Sashe 47
Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Wurgi takeyi da duk abinda yazo hannun ta, Siddiqa da Farida ne suke ƙoƙarin kamata duk tabi ta jiwa kanta ciwo saboda gilasan da ta fasa kuka take tare da wani irin ihu na tsan tsan baƙin ciki da takaici,da suka kasa tsaida ita sai suka ruga suka kira inno, inno tayi matuƙar mamakin wannan haukan na Taufiƙa,cikin muryar da take ɗauke da tsantsar baƙin ciki tace"Taufiƙa Ni dai wannan halin naku na ɓaƙin hali da shegiyar baƙar zuciya ba acikin zuriyata kuka sameshi ba,dan duk cikin yarana mata shida cas ban haifi me baƙar zuciya da mugunta ba sai dai acan dangin ubanku kuka kwaso wannan mugun halin, tur wallahi Taufiƙa kinji kunyar rayuwarki da babbar asarar da idan baki gyara halinki ba rayuwarki bazatayi kyau ba,kuma har abada ke da Abdallah dan ya riga yayi miki nisa wutsiyar raƙumi tayi nesa da ƙasa,baku dace ba ko ta wanne ɓangare, Bintun dai da kika tsana da ita ya dace Allah baya jarabtar kamilin mutum kamar Abdallah da Auren mace irinki, kina zaune a gidan nan zakiyi kallon yadda ake zaman Aure mai cike da mutunta juna kina zaune a gidan nan zakiga yadda Abdallah zai maida Bintu sarauniyar mata kina zaune a gidan nan zaki kalli soyayyar da baki taɓa ji ko gani ba arayuwarki, kina zaune a gidan nan zakiga yadda Abdallah zai durƙusa ya juya baya Bintu ta hau ya goyeta ya sa majanyi ya ɗaure kuma kina zaune zakiga yadda yarinyar da kika ƙasƙantar zata juya mijin da kikaso kike gani ya wuce ajinta, kina zaune kuma zakiga yadda Bintu za tayi taƙama da estate din nan kamar yadda kike mata borin tsiya,haka kuma kina zaune Bintu zata riƙe arzikin da baki taɓa mafarkin samun sa ba arayuwar ki, Taufiƙa Ni na gaya miki wannan wataran ko babu raina sai kin tuna da wannan kalaman nawa saboda da ikon rabbil izzati duk abinda nazana miki sai sun tabbata A kan rayuwar Bintu saboda ita ɗin kamar waliyiya take saboda wankakkiyar zuciya bata nufin kowa da sharri sai Alkhairi, wannan alkairin shine zai bibiyi rayuwarta da dukkanin zuriyarta insha Allah!'daga haka ta fita daga ɗakin cikin farin ciki saboda ji take ta fato Taufiƙa a kan yadda ta daɗe aranta, ta wanke takaicinta na tun ranar da suka dawo gidan akan abinda sukewa Bintu gashi tana jin abinda ta faɗa tamkar sun riga sun tabbata akan bintun duk da tasan a kwai ƙalubale cikin rayuwar ta to amma tayi yaƙinin cewa da sannu wannan lokacin zaizo.
Sayyid ma yashiga halin É—imauta da jin wannan al'amari, saboda akwai shirin da yasoyi kafin faruwar lamarin to amma dai ko yanzun ma babu abinda zai dakatar dashi daga aikin da aka saka shi duk da bai san wanda yayi wa Bintu wannan test É—in ba amma dole zai bincika ya nemo wanda ta haÉ—a kai dashi ko wanda yasa ta aikin dan yanzu aikin da aka bashi kenan kuma da sannu zai zamu nasarar aiwatar da abinda yake aikin sane, dan ya É—au alwashin ba zai bawa waÉ—an da suka sakashi aikin Nan kunya ba.
