Sashe 68
Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
A hankali ta buɗe bakinta ta fara da gaya masa yadda sukayi da Anty Nafisa ba tare da ta ɓoye masa komai ba,shuru tayi bata kuma cewa ko mai ba,wanda shi kuma Abdallah so yake kawai yaji ta bashi labarin ta,
Zuba mata ido yayi yana jiran jin ta ina zata fara,dan a haƙiƙanin gaskiya ya zaƙu da yaji wacece Bintu, wanda tun jiya shine aransa so yake ya tabbatar da abinda mutumin nan ya faɗa,idan har abinda ya faɗa yazo dai dai da wanda Bintun zata faɗa masa,to kuwa tabbas dole su san duk yadda zasuyi dan janyo hankalin Anty Nafisa ta buɗe musu sirrin da take ta ɓoyo, dan yana da yaƙinin cewa sirrin baya rasa na saba da Bintun,yana ji ajikin sa Nafisa itace sanadin komai,itace mafarin dukkanin abinda ya faru,dan ga dukkanin alamu tasan da zaman ɗiyar Umar ɗin,idan ba haka ba ba yadda za ayi ace ta tashi hankalinta kamar yadda Bintu ta sanar dashi,tabbas akwai lauje cikin naɗi akwai wani ɓoyayyan al amari me girma wanda ita Anty Nafisa bata son kowa ya sani, shine kuma sirrin datake muƙu-muƙun ɓoyewa,kuma da izinin Allah su sai sun sata ta faɗa ko ma meye da bakin ta,da kanta zata ɗauki wuƙa ta bur mawa cikinta,koma ace ta burma,tunda gashi bata iya aiwatar da komai batare da shawarar Bintu ba,wanda tabbas wannan wata alama ce data ke nuni da cewa ƙarshen Anty Nafisa ya zo,
"Ganin yadda ya zuba mata ido yasa tashiga ƙif-ƙifta nata idanuwan saboda ta rasa ta ina zata fara, ita sam bata iya bada dogan labari ba,wani tunani tayi a ranta wanda yasa ta ɗan kalleshi,kana cikin sanyin muryar ta tace"zan ɗauko maka deary ɗin da fafi ya bani sai ka duba,ina ga zaifi sauƙi!'ta faɗa tana lumshe idanunta,cikin alamun nuna gamsuwa da Maganar tata yace"kije ki ɗauko yanzu ina jiranki!'ya faɗa yana ɗan kwanciya jikin makarin gadon,wanda shima faɗa kawai yayi amma yasan Bintu baza ta iya fita a wannan lokacin ba,shuru tayi a wajen batare da ta motsaba,juyowa yayi yana fuskantar ta tare da yi mata alamar me take jira?tura ɗan ƙaramin bakinta tayi batare da tace"ko mai ba,har zai share ta sai kuma yaji ba zai iya ba yana so a daren nan ya karanta labarin Bintun,dan haka ya tashi yana mai zura silifas ɗin dake bakin gadon wanda akayi shi da yadin dake shimfiɗe saman gadon,tashi muje! ya faɗa yana wucewa gaba.
A hankali take bin bayan sa, wanda hakan ma ji take kamar za a ruƙota ta baya,lokacin da suka fita falon inno ne taji kamar anabin bayanta,tun tana daurewa har dai ta kumaji kamar an taɓota ta baya,cikin wani irin razana da tsinkewar zuciya ta ruƙo hannun sa yana juyowa ta faɗa jikin sa tasa hannu ta zagaye shi ta rikeshi katamau idanunta a runtse,hannu yasa ya ɗago fuskar ta,yana mamakin abinda ya tsorata ta lokaci ɗaya haka,sam taki bashi damar ganin fuskarta saboda yadda ta shigar da fuskar cikin ƙirjin shi, dalilin kusan cin su da juna ne yasa har yana iya jiyo bugun zuciyar ta wanda suke bugawa tare da tasa zuciyar, A hankali yasa hannun sa A gadon bayan ta yana ɗan partin bayan nata a hankali dan samar mata da nutsuwa,tana manne ajikin sa ya cigaba da tafiya da ita har suka kai cikin ɗakin ta,zama yayi da ita ajikin sa,cikin san yayi calming ɗin ta yace"buɗe idanunki, ki gani ba kowa mun shigo ɗakin ki,tashi ki nunan inda littafin yake!'A hankali yake mata maganar kamar wanda yake tsoran tashin jaririn da ya rasa uwar sa tashi daga baccin da yake,a tsorace ta ɗago kan nata tana bin ɗakin da ido a sace,kana cikin ƙara maƙale shi tace"yana cikin durowar can A cikin wata baƙar jaka, idan ka buɗe jakar zaka kuma ganin wata ƴar leda baƙa to aciki yake!'duk maganar nan da takeyi tuni ta daɗe da mai da kanta ta ƙunshe cikin jikin sa,ba dan Allah yayi masa ƙarfin ji bama da ba zai ji abinda take cewa ba,saboda yadda take yin maganar ƙasa ƙasa,kuma cikin tsoro.
