Sashe 57
Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bintu tunanin ta hanyar da zata samu ta isar da saƙonta gurin Hajiya ladidi da Nafisa,ne hanyar da zata fara tarwatsa dangantakar su ko dan ta samu abin da takeso duk da tasan shiga tsakanin ɗa da uwa sai Allah, amma tanada yaƙinin Allah bazai kamata da haƙƙin su ba, tunda neman samun warware wani babban ƙulli take wanda zaiyi sanadin tar watsewar mutane da dama da kuma shiriyar wasu da dama, gashi bata san inda wayarta take ba tun ranar da aka kaita station, turo ƙofar ɗakin da akayi ne yasa ta dakatawa daga sintirin da takeyi tare da juyowa alokaci ɗaya tana kallon Anty Nafisa wadda ta shigo,ƙarasowa tayi gaban Bintu tare da miƙa mata wayar ta, Bintu kallon ta take cike da mamakin yadda akayi wayar taje hannunta ,kamar tasan tunanin da Bintu takeyi, tace"nima a wajen Hajiya Babba na karɓo lokacin na shiga gaida ta sai na tarar tana cewa Rahima tazo ta kawo Miki shine nace ta kawo zan baki nima nan nayo kinji dalili kuma nima rashin wayar taki ya dameni gashi babu halin na baki wata!'hannu tasa ta karɓa tare da cewa na gode nima yanzu tunanin wayar nake saboda ina buƙatar magana da Hajiyarki saboda...sai kuma tayi shiru da alamun kamar tayi suɓutar baki a zan cen nata, Anty Nafisa tace" ina jinki saboda me?shuru Bintu tayi tana ɗan kauce kauce alamun ta dai ya nuna rashin gaskiya,cikin da bar bar cewar zance tace"a'a babu ko mai fa wani saƙone da ban!'zuba mata ido Anty Nafisa tayi da alamun rashin yadda cikin idanun ta sai dai kuma ba tace komai ba amma yanayin ta ya nuna akwai Magana abakinta.
Bintu ta kawar da wancan zan cen da cewa Anty Nafisa a kwai wani abu sabone? cikin wani yanayi Anty Nafisa tace"Bintu ai ko da yaushe gidan nan baya rabo da sabon labari wanda yake ƙunshe da sabuwar manaƙisa,na san da cewa burina ya sha ban ban da sauran burukan da ke zuciyoyin gidan nan,dan haka Ni bani da damuwa da sanin abinda suke hari burina kawai shine buri, tunda bani da kishiya ta wajen tarayya da abinda nake so to duk me sauƙine,shi yasa kikaga ban cika azarɓaɓi cikin aikina ba,dan nasan burina zai cika,to amma kuma yanzu wannan tunanin ya rushe saboda abinda na gano wanda Gara ace ina da masu tarayya akan dukiyar mijina, Bintu ta ɗan numfasa kana tace"yanzu me kike so dani ina cewa Ni aikina sai nan da watannin da kika ƙaiyadewa cikin ki zan fara? Anty Nafisa tace"hakane,amma akwai abinda yake son shigowa cikin burina shi yasa nake ganin gwara tun kafin cikin yayi ƙwari mu yi abinda ya dace kawai zaki aiwatar da aikinki acikin wannan lokacin!'duk da cewa Bintu ta girgiza da jin sauyin ra ayi daga Anty Nafisa amma sai ta dake ta nuna jarumta akaron ta na farko,dan haka cikin ƙwarin gwiwa tace"to amma kina ganin hakan ba zai zo da wata matsalaba,kuma meye abinda yake shirin kawo miki Barazana cikin burinki?wani irin kallon anya na gaya miki tayiwa Bintu, kana kuma tace"ina ganin babu wata matsala da zamu fuskan ta ki daina wannan tunanin fatan nasara ko da yaushe nakewa kaina ba faɗuwa ba,san nan kuma babu buƙatar kiji dalilin da yasa nake son janyo aikin nan kusa,kawai kiyi abin da nasaka ki ba wai tambayar abinda bai zama hurumin ki ba, wannan sirrinane da idan ba Hajiyata ba babu wanda yasani a duniya!'da sauri Bintu tace"shike nan na gamsu da bayananki amma nima ina da shawarar da zan baki!' Anty Nafisa tace"ina sauraran ki bamu da lokaci me yawa!'Bintu ta ɗan yi ƙasa da murya tare da cewa me zai hana ki fara ɗaukar matakin karɓar duk wasu manyan kadarorin mijinki cikin dabara kisa duk ya saka miki hannu su zama mallakin ki kafin mu kai ga sheshi"zubawa Bintu ido tayi cikin zurfafa tunani da mamakin manufar Bintu a kan wannan shawara,cike da mamakin tace"Bintu meye manufarki ta can ja min tunani?