Sashe 72
Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Wata tsawa shugaba azukyi ya dakawa Nanu, me kake yi haka ne?kasan wannan hanyar da ka biyo ba hanya bace me ɓullewa,me yasa baka tsaya akan wan can shirin namu ba, tabbas kayi gangan cin fallasa Muryar ka ga yarinyar nan,domin tabbas yanzu da abinda zata samu dama akanka ke nan!'ya ajiye maganar cikin wani irin huci na tsananin ɓaci rai da abin da nanun yayi,wanda aka kira da nanu yayi ƙasa da kan sa tare da cewa afuwa nake nema shugaba yanzu meye abinyi?babu wani abin yi nanu saboda ka nuna mana bamu da wani amfani a cikin wannan tafiyar dan haka sai kaje ka ƙara sa aikin ka kai ɗaya!'cikin tashin hankali nanu ya kwanta a ƙasa yana mai neman afuwar shugaba,nasan nayi kuskure amma ayi min afuwa!' shugaba yace"tabbas yanzu yarinyar nan zata dinga bibiyar ka ta muryar ka, don kuwa ka riga ka buɗe mata hanya da ace kayi haƙuri ka barta a iya tsoron da muka dasa mata da yanzu bamu da wata matsala yanzu ka riga ka rusa komai!'yanzu lalata wannan shirin yana da matukar wuya, saboda muryar ka ta riga ta zauna a cikin ƙwaƙwalwar ta,cikin ƙara yin ƙan da kai yace"yanzu meye abinyi shugaba?yace"dole sai mun nemi taimakon dodo jack dan haka yanzu kaje za muyi magana bayan na gana dashi!'nanu dai ya haƙora ne amma ba dan ransa yaso ba dan sai yanzu ya ankara da babban kuskuren da yayi baya son wannan abin da yayi ya zama shine sanadin tonuwar asirin sa, duk yadda zaiyi da yarinyar nan sai yayi dan samun cikar burin sa da kuma rufuwar asirin sa,
Nafisa dai tana cikin tsaka mai wuya ta rasa inda tunanin ta zai tsaya maganganun Bintu ne suke ta kaiwa da kawowa cikin ƙwaƙwalwar ta,anya kuwa tana da wannan ƙwarin gwiwar a wajen Umar?duk da tana da tabbacin bai san komai akan abinda ta aikata ba,amma bata tunanin akwai wannan yardar da Bintu take faɗa a tsakaninsu,haka kawai take jin bata yadda da kanta a wajen Umar ɗin ba,to ko gwadawa zatayi ta gani ko zata dace?goge zufar dake ta tsatstsafo mata tayi,a fili ta furta,zan gwada Bintu zan ga yadda Umar ya ɗauke Ni da kuma kallon da yake min zan tambaye shi abinda yake damun sa zan gani ko zai gaya min indai kuwa ya faɗa min to tabbas zan ƙara kwantar da hankali na saboda na yadda ya amince dani ba kuma ya zargi na da aikata masa babban laifi.