Acan cikin copy kuma Samira ce tare da Alhaji Sama'ila zaune bisa kujerun ƙarfe sai ƴan kayan lashe lashe agabansu,Alhaji Sama'ila ne ya dubi Samira cikin zaƙuwa da san jin abinda zatace masa yace"Samira inajinki jiya da tunanin maganar da zamuyi nayi bacci!'murmushi tayi kana tace"abinda zan gaya maka wani Abune da ya shafi rayuwata wanda kuma naga ka can canta da nasanar dakai saboda yadda da zaman amana!'jinjina kansa yayi cike da gamsuwa da jin daɗin lafazinta,ta cigaba da cewa,shiyasa na shirya gaya maka duk wani sirrina wanda zaka iya zuwa kaji shi a wani baki na da ban, kuma hakan zai iya kawo mana saɓani cikin kyakykyawar mu'amalar mu!' katse ta yayi da cewa duk naji wannan na kuma fahimta ki sanar dani abinda yake faruwa kai tsaye karki samu damuwa!'ƙasa tayi da kanta kana cikin taushin murya tace"Ni dai na kasan ce ƴar babban gida kuma wadda take da tarin dangi da ƴan uba saboda mahaifinmu yana da tarin mata,shiyasa ya tara ƴaƴa da yawa,haka kuma yana da tarin dukiya wadda har ta zama abar kwatance cikin jama"a,amma abin mamakin sam mahaifinmu baya mora mana da ko biyar daga cikin arzikin sa kowa sai dai ya nema da kansa, matan mu da mazan mu hakan ne yasa har so muke muga mahaifin mu ya faɗi ya mutu,ganin abubuwan suna daɗa yawa sai kawai mukayi shawara a junan mu na me zai sa mu kasheshi tunda yaƙi mutuwa, wannan shawarar duk munyi amanna da ita amma iya mu waɗanda suke da buƙatar hakan,dan haka muka shirya da wasu ƴan daba mukayi ciniki dasu suka shiga har gida suka soka masa wuƙa, wannan shine sanadin mutuwar mahaifinmu kuma mun sami abin da muke nema na dukiya da kadarori!'sauke numfashi tayi tana dauke kanta ƙasa cikin sanyin murya tace" masa wannan labarinne bana so kazo kaji daga baya ka tsaneni shiyasa naga gara na faɗa maka da bakina saboda ka fahimceni!'shiru gurin ya ɗauka na wasu daƙiƙai daga bisani Alhaji Sama'ila ya gyara zamansa tare da goge zufar da ta ɗan taru saman goshinsa kana yace" Samira yanzu nadamar abinda kika aikata kike kome?shiru ta ɗan yi kana kuma tace"bazan yaudareka ba Alhaji Sama'ila sam bana nadamar abinda na aikata koda zuwa za ayi A tafi dani akan laifin kisan mahaifina!'ta ƙara sa maganar cikin nuna taurin zuciya, murmushi yayi tare da cewa gaskiya Samira kin burgeni wannan abin da kikayi shine ya nunamin zaki iya zama dani kuma zamu gudu tare mu tsira tare, tabbas zan iya saka ki cikin tafiyar mu,dan haka nima zan gaya miki kaɗan daga cikin aikin da mukeyi a yanzu amma ba yanzu ba sai mun sake zama!' tace"amma ko na jiya ne ka sanar dani saboda hankalina ya tashi sosai!'yace" kar ki damu ba komai bane wannan muna kan war ware matsalar tace" duk da haka dai yakamata ka faɗa koda taimakon da zan iya yi maka!'ɗan jim yayi kana yace"hakane,bata labarin abinda ya faru da Bintu da Abdallah yayi tare da yi mata bayanin abinda suke nema ya dai yi mata bayanin komai ataƙaice ya kuma ce zai sakata cikin tafiyar tasu,cikin farin ciki tace"amma da kasan da wannan business ɗin baka taɓa tallata min ba, Alhaji Sama'ila ya ƙyalƙyale da dariya cikin dariyar yake cewa to ai gashi yanzu na tallata miki har ma na siyar miki da ita!' itama dariyar tayi kana kuma ta ɗan maida fuskarta serios tace"kuma ku bakwa tunanin wani ko wata da zai iya sakata yin hakan?girgiza kansa yayi tare da cewa, gaskiya bama tunanin kowa,dan A binciken da muke kanyi kenan!'ta wacce hanya kake gani zanbi dan taimaka muku? yace" zamuyi maganar da sauran team ɗina idan ta kama ma ayi mitin ɗin dake duk zan sanar miki!'murmushi tayi tare da saurin danna sevin a recording ɗin da tasaka kana ta miƙe tace"to shike nan dear Ina nan inajiranka ni zan wuce gida!'muje nima ai wucewar zanyi!'daga nan suka taka har zuwa bakin motar Samiran, ya buɗe mata ta shiga suka kuma yin sallama kana ta ja motar sai da yaga fitar ta kana shima ya shiga tasa ya bar gurin.
