yace"alfarma ce nake so kiyi min!'Hajjo tace"faɗi matsalar ka tsakanina da kai babu alfarma!'cikin ƙara tausasa murya yace"dan Allah Hajjo karki faɗawa Abba Umar komai kiyi shiru da bakin ki saboda ayanzu sanin sa zai iya haifar da wata babbar matsalar wan nan yazama sirrin mu har zuwa lokacin da Allah zai kawo mana ƙarshen komai!'Hajjo ta ɗan yi jim kana kuma tace" idan kana ganin hakan zaifi to babu damuwa game da hakan kuma wannan tunani ne mai kyau, insha Allah bazai san komai ba!'yauwa Hajjo na gode da fahimta!'daga haka sukayi sallama ya fita,Hajjo tace"kije kuyi sallama mana Batula!'cikin sanyin jiki Bintu tabi Abdallah wanda har ya shiga mota.
A cikin motar ta same shi shi kaɗai,sai ta tsaya daga bakin ƙofar tana kallon sa idanuwan ta har sun cicciko da ƙwalla,miƙa mata hannun sa yayi alamar ta taho a hankali ta taka ta saka hannunta cikin nasa,janyo ta yayi cikin motar,yasa hannu ya rufe kana ya juyo da fuskarta gareshi,hmm gayamin wannan kuma na meye?ya faɗa yana lakato hawayen da suka zubo mata,fadawa jikin shi tayi tana ɗan sakin wata ƴar sheshsheƙa tare da ajiyar zuciya,shafa bayan ta ya shiga yi cikin ƙoƙarin samar mata da nutsuwa yace" ko bazaki iya zama ba mutafi?ɗan tura ƙaramin bakinta tayi tana ɗan bugun saitin zuciyar sa tace"kaima ka zauna mana sai goben mu tafi tare!'zaro idanuwan sa yayi tare da cewa kai Bint ya za ayi gan sameme dani na kwanar musu agida sai kace wanda mukazo wani garin!'shuru tayi batace komai ba,ɗago fuskarta yayi tare da ɗora bakinshi kan nata,A Hankali ya shiga tsotsa kamar mayunwacin da ya kwana baici ba,sun ɗau tsawon mintuna biyu kafin ya saketa,cikin muryar sa da ta sauya yace"maza shiga gida ina kallon ki!'cikin sanyin jiki kamar bata so, haka ta fita ta shige cikin gidan tana waiwayen sa, saida yaga shigar ta kana ya kira Daniyal,yazo su tafi,sai da suka fara tafiya kana yace"gidan sirri zaka kaini!'ok sir Daniyal ya faɗa yana ƙarawa motar gudu.
Sosai fa Anty Nafisa tasa ake mata bincike akan shiga da fitar Abba Umar, wanda garin haka ne aka binciko mata gidan su Hajjo,daga nan tace yaran da tasa su aikin su duba tanaso agano mata suwaye acikin gidan,to wannan aikin ne dai ya ɗan dauki lokaci dan har yanzu jiran sakamako take,sai kuma yau katsaham da aka tashi da gobarar wan can ɗakin da itama ta daɗe tana son kai masa ziyara dan sanin ko me aka ɓoye acikin sa,ana cikin wannan jimamin kuma sai ta samu kira daga yaran da tasa suyi mata bincike,suna tabbatar mata da cewa sunga baƙin fuska sunzo gidan har mutum uku,amma dai babu Abba Umar acikin su,cikin tashin hankali tace"wane jinsi ne?yaron ya sanar mata cewa mace guda ɗaya sai maza biyu take zuciyar ta ta hau bugu,cikin rawar baki tace"lallai kuma cikin gaggawa inaso ku turomin da fuskokin su,a yau ba sai gobe ba!'daga haka ta kashe wayar tare da yin jifa da ita,tana fitar da wani irin zazzafan hucin ta shin hankali, Allah dai yasa ba shegun nan ne suka dawo ba,duk da cewa bata tunanin hakan zai tabbata amma tana matuƙar jin tsoron faruwar hakan.
Yana yawan shiga ɓangaren inno dan kawai ya duba yaga ko su Abdallah sun dawo,sai dai kuma har yanzu da lokacin ranar ya kusa wucewa shuru kake ji babu alamar dawowar su,har inno sai da taso gane wani abu atare da shi saboda yawan shigo mata yake yi duk minti bayan minti,a shigowar sa ta wajen biyar ne inno tace" wai kai lafiyar ka kuwa ɗan nan ko dai da wani abu da kake jira ko kake nema?yace"ba wani abu inno kawai dai ina ɗan duba lafiyarki ne!'ya faɗa tare da ficewa daga falon,inno ta bishi da wani mugun kallo tare da fidda wani ɗan sauti kamar irin ƙwafa ɗin nan,a bayyane ta furta cewa komai ya kusa zuwa ƙarshe ayi dai mu gani!'