Abdallah ya samu duk wasu bayanai daya buƙata a kan Alhaji Rufa'i kuma ya gamsu da gaskiyar sa,yanzu yana tunanin kiran sa dan su tattauna akan batun Alhaji Shamsi tunda har yana tunanin shi Alhaji Shasin zai iya sanin kome ne ake rigima da neman sa ta kowace hanya,yinin ranar bai samu sukuni ba saboda yawan aiyukan da ya aiwatar a ranar duk wasu baya nai da yake bukata na mutanen da yake da alama akansu ya samu,dan haka ba tare da wani ɓata lokaci ba ya fara baza ma aikatan sa dan soma bincike akan su,
Bai samu shigowa gidan ba sai misalin goma na dare,a gajiye ya shiga ɓangaren sa,kai tsaye ya faɗa toilet ya sakarwa kansa shaya,sai da ya shirya tsaf kana ya nufi dinnin dan samawa cikin sa wani abun,
Tun ƙarfe takwas take duba agogo da leƙen window ko zataga dawowar sa amma shuru bai dawo ba ga yanayin garin da hadari alamu ya nuna dai yau zasu iya samun ruwa,dan ma dai damunar batayi nisa ba,
hakan ne yasa taji duk ta damu da rashin dawowar tasa ko lafiya yake?ta riga ta daɗe da sanin baya wuce wannan lokacin,shi yasa duk tabi ta damu,dan hararar hanyar tayi tare da cewa ko me yasa ma na damu bayan ko ya dawo ba lallai ne yayi min magana ba!'ta faɗa tamkar yana kusa da ita har da dan murguɗa baki,sai dai kuma duk da hakan ta kasa haƙurin shi yasa tana jin karar mota tayi saurin bude labilan tana leƙawa,wata sassanyan Ajiyar zuciya ta saki lokacin da ta tabbatar da cewa shine ya shigo, komawa tayi ta zauna abakin gadon tana tunanin ta yadda za ayi taje ɓangaren nasa tunda bata da sauran wani abu da zatayi acan ɗin,ta gumi ta zuba,can kuma sai ta miƙe, toilet ta shiga tayi brosh tana fitowa ta saka wata rigar bacci wadda ta tsaya iya cinyoyin ta daga nan tayi kwanciyar ta dan ta rasa hanyar da zatabi dan zuwa ɓangaren nasa,kalan ma inje ya koroni ta faɗa tana tura baki tare da shigewa cikin ɓargonta saboda yanayin iskar da ake ga dukka nin alamu dai ruwa zai iya zuba ako wane lokaci.
Abdallah ma dai a gurin sa kusan hakane,aiki yake amma hankalin sa yana kan duban hanya,tunanin zuwan ta yake akoda yaushe,sai dai har zuwa wannan lokacin baiji motsinta ba,ɗan tsaki yayi tare da janye laptop ɗin dake gaban sa,tashi yayi ya shiga toilet Jim kaɗan ya fito,ya ɗanyi abinda ya zama al dar sa,kana ya kwanta bayan yayi addu'oin sa,so yake ya kwanta ya ɗan rage bacci kafin ajima ya tashi yayi nafilfilu,sai dai kuma hakan ya gagara a wajen sa,mamakin yadda akayi ya kasa samun sukuni saboda yarinyar yake,ta wani bangaren kuma yana mamakin yadda ta iya kwanciya ita ɗaya,ya santa da tsoro gashi kuma yana gani kamar a kwai abinda yake damunta a kwanakin nan,lumshe idanun yayi yana jin wani irin yanayi a can cikin jikin sa,iska ce ta fara kaɗawa mai ƙarfi wadda take tasowa da ƙura,da sauri ya tashi ya kuma gyara windows ɗin ɗakin,duk abinda yakeyi zuciyar shi na wajen ta, gani yakeyi tausayin Bintu zai iya saka shi a wani hali,duba da yadda ya kasa sukuni ganin yau gaba ɗaya bai ganta ba,ga yanayin tsoronta dayake taɓa masa zuciya, ji yake tamkar yaje ya dubata,kasa zama yayi a ɗakin ya fito falo saboda yana ganin kamar zaifi samun kusanci da ita.