Zuba mata ido yayi ganin bata da alamar zata sake shi yaje ya ɗauko littafin,sai aukin yi masa kwatance da takeyi,ganin lokaci sai tafiya yake basuyi abinda ya kamata ba yasa shi fara ɗan janye ta daga jikinsa, haƙura tayi ta rabu daga jikin nasa amma bata rabu da binsa kamar jela ba,har sai da yaje ya buɗe durowar da ta kwatanta masa,ya ɗauko jakar tare da buɗeta ya ɗauko ledar itama kana ya maida su inda suke ya rufe,tana ganin haka tayi saurin matsawa jikin sa wanda dama jiran sa take ya gama abinda yakeyi ta ɗora daga inda ta tsaya,duban ta yayi cikin fuskarsa da take a haɗe yace"Bint wai wannan wane irin tsorone haka?ki rage tsoron nan yayi yawa!'ya faɗa yana ɗan janye ta daga jikin sa,ba dan taso ba ta rabu da jikinsa tare da raɓe a gefe kana ganin ta zaka gane cewa a matuƙar firgice take, durowar kayanta ya bude tare da ɗauko mata kayan bacci da hijabi, kana ya kama hannunta suka fita,har suka koma ɓangaren sa jikin Bintu bai daina ɓarin tsoro ba,wanda shi Abdallah atunanin sa kawai irin tsorone irin na Bintu,amma a haƙikanin gaskiya a kwai wani abu da shi Abdallah bai sani ba.
Suna shiga ɗakin sa yasaki hannunta tare da miƙa mata kayan da ya ɗauko mata,karɓa tayi batare da ta motsa daga inda take tsaye ba,tana ta dai jujjuya kayan a hannun ta,ganin kamar bata gane abin da yake nufi ba yasa shi cewa kije ki canja kayan jikin ki idan bazaki iya yin wankan ba!'kamar wadda ƙwai ya fashewa haka take taka ƙafaunta dan zuwa toilet ɗin, zuciyar ta kuwa kamar zatayo waje saboda tsananin tsoron da ke cikinta,ƙoƙar tawa tayi ta fara karanto addu'oi bayan tashiga toilet ɗin,haka nan takejin wata kasala a cikin kwana biyun nan wanda ta rasa da lilin hakan,bata iya yin addu'oin ta yadda ya kamata, ko da ta fara sai bacci ya kamata,ga wani irin tsoron da take yawan ji,wanda ta san da ba haka take ba,duk da cewa tasan tana da tsoro amma ba kamar yadda takeji yanzu ba,cikin san dakewa da kalato jarumta ta cire kayan jikin ta,so takeyi ta ɗan yi wankan dan bazata iya bacci batare da tayi wanka ba,da tai makon addu'ar da ta samu ta zauna abakinta tayi wankan tare da ɗaura alwala kana taja ƙaramin tawul ta ɗaura ajikin ta,tana gab da fitowa taji kamar anja tawul ɗin da ta ɗaura ajikinta ta baya,ai da wani irin gudu ta ƙara sa fitowa jikinta yana wani irin rawa,
Ganin ta yayi kawai kamar anjeho ta,da gudu ta faɗa jikin sa tare da ruƙun kumeshi,zuba mata idanunsa yayi zuciyar sa cike da saƙe saƙe,anya kuwa yariyar nan lafiya take?yasan cewa tabbas Bintu tana da tsoro amma kuma bai taɓa ganin tsoron ta kamar na wannan lokacin ba,take zuciyar shi ta fara kaikawo akan wannan al'amari,jin yadda take ta shigewa cikin jikin sane yasa shi dawowa daga nazarin al'amarin da yake,cikin nutsatstsiyar Muryar sa yace"lafiyar ki kuwa? me yake damun ki haka?alokaci ɗaya ya jero mata waɗan nan tambayoyin yana mai son ganin fuskar ta, ta hanyar ƙoƙarin ɗago da kanta da ta cusa a cikin kirjin shi,