ɗan waige Bintu tayi tare da ƙara tabbatar da babu wanda yake musu laɓe, kana ta kuma yin ƙasa da muryar ta tace"manufata saboda koda idan ya mutu ƴan uwansa zasu iya handame dukiyar ke kuma wata ƙil dun haƙilon da kikayi akan dukiyar ya tashi Aban za saboda na fahimci gidan nan kowa haɗamammene basu da godiyar Allah duk irin tarin dukiyar da mahaifin su yake da ita amma kullum burin su shine ta yaya zasu ƙara arziki,ina ganin idan kika tsaya kallon ruwa tabbas kwaɗo zai iya yimiki ƙafa!'ta ƙara sa maganar tanayiwa Anty Nafisa wani kallo tare da fatan karɓuwar shawararta batare da tayi dogon na zari ba,ai kuwa cikin wani irin mamakin yadda akayi Bintu tayi wannan dogon tsinkaye,Anty Nafisa ta rugumota tare da cewa U are very smart, Bintu kina da fikira tabbas shigowar ki gidan nan ba ƙaramin cigaba da nasara zai kawowa rayuwata ba,na amince da sha wararki sai dai kuma a inda gizo ke saƙar yadda za ayi yasaka min hannun tunda mijina ba shanyayye bane atsaye yake da ƙafafun sa!'Bintu tace" masha Allah anzo gurin Nafisa kinga ta kanki tunda kika yadda dani sai na kawo ƙarshen makircin ku,taɓa tan da Anty Nafisa tayi yasa tayi firgigigit, Anty Nafisa tace"ya kikayi shiru?a hankali Bintu ta sauke doguwar ajiyar zuciya kana tace"mafita nake nemo miki!' cikin zaƙuwa Nafisa tace mecece mafitar? Bintu tace"mafitar itace in dai har kin yadda dani kuma kin gansu ba dan kuɗi zanyi miki aiki ba sai dai taimakon rayuwata da rayuwar waɗan da suke jirana dan taimakon ta su rayuwar, shine ina so ki dinga bi a sannu a hankali kina sace kadarorinsa, Ni kuma ki dinga bani zansa ka ayi fake ɗin takardun saiki maida masa fake ɗin ke kuma ki riƙe original ɗin!'ɗan jim Nafisa tayi daga bisani kuma taja wani dogon numfashi kana tace"kina da hanyar yin hakan yadda baza aganomu ba?da babu ai bazan kawo wannan shawarar ba!' ta faɗa tana ɗan goge fukarta, Anty Nafisa tace"ba dai Ni zaki bawa original ɗin ba idan akayi fake ɗin?tace"haba Anty Nafisa kamar bakya gane yaren da nake miki, ke zan bawa mana kinga idan ko mai ya faru koda sun so cutarki ke tuni kinyi maganin su,guduwa zakiyi abinki baruwan ki da tuhuma dama Ni ba asan meke tsakanin mu ba ina ga wannan hanyar itace mafi sauƙi wajen karya ƙwaɗayayyu!'Anty Nafisa tace"tabbas Maganar ki haka take bazan yi ƙasa a gwiwa ba tun daga yanzu zan fara nema da lalube tunda baya ƙasar!'juyawa tayi cikin sauri tana cewa Bintu bazaki ƙara ganina ba sai da wasu daga cikin kadarorin mijina!'daga haka ta fita daga ɗakin.
Wani irin tsalle tayi tare da faɗawa saman gadonta ta rungume fulo tana sakin wani murmushi me cike da samun ƙarfin gwiwa da kuma hangen nasara wadda take tun karo su nan ba da daɗewa ba Anty Nafisa kin gama zuwa hannu watan cin ubanki da faɗuwarki yayi wannan farin cikin da takeji kamata yayi acce da me taya ta,babu wanda ya daɗi mata sai ogan ta shi yakamata ya ji wannan sarasa da suka samu ita kanta tayi mamakin yadda wannan tunani yazo mata lokaci ɗaya tare da tsara yadda zata tafiyar da komai cikin kwanciyar hankali da nasara.