"Can cikin baccin ta ta dinga jin kamar ana ta shinta a matukar firgice ta farka tana son yin addu'a amma hakan ya gagara saboda yadda taji tamkar an rufe mata baki, cikin zuciyarta ta ta dinga ƙoƙarin yin addu'ar yayin da duk jikin ta rawa yake,ga wata irin walƙiya da ake yi da tsawa saboda ruwan da akafara tamkar da bakin ƙwarya,kuka ta saka tana laluben hanyar da zata sauka daga gadon dan ta kunna hasken ɗakin,da ƙyar ta samu ta lalubo wayar ta ta kunna tare da saukowa daga kan gadon hasken ɗakin ta fara kunnawa,raɓewa tayi a can lokon ɗakin babu abinda jikin ta yake sai rawa saboda tsananin tsoro,ji take kamar ba ita kaɗai ce acikin ɗakin ba, zuciyarta kamar zata faso kirjin ta haka take ji,
Gaba daya ya kasa samun sukunin zuciya ba ma kamar yadda yaga an tsuge da ruwa wanda yake tafe da tsawa da walƙiya,baya jin zuciyar shi zata barshi ya nutsu ya aiwatar da wani abu ba tare da yaje yagano amanar da Alhaji Baba ya bashi ba,cikin wani irin zafin nama ya miƙe tare da fita daga ɓangaren nasa,kai tsaye ya nufi ɗakinta yana kusanta ɗakin yanajin bugun zuciyar shi na ƙaruwa,a can lokon ɗakin ya hango ta a rakuɓe kamar wata ƙadangaruwa,tanajin buɗe ƙofar tasa ta ƙara ƙarfin kukan ta,tare da runtse idanun ta,cikin ta kun shi na zaratan maza ya nufo inda take,yayin da zuciyarta take ci gaba da wani irin bugu jira kawai take taji yadda Ubangiji zai yi ikon sa akanta,lokacin da ya ƙaraso kusa da ita sai taji yanayin bugun zuciyar ta ya sauya wani irin sanyi taji yana shigarta haka kuma hankalin ta yana kwanciya zuciyar ta na fita daga cikin mugun firgicin da ta shiga,zuba mata ido yayi batare da yayi mata magana ba,A hankali ta shiga buɗe idanunta saboda sassan yan ƙamshinsa da ƙofofin hancinta suka fara shaƙa wanda ya riga ya zama hadda a cikin hancinta,idanun ta ne suka sauka akan kyawawan ƙafafunsa da suke kwance luf cikin tattausan carpet ɗin dake shimfiɗe a ɗakin,cikin wani irin sauri wanda yake gauraye da wani irin shauƙi ta faɗa jikin sa tare da ƙankameshi tana kuma sakin wani marayan kuka mai cike da ban tausayi,riketa yayi sosai tare da ƙara gyara mata kwanciya,yana ɗan shafa bayanta wanda hakan yake nuni da calmin ɗin ta da yake son yi, bai ce mata ko mai ba sai ɗan sunkuyawa da yayi ya ɗauki wayar ta datake yashe a ƙasa,kana ya jawo hannun ta suka fita daga ɗakin,suna gaba da shiga falon sa,suka juyo muryar inno,ɗan tsayawa yayi saboda ƙarasowar innon gaban su,cikin yanayin damuwa tace"me yake faruwa ne Abdallah,me yasa mu Batular?ta jero masa tambayoyin tana riƙon Bintun da har yanzu hawaye basu daina saraftu akan kyakykyawar fuskarta ba,
Nafisa dai tana cikin tsaka mai wuya ta rasa inda tunanin ta zai tsaya maganganun Bintu ne suke ta kaiwa da kawowa cikin ƙwaƙwalwar ta,anya kuwa tana da wannan ƙwarin gwiwar a wajen Umar?duk da tana da tabbacin bai san komai akan abinda ta aikata ba,amma bata tunanin akwai wannan yardar da Bintu take faɗa a tsakaninsu,haka kawai take jin bata yadda da kanta a wajen Umar ɗin ba,to ko gwadawa zatayi ta gani ko zata dace?goge zufar dake ta tsatstsafo mata tayi,a fili ta furta,zan gwada Bintu zan ga yadda Umar ya ɗauke Ni da kuma kallon da yake min zan tambaye shi abinda yake damun sa zan gani ko zai gaya min indai kuwa ya faɗa min to tabbas zan ƙara kwantar da hankali na saboda na yadda ya amince dani ba kuma ya zargi na da aikata masa babban laifi.