Zuba mata narkakkun idanunsa yayi A yayin da yasamu nasarar ɗago kan nata,itama kallon shi takeyi,da idanunta da suka cika da ƙwalla,cikin taushin murya yace"Bint gayamin meke damunki?girgiza kanta tayi saiga wasu zafafan hawaye sun sauka kan kumatunta,atare suka kai hannuwan su kan fuskar ta dan share hawayen,shi yana ƙoƙarin share mata itama tana ƙoƙarin gogewa,sai ya zamana hannun sa yana saman nata,kallon juna suka cigaba dayi cikin wani irin yanayi mai wuyar fassarawa,itace tayi ƙoƙarin fara janye idonta akan sa tare da janye hannun ta,kana shi kuma cikin sanyin murya da kasalar da tausayin ta yasaka masa ya yace" da ita,faɗa min damuwar ki!'salon da yayi magana dashi shine ya kuma karya wa Bintu zuciya kawai sai ta saki wani ɗan marayan kuka cikin muryar kukan da takeyi ƙasa ƙasa, tace"bana jin daɗi tsoro nakeji zuciya ta wani irin bugu take,ban taɓa jin abin da nakeji yanzu ba na kasa yin addu'a kayi min addu'a kaji Yahh Abdallah!'ta faɗa tana saka duka hannayen ta saman funkar ta tare da girgiza kanta,wani irin tausayine wanda yake gauraye da wani irin yanayi da ba zai iya tan-tance na meye ba ya rufe shi,cikin yanayin da bai sake shi ba ya gyara kwanciyar shi sosai kana itama ya gyara mata kwanciya ajikin sa tare da sa blanket ya rufeta,kana ya shiga tofa mata addu'oi har sai da yaji ta daina jan ajiyar zuciya tare da shaahsheƙar kukan da takeyi,kana ya janyo littafin da dama yana kusa dashi ya buɗe tare da Bismillah,ya fara karantawa,
Zuba mata ido yayi yana jiran jin ta ina zata fara,dan a haƙiƙanin gaskiya ya zaƙu da yaji wacece Bintu, wanda tun jiya shine aransa so yake ya tabbatar da abinda mutumin nan ya faɗa,idan har abinda ya faɗa yazo dai dai da wanda Bintun zata faɗa masa,to kuwa tabbas dole su san duk yadda zasuyi dan janyo hankalin Anty Nafisa ta buɗe musu sirrin da take ta ɓoyo, dan yana da yaƙinin cewa sirrin baya rasa na saba da Bintun,yana ji ajikin sa Nafisa itace sanadin komai,itace mafarin dukkanin abinda ya faru,dan ga dukkanin alamu tasan da zaman ɗiyar Umar ɗin,idan ba haka ba ba yadda za ayi ace ta tashi hankalinta kamar yadda Bintu ta sanar dashi,tabbas akwai lauje cikin naɗi akwai wani ɓoyayyan al amari me girma wanda ita Anty Nafisa bata son kowa ya sani, shine kuma sirrin datake muƙu-muƙun ɓoyewa,kuma da izinin Allah su sai sun sata ta faɗa ko ma meye da bakin ta,da kanta zata ɗauki wuƙa ta bur mawa cikinta,koma ace ta burma,tunda gashi bata iya aiwatar da komai batare da shawarar Bintu ba,wanda tabbas wannan wata alama ce data ke nuni da cewa ƙarshen Anty Nafisa ya zo,
"Ganin yadda ya zuba mata ido yasa tashiga ƙif-ƙifta nata idanuwan saboda ta rasa ta ina zata fara, ita sam bata iya bada dogan labari ba,wani tunani tayi a ranta wanda yasa ta ɗan kalleshi,kana cikin sanyin muryar ta tace"zan ɗauko maka deary ɗin da fafi ya bani sai ka duba,ina ga zaifi sauƙi!'ta faɗa tana lumshe idanunta,cikin alamun nuna gamsuwa da Maganar tata yace"kije ki ɗauko yanzu ina jiranki!'ya faɗa yana ɗan kwanciya jikin makarin gadon,wanda shima faɗa kawai yayi amma yasan Bintu baza ta iya fita a wannan lokacin ba,shuru tayi a wajen batare da ta motsaba,juyowa yayi yana fuskantar ta tare da yi mata alamar me take jira?tura ɗan ƙaramin bakinta tayi batare da tace"ko mai ba,har zai share ta sai kuma yaji ba zai iya ba yana so a daren nan ya karanta labarin Bintun,dan haka ya tashi yana mai zura silifas ɗin dake bakin gadon wanda akayi shi da yadin dake shimfiɗe saman gadon,tashi muje! ya faɗa yana wucewa gaba.