Sai da yagama sauraren recording ɗin kana ya ɗan yi wani muskilin murmushi,karkuso kuga fuskar Abdallah da murmushi saboda matuƙar kyan da yayi masa kumatunsa saida ya loɓa irin na Bintu,cikin daddaɗar Muryar sa yace"na gode Samira kinyi ƙoƙari sosai ina fatan mana nasara cikin dukkanin aiyukan mu dana yanzu dana gaba!'amin ya hayyu ya ƙaiyumu,ta faɗa tana ƙoƙarin ta shi sallama tayi masa,bayan fitarta ya ɗan jingina bayansa da makarin kujerar tare da lumshe shanyayyun idanun sa,ko ya waccen rigimammiyar take ciki? tun ɗazu ya bada take away a ka kai mata ko taci ta haƙura da kukan oho mata rigimammiya kawai, tsadadden agogon dake ɗaure a hannun sa ya kalla ƙarfe uku da arba'in miƙewa yayi ya kwashi tarkacen sa kana ya fita, masallaci suka fara shiga sukayi sallah daga nan suka nufi gidan sa na area 1.
Sayyid ma yashiga halin É—imauta da jin wannan al'amari, saboda akwai shirin da yasoyi kafin faruwar lamarin to amma dai ko yanzun ma babu abinda zai dakatar dashi daga aikin da aka saka shi duk da bai san wanda yayi wa Bintu wannan test É—in ba amma dole zai bincika ya nemo wanda ta haÉ—a kai dashi ko wanda yasa ta aikin dan yanzu aikin da aka bashi kenan kuma da sannu zai zamu nasarar aiwatar da abinda yake aikin sane, dan ya É—au alwashin ba zai bawa waÉ—an da suka sakashi aikin Nan kunya ba.
Acan cikin copy kuma Samira ce tare da Alhaji Sama'ila zaune bisa kujerun ƙarfe sai ƴan kayan lashe lashe agabansu,Alhaji Sama'ila ne ya dubi Samira cikin zaƙuwa da san jin abinda zatace masa yace"Samira inajinki jiya da tunanin maganar da zamuyi nayi bacci!'murmushi tayi kana tace"abinda zan gaya maka wani Abune da ya shafi rayuwata wanda kuma naga ka can canta da nasanar dakai saboda yadda da zaman amana!'jinjina kansa yayi cike da gamsuwa da jin daɗin lafazinta,ta cigaba da cewa,shiyasa na shirya gaya maka duk wani sirrina wanda zaka iya zuwa kaji shi a wani baki na da ban, kuma hakan zai iya kawo mana saɓani cikin kyakykyawar mu'amalar mu!' katse ta yayi da cewa duk naji wannan na kuma fahimta ki sanar dani abinda yake faruwa kai tsaye karki samu damuwa!'ƙasa tayi da kanta kana cikin taushin murya tace"Ni dai na kasan ce ƴar babban gida kuma wadda take da tarin dangi da ƴan uba saboda mahaifinmu yana da tarin mata,shiyasa ya tara ƴaƴa da yawa,haka kuma yana da tarin dukiya wadda har ta zama abar kwatance cikin jama"a,amma abin mamakin sam mahaifinmu baya mora mana da ko biyar daga cikin arzikin sa kowa sai dai ya nema da kansa, matan mu da mazan mu hakan ne yasa har so muke muga mahaifin mu ya faɗi ya mutu,ganin abubuwan suna daɗa yawa sai kawai mukayi shawara a junan mu na me zai sa mu kasheshi tunda yaƙi mutuwa, wannan shawarar duk munyi amanna da ita amma iya mu waɗanda suke da buƙatar hakan,dan haka muka shirya da wasu ƴan daba mukayi ciniki dasu suka shiga har gida suka soka masa wuƙa, wannan shine sanadin mutuwar mahaifinmu kuma mun sami abin da muke nema na dukiya da kadarori!'sauke numfashi tayi tana dauke kanta ƙasa cikin