Sashe 104
Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A can falon Hajja kuwa bayan da ya tabbatar da Taufiƙa ta bar wajen,sai ya ɗan kuma gyara zaman shi cikin nutsuwa yace"Hajjah dama nazo ne akan maganar Dadyna!'yadda ta zuba masa ido da yanayin ruɗewa shine yaso bashi ƴar dariya,sai dai kuma yayi ƙoƙarin maida ta tunda dama ba al aldarshi bace,cikin ɗan ruɗewar da ta farayi tace"Abubakar ke nan?yace"wanda kika tafi dashi jiya!'ya faɗa idanun sa akan Bintu wadda ita kuma ta zubawa Hajja nata idon dan har yanzu al'amarin mamaki yake bata, bata taɓa yiwa Hajja kallon muguwaba amma sai gashi ya tabbata cewa itace makirar cikin zuri'ar Alhaji Baba,Hajja kuwa da kyar ta iya aro jarumta wanda duk da haka tsoran ta da rashin gaskiyar ta bai kasa bayyanuwa ba,cikin kasa haɗa ido da ɗayansu tace"Abdallah an samu akasi fa ban san ta inda abun ya juya ba saboda wannan mutumin ba Abubakar bane,kuma ina tunanin duk daga sharrin Habibu ne!'ta juya maganar dan san tabbatar da zargin ko sun gano makircinta,cikin dabi ar sa ta rashin gano ainahin abinda yake zuciyarsa,yace"Hajja yanzu kina nufin mun kuma rasa Dady?cike da mamaki take kallon sa,kana tace"amma ai na ɗauka duk ku kuka shirya hakan?ya akai kika san haka?ya kuma jefo mata wata tambayar,cikin ruɗewa da san kama kanta tace"ai shi ya faɗa da bakin sa!'a wannan karon Bintu ce ta jefo mata tata tambayar da cewa to Hajja ya akayi ya faɗa miki bayan wannan abun sirrine tsakanin su su uku?cike da tashin hankali take duban Bintu ta kasa bata amsar tambayar ta,Bintu bata saurari abinda zata ce ba ta cigaba da cewa,kinga hakan yana nufin an so yi masa wani abune da zai iya cutar dashi shi kuma yaga kawai gara ya bayyana cewa bashi ne Dady ba!'wani irin kallon tashin hankali tabi Bintu dashi kana tace"yanzu me kike nufi?nice zanyi ƙoƙarin cutar dashi?da sauri Bintu ta girgiza kanta tare da cewa abun ne akwai mamaki da ɗaure kai Hajja saboda mu ba irin bayanan ki Dady jafar yayi mana ba, hasali ma munzo ne dan sanar dake abin da ke faruwa,sai kuma muka ji saɓanin abin da ya kawo mu daga bakin ki,bayan kuma kince an ɗauke Dadyn!'Bintu ta ƙarasa maganarta da tsare Hajja da idanuwan ta irin na Abdallah,wata irin zufa ce ta shiga ketowa Hajja tana kuma mamakin yadda yara ƙananu suke son mozanta ta a fakaice,gashi sunƙi bata damar gano manufar su,ganin halin da tashiga ne yasa Abdallah miƙewa tare da cewa,shike nan Hajja yanzu ina shi wan can da muka saka a madadin Dady?da sauri tace"ai yana nan zan sa akawoshi!'Bintu tace"meyasa da kikaga ba Dady bane baki barshi yay tafiyarsa ba?a yanzu kam anzo gaɓar da take neman fito da kanta, kasa bawa Bintu amsa tayi saboda bata da amsar,dan haka shuru tayi tana rarraba ido, Abdallah ya kama hanyar fita daga falon ba tare da ya kuma tankawa ba.