Duk mintuna sai ta duba agogon dake manne jikin bangon kiching ɗin Allah Allah takeyi ya dawo ta zaƙu ta sanar dashi wannan labari, ɗan tura baki tayi cikin karaya take cewa yanzu haka ma ya gwaleni ko yaƙi nuna farin cikin sa kuma ba lallai ya yaba min ba,bazan ma faɗa maka ba na fasa!'ta ƙare maganar tare da murguɗa ɗan ƙaramin bakinta.
Kamar yadda ya saba saida ya tsaya ya gabatar da sallar magriba da isha kana ya nufo cikin gidan,kai tsaye part É—in sa ya shige bayan yayiwa inno sannu da gida.
Baƙaramin mamaki yayi ba ganinta a falon nasa amma sai ya basar yayi kamar bai ganta ba,ɗan harara ta watsa masa ƙasa ƙasa tana aiyana wa aranta dama tasan wulaƙanci zata sha gashi tun daga yanzu ta fara gani,ita sam bata ga wani abun faɗa da haƙilo da Taufiƙa takeyi kan wannan muskilin ba,wanda magana ma sai ya gadama zaiyita,ji tayi yana cewa idan kin gama bani saƙon hararar sai ki tashi ki tafi ko!'cikin dawowa hayyacinta tace"Ni ban harare kaba sannu da zuwa fa nake maka amma kace na harareka!'cigaba yayi da takun sa cikin nutsuwa batare da ya tanka mata ba ya dai san wannan zaman a kwai dalilin sa,shigewa yayi ɗakinsa ita kuma Bintu ta cigaba da zaman jiran sa, duk da tace ya bata haushi ta fasa faɗa masa cigaban da suka samu,(to Hajiya Bintu bari nima najira naga ya zata kaya muku keda jarumin naki wanda kika kira da miskili duk da naga kamar ke ba yayi miki miskilan cin)
Yadda ya tafi ya barta haka ya dawo ya sameta,nan ɗin ma bai kula ta ba ya wuce kan dinning table dan bawa ciki hakkin sa,sai da ya gama tsaf kana ya taso ya dawo cikin falon,zama yayi kan hamshaƙiyar kujerar sa tare da ɗora ƙafafunsa kan ƙaramin Centre table ɗin dake gaban kujerar,rimot ya ɗauka ya kunna tafkekiyar placsiman da ta mamaye rabin bangon,Bintu dai kallo take binsa dashi ƙasa ƙasa haka nan taji ya mata kyau shigar da yayi ta wata Jessi da ƙaramin gajeren wando iya gwiwa ya burge ta ga wani sihir taccen ƙamshi da ya mamaye wajen tun fitowar sa yayi wani fresh dashi fatar sa sai wani glowing take,cikin ƙasai tacciyar muryarsa yace"ya dai kallon fa?wata irin kunya ce ta kamata kai wannan mutum kwai ƙwaƙƙwafi duk yadda tayi takatsan tsan wajen kallon sa amma sai da ya ganota,tashi tayi zata fita daga falon, ta kuma tsinkayar muryar sa yana cewa karki sake ki fita daga falon nan idan ba haka ba kin san karon mu dake ba zai kyau ba!'dawowa tayi tare da zama inda ta tashi,nuna mata gefan sa yayi ba tare da yayi magana ba,babu yadda ta iya dake yanzu ta fara gane yaran sa na magana da nuni ko da gira ko da ido,
Bintu ta kawar da wancan zan cen da cewa Anty Nafisa a kwai wani abu sabone? cikin wani yanayi Anty Nafisa tace"Bintu ai ko da yaushe gidan nan baya rabo da sabon labari wanda yake ƙunshe da sabuwar manaƙisa,na san da cewa burina ya sha ban ban da sauran burukan da ke zuciyoyin gidan nan,dan haka Ni bani da damuwa da sanin abinda suke hari burina kawai shine buri, tunda bani da kishiya ta wajen tarayya da abinda nake so to duk me sauƙine,shi yasa kikaga ban cika azarɓaɓi cikin aikina ba,dan nasan burina zai cika,to amma kuma yanzu wannan tunanin ya rushe saboda abinda na gano wanda Gara ace ina da masu tarayya akan dukiyar mijina, Bintu ta ɗan numfasa kana tace"yanzu me kike so dani ina cewa Ni aikina sai nan da watannin da kika ƙaiyadewa cikin ki zan fara? Anty Nafisa tace"hakane,amma akwai abinda yake son shigowa cikin burina shi yasa nake ganin gwara tun kafin cikin yayi ƙwari mu yi abinda ya dace kawai zaki aiwatar da aikinki acikin wannan lokacin!'duk da cewa Bintu ta girgiza da jin sauyin ra ayi daga Anty Nafisa amma sai ta