A hankali take bin bayan sa, wanda hakan ma ji take kamar za a ruƙota ta baya,lokacin da suka fita falon inno ne taji kamar anabin bayanta,tun tana daurewa har dai ta kumaji kamar an taɓota ta baya,cikin wani irin razana da tsinkewar zuciya ta ruƙo hannun sa yana juyowa ta faɗa jikin sa tasa hannu ta zagaye shi ta rikeshi katamau idanunta a runtse,hannu yasa ya ɗago fuskar ta,yana mamakin abinda ya tsorata ta lokaci ɗaya haka,sam taki bashi damar ganin fuskarta saboda yadda ta shigar da fuskar cikin ƙirjin shi, dalilin kusan cin su da juna ne yasa har yana iya jiyo bugun zuciyar ta wanda suke bugawa tare da tasa zuciyar, A hankali yasa hannun sa A gadon bayan ta yana ɗan partin bayan nata a hankali dan samar mata da nutsuwa,tana manne ajikin sa ya cigaba da tafiya da ita har suka kai cikin ɗakin ta,zama yayi da ita ajikin sa,cikin san yayi calming ɗin ta yace"buɗe idanunki, ki gani ba kowa mun shigo ɗakin ki,tashi ki nunan inda littafin yake!'A hankali yake mata maganar kamar wanda yake tsoran tashin jaririn da ya rasa uwar sa tashi daga baccin da yake,a tsorace ta ɗago kan nata tana bin ɗakin da ido a sace,kana cikin ƙara maƙale shi tace"yana cikin durowar can A cikin wata baƙar jaka, idan ka buɗe jakar zaka kuma ganin wata ƴar leda baƙa to aciki yake!'duk maganar nan da takeyi tuni ta daɗe da mai da kanta ta ƙunshe cikin jikin sa,ba dan Allah yayi masa ƙarfin ji bama da ba zai ji abinda take cewa ba,saboda yadda take yin maganar ƙasa ƙasa,kuma cikin tsoro.
Zuba mata ido yayi ganin bata da alamar zata sake shi yaje ya ɗauko littafin,sai aukin yi masa kwatance da takeyi,ganin lokaci sai tafiya yake basuyi abinda ya kamata ba yasa shi fara ɗan janye ta daga jikinsa, haƙura tayi ta rabu daga jikin nasa amma bata rabu da binsa kamar jela ba,har sai da yaje ya buɗe durowar da ta kwatanta masa,ya ɗauko jakar tare da buɗeta ya ɗauko ledar itama kana ya maida su inda suke ya rufe,tana ganin haka tayi saurin matsawa jikin sa wanda dama jiran sa take ya gama abinda yakeyi ta ɗora daga inda ta tsaya,duban ta yayi cikin fuskarsa da take a haɗe yace"Bint wai wannan wane irin tsorone haka?ki rage tsoron nan yayi yawa!'ya faɗa yana ɗan janye ta daga jikin sa,ba dan taso ba ta rabu da jikinsa tare da raɓe a gefe kana ganin ta zaka gane cewa a matuƙar firgice take, durowar kayanta ya bude tare da ɗauko mata kayan bacci da hijabi, kana ya kama hannunta suka fita,har suka koma ɓangaren sa jikin Bintu bai daina ɓarin tsoro ba,wanda shi Abdallah atunanin sa kawai irin tsorone irin na Bintu,amma a haƙikanin gaskiya a kwai wani abu da shi Abdallah bai sani ba.