sanyin murya tace" masa wannan labarinne bana so kazo kaji daga baya ka tsaneni shiyasa naga gara na faɗa maka da bakina saboda ka fahimceni!'shiru gurin ya ɗauka na wasu daƙiƙai daga bisani Alhaji Sama'ila ya gyara zamansa tare da goge zufar da ta ɗan taru saman goshinsa kana yace" Samira yanzu nadamar abinda kika aikata kike kome?shiru ta ɗan yi kana kuma tace"bazan yaudareka ba Alhaji Sama'ila sam bana nadamar abinda na aikata koda zuwa za ayi A tafi dani akan laifin kisan mahaifina!'ta ƙara sa maganar cikin nuna taurin zuciya, murmushi yayi tare da cewa gaskiya Samira kin burgeni wannan abin da kikayi shine ya nunamin zaki iya zama dani kuma zamu gudu tare mu tsira tare, tabbas zan iya saka ki cikin tafiyar mu,dan haka nima zan gaya miki kaɗan daga cikin aikin da mukeyi a yanzu amma ba yanzu ba sai mun sake zama!' tace"amma ko na jiya ne ka sanar dani saboda hankalina ya tashi sosai!'yace" kar ki damu ba komai bane wannan muna kan war ware matsalar tace" duk da haka dai yakamata ka faɗa koda taimakon da zan iya yi maka!'ɗan jim yayi kana yace"hakane,bata labarin abinda ya faru da Bintu da Abdallah yayi tare da yi mata bayanin abinda suke nema ya dai yi mata bayanin komai ataƙaice ya kuma ce zai sakata cikin tafiyar tasu,cikin farin ciki tace"amma da kasan da wannan business ɗin baka taɓa tallata min ba, Alhaji Sama'ila ya ƙyalƙyale da dariya cikin dariyar yake cewa to ai gashi yanzu na tallata miki har ma na siyar miki da ita!' itama dariyar tayi kana kuma ta ɗan maida fuskarta serios tace"kuma ku bakwa tunanin wani ko wata da zai iya sakata yin hakan?girgiza kansa yayi tare da cewa, gaskiya bama tunanin kowa,dan A binciken da muke kanyi kenan!'ta wacce hanya kake gani zanbi dan taimaka muku? yace" zamuyi maganar da sauran team ɗina idan ta kama ma ayi mitin ɗin dake duk zan sanar miki!'murmushi tayi tare da saurin danna sevin a recording ɗin da tasaka kana ta miƙe tace"to shike nan dear Ina nan inajiranka ni zan wuce gida!'muje nima ai wucewar zanyi!'daga nan suka taka har zuwa bakin motar Samiran, ya buɗe mata ta shiga suka kuma yin sallama kana ta ja motar sai da yaga fitar ta kana shima ya shiga tasa ya bar gurin.
Sai da yagama sauraren recording ɗin kana ya ɗan yi wani muskilin murmushi,karkuso kuga fuskar Abdallah da murmushi saboda matuƙar kyan da yayi masa kumatunsa saida ya loɓa irin na Bintu,cikin daddaɗar Muryar sa yace"na gode Samira kinyi ƙoƙari sosai ina fatan mana nasara cikin dukkanin aiyukan mu dana yanzu dana gaba!'amin ya hayyu ya ƙaiyumu,ta faɗa tana ƙoƙarin ta shi sallama tayi masa,bayan fitarta ya ɗan jingina bayansa da makarin kujerar tare da lumshe shanyayyun idanun sa,ko ya waccen rigimammiyar take ciki? tun ɗazu ya bada take away a ka kai mata ko taci ta haƙura da kukan oho mata rigimammiya kawai, tsadadden agogon dake ɗaure a hannun sa ya kalla ƙarfe uku da arba'in miƙewa yayi ya kwashi tarkacen sa kana ya fita, masallaci suka fara shiga sukayi sallah daga nan suka nufi gidan sa na area 1.