Abdallah ya samu duk wasu bayanai daya buƙata a kan Alhaji Rufa'i kuma ya gamsu da gaskiyar sa,yanzu yana tunanin kiran sa dan su tattauna akan batun Alhaji Shamsi tunda har yana tunanin shi Alhaji Shasin zai iya sanin kome ne ake rigima da neman sa ta kowace hanya,yinin ranar bai samu sukuni ba saboda yawan aiyukan da ya aiwatar a ranar duk wasu baya nai da yake bukata na mutanen da yake da alama akansu ya samu,dan haka ba tare da wani ɓata lokaci ba ya fara baza ma aikatan sa dan soma bincike akan su,
Bai samu shigowa gidan ba sai misalin goma na dare,a gajiye ya shiga ɓangaren sa,kai tsaye ya faɗa toilet ya sakarwa kansa shaya,sai da ya shirya tsaf kana ya nufi dinnin dan samawa cikin sa wani abun,
Tun ƙarfe takwas take duba agogo da leƙen window ko zataga dawowar sa amma shuru bai dawo ba ga yanayin garin da hadari alamu ya nuna dai yau zasu iya samun ruwa,dan ma dai damunar batayi nisa ba,
hakan ne yasa taji duk ta damu da rashin dawowar tasa ko lafiya yake?ta riga ta daɗe da sanin baya wuce wannan lokacin,shi yasa duk tabi ta damu,dan hararar hanyar tayi tare da cewa ko me yasa ma na damu bayan ko ya dawo ba lallai ne yayi min magana ba!'ta faɗa tamkar yana kusa da ita har da dan murguɗa baki,sai dai kuma duk da hakan ta kasa haƙurin shi yasa tana jin karar mota tayi saurin bude labilan tana leƙawa,wata sassanyan Ajiyar zuciya ta saki lokacin da ta tabbatar da cewa shine ya shigo, komawa tayi ta zauna abakin gadon tana tunanin ta yadda za ayi taje ɓangaren nasa tunda bata da sauran wani abu da zatayi acan ɗin,ta gumi ta zuba,can kuma sai ta miƙe, toilet ta shiga tayi brosh tana fitowa ta saka wata rigar bacci wadda ta tsaya iya cinyoyin ta daga nan tayi kwanciyar ta dan ta rasa hanyar da zatabi dan zuwa ɓangaren nasa,kalan ma inje ya koroni ta faɗa tana tura baki tare da shigewa cikin ɓargonta saboda yanayin iskar da ake ga dukka nin alamu dai ruwa zai iya zuba ako wane lokaci.
Abdallah ma dai a gurin sa kusan hakane,aiki yake amma hankalin sa yana kan duban hanya,tunanin zuwan ta yake akoda yaushe,sai dai har zuwa wannan lokacin baiji motsinta ba,ɗan tsaki yayi tare da janye laptop ɗin dake gaban sa,tashi yayi ya shiga toilet Jim kaɗan ya fito,ya ɗanyi abinda ya zama al dar sa,kana ya kwanta bayan yayi addu'oin sa,so yake ya kwanta ya ɗan rage bacci kafin ajima ya tashi yayi nafilfilu,sai dai kuma hakan ya gagara a wajen sa,mamakin yadda akayi ya kasa samun sukuni saboda yarinyar yake,ta wani bangaren kuma yana mamakin yadda ta iya kwanciya ita ɗaya,ya santa da tsoro gashi kuma yana gani kamar a kwai abinda yake damunta a kwanakin nan,lumshe idanun yayi yana jin wani irin yanayi a can cikin jikin sa,iska ce ta fara kaɗawa mai ƙarfi wadda take tasowa da ƙura,da sauri ya tashi ya kuma gyara windows ɗin ɗakin,duk abinda yakeyi zuciyar shi na wajen ta, gani yakeyi tausayin Bintu zai iya saka shi a wani hali,duba da yadda ya kasa sukuni ganin yau gaba ɗaya bai ganta ba,ga yanayin tsoronta dayake taɓa masa zuciya, ji yake tamkar yaje ya dubata,kasa zama yayi a ɗakin ya fito falo saboda yana ganin kamar zaifi samun kusanci da ita.