Suna fita taji kamar an zareta daga cikin masifa,kai yaran nan sun iya tambayoyin da zasu saka mutum ya kama kansa sai kace wasu lauyoyi ko ƴan jarida,karma yarinyar nan taji labari,hatsabibiyar yarinya kawai,gaba ɗaya dai a wannan rana nutsuwar Hajja ta ƙare ta rasama ta kaimaiman tunanin da zatayi akan wannan al'amari,bata taɓa tunanin cewa akwai ranar da zata kwaɓe mata ba,bata taɓa tsammanin asirin ta zai iya neman tonuwa ba,kuma ko a yanzun ma bata tunanin haka a ranta dole zata san mafitawa rayuwarta,
Ɗan tsayawa yayi Bintu ta ƙaraso,kallon juna sukayi Sai kawai suka saka dariya,abinda ban taɓa gani ba a fuskar Abdallah,lallai yau farin ciki yay farin ciki,A hankali Bintu ta shiga gwada yadda Hajja tayi tun shigar su falon, Abdallah kuwa Binta kawai yake da wani kasalallan kallo yana murmushin gefan baki,da dai yaga ba da katawa zatayi ba kawai sai ya ja hannun ta suka cigaba da tafiya har zuwa sashen Hajiya Babba,
Kallo take binsu dashi wanda yake nuni da tsananin ƙaunar da take musu kuma har ta kasa ɓoyuwa cikin idanun ta,rungume Bintu tayi tana shafa kanta,ita kuma kamar wata mage tayi wani luf sai faman lum-lumshe idanuwa takeyi,sun ɗan daɗe a ɓangaren Hajiya Babba daga nan sukayi mata sallama suka koma sashen inno,sai da yaje yayi Sallah ya dawo kana ya samu Abincin inno najiran shi,ita Bintu tuni ma har taci nata saboda yunwar da take ji,shima zama yayi yaci, kana ya miƙe tare da ɗan kallon inda Bintu take zaune,so yake ya ɗan fita yaje gidan da yakai su Ummi,ƙarasowa yayi inda take zaune ta ƙurawa tv Ido kamar tanaso ta ciro mutanen dake ciki,zama yayi a kusa da ita tare da ɗan taɓa ta zabura tayi cikin tura baki tace"nikam ka bani tsoro ma!'yace"fita zanyi amma bazan jima ba!'da sauri tace"ba tare zamu tafiba?girgiza mata kai yayi tare dayi mata alama da girarsa, karyar da kai tayi kamar wata sabuwar marainiya,kana tace"ayya Yah Abdallah kasan fa ko ina tare muke zuwa meyasa yanzun bazaka dani ba? kai tsaye ya bata amsa da cewa nan ba gurin zuwan matan aure bane!'zaro idanu tayi tare da cewa to ai kai ma mijin aurene nikam tsoro nakeji bazan iya zama ba!'tashi ki tafi wajen inno!'ya faɗa yana miƙewa,tashi tayi jiki a sanyaye sai murza idanu da takeyi alamun dai tana son yin kuka,tsayawa yayi tare da zuba mata ido,shifa sam bashi da wata zarra akan abinda ya shafi BINTU,shi yasa yake kokarin ganin yayi abinda zai faranta mata,itace sanadin farin cikin sa da duk wata walwala da ya tsinci kansa aciki,kamo hannun ta yayi a hankali yayi mata masauƙi cikin faffaɗan ƙirjinsa,wani abu yake ji game da ita yana daɗa tsikarar zuciyarsa,mutsu mutsun da take ne yasa shi ɗago kanta sai yaga hawaye shaɓe shaɓe kan kyakkyawar fuskar ta,bakinsa ya kai kan fuskarta ya shiga share mata hawayen da harshensa, wanda ɗumin harshen nasa ya saukar mata da wata irin kasala da mutuwar jiki, cikin wata irin murya yake cewa ke Bint kin san zafin wannan kuwa kin san raɗadin zubar wayenki kuwa?bata fahimci mai yake nufi ba dan haka sai ta shiga girgiza masa kai,ɗan ware idanun sa yayi akan ta,daga nan kuma ya samu kansa da zura harshen sa cikin bakinta,take jikin ta ya shiga karkarwa,ganin ƙafafunta na san kasa ɗaukar ta yasa ta kuma rikoshi da kyau daga nan salon ya kuma sauyawa da wani irin mayataccen sumba mai ruɗa zuciya da gangar jiki,ba ga ogan ba,baga yarinyar ogan ba,wani irin mahaukacin salo yakewa Bint din tasa wanda shi kansa baibsan daga ina ya iyasaba,nema yake ya kasa control ɗin kansa akan Bintu,duk wani ƙarfin shi ƙare wa yake a duk lokacin da ya kasance da ita,suna cikin wannan halin basu ankara ba saijin kiran sallar magriba sukayi a tsakar kansu,wanda dole ta sa su rabuwa da juna,kawar da kanta tayi saboda kunyar abin da tayi,leƙa fuskarta yayi tare da cewa my ukty, na fasa fitar bazan barki ke ɗaya ba,da sauri ta juyo da fuskarta gareshi sai caraf ta kuma tsinkayar bakinsa cikin nata,amma ba sha yake ba tsayawa yayi yana kallon cikin idanun ta da ta kasa kallon sa,a hankali ya miƙe da ita ajikin sa ya nufi hanyar bedroom ɗinsa,sai da ya shiga kana ya sake ta tare da shigewa toilet,yana fitowa yace"kiyi alwala masallaci zanje yanzu zan dawo!'kai ta ɗaga mishi kamar wata ƙadangaruwa dan bakinta da jikin ta duka amace suke da irin zazzafan kulawar Abdallah agareta.