dake ta nuna jarumta akaron ta na farko,dan haka cikin ƙwarin gwiwa tace"to amma kina ganin hakan ba zai zo da wata matsalaba,kuma meye abinda yake shirin kawo miki Barazana cikin burinki?wani irin kallon anya na gaya miki tayiwa Bintu, kana kuma tace"ina ganin babu wata matsala da zamu fuskan ta ki daina wannan tunanin fatan nasara ko da yaushe nakewa kaina ba faɗuwa ba,san nan kuma babu buƙatar kiji dalilin da yasa nake son janyo aikin nan kusa,kawai kiyi abin da nasaka ki ba wai tambayar abinda bai zama hurumin ki ba, wannan sirrinane da idan ba Hajiyata ba babu wanda yasani a duniya!'da sauri Bintu tace"shike nan na gamsu da bayananki amma nima ina da shawarar da zan baki!' Anty Nafisa tace"ina sauraran ki bamu da lokaci me yawa!'Bintu ta ɗan yi ƙasa da murya tare da cewa me zai hana ki fara ɗaukar matakin karɓar duk wasu manyan kadarorin mijinki cikin dabara kisa duk ya saka miki hannu su zama mallakin ki kafin mu kai ga sheshi"zubawa Bintu ido tayi cikin zurfafa tunani da mamakin manufar Bintu a kan wannan shawara,cike da mamakin tace"Bintu meye manufarki ta can ja min tunani?ɗan waige Bintu tayi tare da ƙara tabbatar da babu wanda yake musu laɓe, kana ta kuma yin ƙasa da muryar ta tace"manufata saboda koda idan ya mutu ƴan uwansa zasu iya handame dukiyar ke kuma wata ƙil dun haƙilon da kikayi akan dukiyar ya tashi Aban za saboda na fahimci gidan nan kowa haɗamammene basu da godiyar Allah duk irin tarin dukiyar da mahaifin su yake da ita amma kullum burin su shine ta yaya zasu ƙara arziki,ina ganin idan kika tsaya kallon ruwa tabbas kwaɗo zai iya yimiki ƙafa!'ta ƙara sa maganar tanayiwa Anty Nafisa wani kallo tare da fatan karɓuwar shawararta batare da tayi dogon na zari ba,ai kuwa cikin wani irin mamakin yadda akayi Bintu tayi wannan dogon tsinkaye,Anty Nafisa ta rugumota tare da cewa U are very smart, Bintu kina da fikira tabbas shigowar ki gidan nan ba ƙaramin cigaba da nasara zai kawowa rayuwata ba,na amince da sha wararki sai dai kuma a inda gizo ke saƙar yadda za ayi yasaka min hannun tunda mijina ba shanyayye bane atsaye yake da ƙafafun sa!'Bintu tace" masha Allah anzo gurin Nafisa kinga ta kanki tunda kika yadda dani sai na kawo ƙarshen makircin ku,taɓa tan da Anty Nafisa tayi yasa tayi firgigigit, Anty Nafisa tace"ya kikayi shiru?a hankali Bintu ta sauke doguwar ajiyar zuciya kana tace"mafita nake nemo miki!' cikin zaƙuwa Nafisa tace mecece mafitar? Bintu tace"mafitar itace in dai har kin yadda dani kuma kin gansu ba dan kuɗi zanyi miki aiki ba sai dai taimakon rayuwata da rayuwar waɗan da suke jirana dan taimakon ta su rayuwar, shine ina so ki dinga bi a sannu a hankali kina sace kadarorinsa, Ni kuma ki dinga bani zansa ka ayi fake ɗin takardun saiki maida masa fake ɗin ke kuma ki riƙe original ɗin!'ɗan jim Nafisa tayi daga bisani kuma taja wani dogon numfashi kana tace"kina da hanyar yin hakan yadda baza aganomu ba?da babu ai bazan kawo wannan shawarar ba!' ta faɗa tana ɗan goge fukarta, Anty Nafisa tace"ba dai Ni zaki bawa original ɗin ba idan akayi fake ɗin?tace"haba Anty Nafisa kamar bakya gane yaren da nake miki, ke zan bawa mana kinga idan ko mai ya faru koda sun so cutarki ke tuni kinyi maganin su,guduwa zakiyi abinki baruwan ki da tuhuma dama Ni ba asan meke tsakanin mu ba ina ga wannan hanyar itace mafi sauƙi wajen karya ƙwaɗayayyu!'Anty Nafisa tace"tabbas Maganar ki haka take bazan yi ƙasa a gwiwa ba tun daga yanzu zan fara nema da lalube tunda baya ƙasar!'juyawa tayi cikin sauri tana cewa Bintu bazaki ƙara ganina ba sai da wasu daga cikin kadarorin mijina!'daga haka ta fita daga ɗakin.