"Can cikin baccin ta ta dinga jin kamar ana ta shinta a matukar firgice ta farka tana son yin addu'a amma hakan ya gagara saboda yadda taji tamkar an rufe mata baki, cikin zuciyarta ta ta dinga ƙoƙarin yin addu'ar yayin da duk jikin ta rawa yake,ga wata irin walƙiya da ake yi da tsawa saboda ruwan da akafara tamkar da bakin ƙwarya,kuka ta saka tana laluben hanyar da zata sauka daga gadon dan ta kunna hasken ɗakin,da ƙyar ta samu ta lalubo wayar ta ta kunna tare da saukowa daga kan gadon hasken ɗakin ta fara kunnawa,raɓewa tayi a can lokon ɗakin babu abinda jikin ta yake sai rawa saboda tsananin tsoro,ji take kamar ba ita kaɗai ce acikin ɗakin ba, zuciyarta kamar zata faso kirjin ta haka take ji,
Gaba daya ya kasa samun sukunin zuciya ba ma kamar yadda yaga an tsuge da ruwa wanda yake tafe da tsawa da walƙiya,baya jin zuciyar shi zata barshi ya nutsu ya aiwatar da wani abu ba tare da yaje yagano amanar da Alhaji Baba ya bashi ba,cikin wani irin zafin nama ya miƙe tare da fita daga ɓangaren nasa,kai tsaye ya nufi ɗakinta yana kusanta ɗakin yanajin bugun zuciyar shi na ƙaruwa,a can lokon ɗakin ya hango ta a rakuɓe kamar wata ƙadangaruwa,tanajin buɗe ƙofar tasa ta ƙara ƙarfin kukan ta,tare da runtse idanun ta,cikin ta kun shi na zaratan maza ya nufo inda take,yayin da zuciyarta take ci gaba da wani irin bugu jira kawai take taji yadda Ubangiji zai yi ikon sa akanta,lokacin da ya ƙaraso kusa da ita sai taji yanayin bugun zuciyar ta ya sauya wani irin sanyi taji yana shigarta haka kuma hankalin ta yana kwanciya zuciyar ta na fita daga cikin mugun firgicin da ta shiga,zuba mata ido yayi batare da yayi mata magana ba,A hankali ta shiga buɗe idanunta saboda sassan yan ƙamshinsa da ƙofofin hancinta suka fara shaƙa wanda ya riga ya zama hadda a cikin hancinta,idanun ta ne suka sauka akan kyawawan ƙafafunsa da suke kwance luf cikin tattausan carpet ɗin dake shimfiɗe a ɗakin,cikin wani irin sauri wanda yake gauraye da wani irin shauƙi ta faɗa jikin sa tare da ƙankameshi tana kuma sakin wani marayan kuka mai cike da ban tausayi,riketa yayi sosai tare da ƙara gyara mata kwanciya,yana ɗan shafa bayanta wanda hakan yake nuni da calmin ɗin ta da yake son yi, bai ce mata ko mai ba sai ɗan sunkuyawa da yayi ya ɗauki wayar ta datake yashe a ƙasa,kana ya jawo hannun ta suka fita daga ɗakin,suna gaba da shiga falon sa,suka juyo muryar inno,ɗan tsayawa yayi saboda ƙarasowar innon gaban su,cikin yanayin damuwa tace"me yake faruwa ne Abdallah,me yasa mu Batular?ta jero masa tambayoyin tana riƙon Bintun da har yanzu hawaye basu daina saraftu akan kyakykyawar fuskarta ba,