Suna shiga ɗakin sa yasaki hannunta tare da miƙa mata kayan da ya ɗauko mata,karɓa tayi batare da ta motsa daga inda take tsaye ba,tana ta dai jujjuya kayan a hannun ta,ganin kamar bata gane abin da yake nufi ba yasa shi cewa kije ki canja kayan jikin ki idan bazaki iya yin wankan ba!'kamar wadda ƙwai ya fashewa haka take taka ƙafaunta dan zuwa toilet ɗin, zuciyar ta kuwa kamar zatayo waje saboda tsananin tsoron da ke cikinta,ƙoƙar tawa tayi ta fara karanto addu'oi bayan tashiga toilet ɗin,haka nan takejin wata kasala a cikin kwana biyun nan wanda ta rasa da lilin hakan,bata iya yin addu'oin ta yadda ya kamata, ko da ta fara sai bacci ya kamata,ga wani irin tsoron da take yawan ji,wanda ta san da ba haka take ba,duk da cewa tasan tana da tsoro amma ba kamar yadda takeji yanzu ba,cikin san dakewa da kalato jarumta ta cire kayan jikin ta,so takeyi ta ɗan yi wankan dan bazata iya bacci batare da tayi wanka ba,da tai makon addu'ar da ta samu ta zauna abakinta tayi wankan tare da ɗaura alwala kana taja ƙaramin tawul ta ɗaura ajikin ta,tana gab da fitowa taji kamar anja tawul ɗin da ta ɗaura ajikinta ta baya,ai da wani irin gudu ta ƙara sa fitowa jikinta yana wani irin rawa,
Ganin ta yayi kawai kamar anjeho ta,da gudu ta faɗa jikin sa tare da ruƙun kumeshi,zuba mata idanunsa yayi zuciyar sa cike da saƙe saƙe,anya kuwa yariyar nan lafiya take?yasan cewa tabbas Bintu tana da tsoro amma kuma bai taɓa ganin tsoron ta kamar na wannan lokacin ba,take zuciyar shi ta fara kaikawo akan wannan al'amari,jin yadda take ta shigewa cikin jikin sane yasa shi dawowa daga nazarin al'amarin da yake,cikin nutsatstsiyar Muryar sa yace"lafiyar ki kuwa? me yake damun ki haka?alokaci ɗaya ya jero mata waɗan nan tambayoyin yana mai son ganin fuskar ta, ta hanyar ƙoƙarin ɗago da kanta da ta cusa a cikin kirjin shi,
Zuba mata narkakkun idanunsa yayi A yayin da yasamu nasarar ɗago kan nata,itama kallon shi takeyi,da idanunta da suka cika da ƙwalla,cikin taushin murya yace"Bint gayamin meke damunki?girgiza kanta tayi saiga wasu zafafan hawaye sun sauka kan kumatunta,atare suka kai hannuwan su kan fuskar ta dan share hawayen,shi yana ƙoƙarin share mata itama tana ƙoƙarin gogewa,sai ya zamana hannun sa yana saman nata,kallon juna suka cigaba dayi cikin wani irin yanayi mai wuyar fassarawa,itace tayi ƙoƙarin fara janye idonta akan sa tare da janye hannun ta,kana shi kuma cikin sanyin murya da kasalar da tausayin ta yasaka masa ya yace" da ita,faɗa min damuwar ki!'salon da yayi magana dashi shine ya kuma karya wa Bintu zuciya kawai sai ta saki wani ɗan marayan kuka cikin muryar kukan da takeyi ƙasa ƙasa, tace"bana jin daɗi tsoro nakeji zuciya ta wani irin bugu take,ban taɓa jin abin da nakeji yanzu ba na kasa yin addu'a kayi min addu'a kaji Yahh Abdallah!'ta faɗa tana saka duka hannayen ta saman funkar ta tare da girgiza kanta,wani irin tausayine wanda yake gauraye da wani irin yanayi da ba zai iya tan-tance na meye ba ya rufe shi,cikin yanayin da bai sake shi ba ya gyara kwanciyar shi sosai kana itama ya gyara mata kwanciya ajikin sa tare da sa blanket ya rufeta,kana ya shiga tofa mata addu'oi har sai da yaji ta daina jan ajiyar zuciya tare da shaahsheƙar kukan da takeyi,kana ya janyo littafin da dama yana kusa dashi ya buɗe tare da Bismillah,ya fara karantawa,