Wani irin tsalle tayi tare da faɗawa saman gadonta ta rungume fulo tana sakin wani murmushi me cike da samun ƙarfin gwiwa da kuma hangen nasara wadda take tun karo su nan ba da daɗewa ba Anty Nafisa kin gama zuwa hannu watan cin ubanki da faɗuwarki yayi wannan farin cikin da takeji kamata yayi acce da me taya ta,babu wanda ya daɗi mata sai ogan ta shi yakamata ya ji wannan sarasa da suka samu ita kanta tayi mamakin yadda wannan tunani yazo mata lokaci ɗaya tare da tsara yadda zata tafiyar da komai cikin kwanciyar hankali da nasara.
Duk mintuna sai ta duba agogon dake manne jikin bangon kiching ɗin Allah Allah takeyi ya dawo ta zaƙu ta sanar dashi wannan labari, ɗan tura baki tayi cikin karaya take cewa yanzu haka ma ya gwaleni ko yaƙi nuna farin cikin sa kuma ba lallai ya yaba min ba,bazan ma faɗa maka ba na fasa!'ta ƙare maganar tare da murguɗa ɗan ƙaramin bakinta.
Kamar yadda ya saba saida ya tsaya ya gabatar da sallar magriba da isha kana ya nufo cikin gidan,kai tsaye part É—in sa ya shige bayan yayiwa inno sannu da gida.
Baƙaramin mamaki yayi ba ganinta a falon nasa amma sai ya basar yayi kamar bai ganta ba,ɗan harara ta watsa masa ƙasa ƙasa tana aiyana wa aranta dama tasan wulaƙanci zata sha gashi tun daga yanzu ta fara gani,ita sam bata ga wani abun faɗa da haƙilo da Taufiƙa takeyi kan wannan muskilin ba,wanda magana ma sai ya gadama zaiyita,ji tayi yana cewa idan kin gama bani saƙon hararar sai ki tashi ki tafi ko!'cikin dawowa hayyacinta tace"Ni ban harare kaba sannu da zuwa fa nake maka amma kace na harareka!'cigaba yayi da takun sa cikin nutsuwa batare da ya tanka mata ba ya dai san wannan zaman a kwai dalilin sa,shigewa yayi ɗakinsa ita kuma Bintu ta cigaba da zaman jiran sa, duk da tace ya bata haushi ta fasa faɗa masa cigaban da suka samu,(to Hajiya Bintu bari nima najira naga ya zata kaya muku keda jarumin naki wanda kika kira da miskili duk da naga kamar ke ba yayi miki miskilan cin)
Yadda ya tafi ya barta haka ya dawo ya sameta,nan ɗin ma bai kula ta ba ya wuce kan dinning table dan bawa ciki hakkin sa,sai da ya gama tsaf kana ya taso ya dawo cikin falon,zama yayi kan hamshaƙiyar kujerar sa tare da ɗora ƙafafunsa kan ƙaramin Centre table ɗin dake gaban kujerar,rimot ya ɗauka ya kunna tafkekiyar placsiman da ta mamaye rabin bangon,Bintu dai kallo take binsa dashi ƙasa ƙasa haka nan taji ya mata kyau shigar da yayi ta wata Jessi da ƙaramin gajeren wando iya gwiwa ya burge ta ga wani sihir taccen ƙamshi da ya mamaye wajen tun fitowar sa yayi wani fresh dashi fatar sa sai wani glowing take,cikin ƙasai tacciyar muryarsa yace"ya dai kallon fa?wata irin kunya ce ta kamata kai wannan mutum kwai ƙwaƙƙwafi duk yadda tayi takatsan tsan wajen kallon sa amma sai da ya ganota,tashi tayi zata fita daga falon, ta kuma tsinkayar muryar sa yana cewa karki sake ki fita daga falon nan idan ba haka ba kin san karon mu dake ba zai kyau ba!'dawowa tayi tare da zama inda ta tashi,nuna mata gefan sa yayi ba tare da yayi magana ba,babu yadda ta iya dake yanzu ta fara gane yaran sa na magana da nuni ko da gira ko da ido,