Duk da cewa zuciyar ta ba anutse take ba hakan bai hanata son aiwatar da niyar ta ba,shirinta takeyi ta haɗa duk wani abu da zai iya zame mata arziki dan wucewa dashi,jira takeyi kawai gari ya waye ta fece,tana cikin wannan shirin kuma katsaham ta samu waya daga Alhaji Baba cewa yana buƙatar ta gobe da misalin goma a falonsa,(kasancewar Abdallah ya dawo da taron da safiya saboda wani tunani da yayi)jikin ta asanyaye ta amsa tare da ajiye wayar,ta gumi ta zabga tana tunanin abinda yasa ake hada taro rana tsaka,wata zuciyar tace mata ko dai mutuwar Umar ce ta samesu shi yasa ake son sanar da ita cikin nutsuwa, wannan tunanin da tayi ne yasa ta kwashewa da wata shegiyar dariya,wadda ita agurin ta ta cin nasara ce,yanzu hankalin ta ya kwanta sai kuma tsimayin abinda zai faru gobe.
Yana cikin filin jirgin sama na malam Aminu Kano ya samu wayar mahaifin sa,nasan kasancewar sa a gobe ƙarfe goma na safe cikin falon sa,cikin ladabi ya sanar da Alhaji Baba ai yana Kano saukar sa ke nan dan haka insha Allahu zai halarci taron,daga nan jirgin da zai kaishi Abuja ya wuce,yana sauka bai wuce ko ina ba sai gidan dasu Hajja suke,cikin girmamawa ya sanar da Hajjo cewa su shirya zai zo ya ɗauke su gobe dan zuwa estate zai gabatar dasu a wajen Alhaji Baba,
Duk wanda ya kamata yasan da wannan gagarumin taron ya sani har ma waɗan da Abdallah baicewa Alhaji Baba ya sanar dasuba, duk saida yasanar dasu ƴaƴan Hajja waɗan da suke nesa da yawa ne kawai bai ce lallai sai sunzo ba,Hajja kuwa ba ƙaramin tashin hankali ta shiga ba,babu yadda batayi da Alhaji Baba ya sanar da ita ko taron na meye,amma yaƙi cewa da ita komai, hasalima sai ya ɓoye mata cewa Abdallah ne ya haddasa taron,ganin yaki sanar da ita dalilin kawai sai ta rabu dashi dan bata son ta tsaurara bincike har ya ɗora mata ayar tambaya,waɗan da basu razana da kiran Alhaji Baba sune masu zuciziyar zinare, zuciyar da babu komai acikin ta sai Alkhairi,to Allah dai ya jiyar da mu Alkhairi a wannan zama na falon Alhaji Baba cewar da yawa daga cikin ahalin wannan estate ke nan.
Suna fita taji kamar an zareta daga cikin masifa,kai yaran nan sun iya tambayoyin da zasu saka mutum ya kama kansa sai kace wasu lauyoyi ko ƴan jarida,karma yarinyar nan taji labari,hatsabibiyar yarinya kawai,gaba ɗaya dai a wannan rana nutsuwar Hajja ta ƙare ta rasama ta kaimaiman tunanin da zatayi akan wannan al'amari,bata taɓa tunanin cewa akwai ranar da zata kwaɓe mata ba,bata taɓa tsammanin asirin ta zai iya neman tonuwa ba,kuma ko a yanzun ma bata tunanin haka a ranta dole zata san mafitawa rayuwarta,
Ɗan tsayawa yayi Bintu ta ƙaraso,kallon juna sukayi Sai kawai suka saka dariya,abinda ban taɓa gani ba a fuskar Abdallah,lallai yau farin ciki yay farin ciki,A hankali Bintu ta shiga gwada yadda Hajja tayi tun shigar su falon, Abdallah kuwa Binta kawai yake da wani kasalallan kallo yana murmushin gefan baki,da dai yaga ba da katawa zatayi ba kawai sai ya ja hannun ta suka cigaba da tafiya har zuwa sashen Hajiya Babba,
Kallo take binsu dashi wanda yake nuni da tsananin ƙaunar da take musu kuma har ta kasa ɓoyuwa cikin idanun ta,rungume Bintu tayi tana shafa kanta,ita kuma kamar wata mage tayi wani luf sai faman lum-lumshe idanuwa takeyi,sun ɗan daɗe a ɓangaren Hajiya Babba daga nan sukayi mata sallama suka koma sashen inno,sai da yaje yayi Sallah ya dawo kana ya samu Abincin inno najiran shi,ita Bintu tuni ma har taci nata saboda yunwar da take ji,shima zama yayi yaci, kana ya miƙe tare da ɗan kallon inda Bintu take zaune,so yake ya ɗan fita yaje gidan da yakai su Ummi,ƙarasowa yayi inda take zaune ta ƙurawa tv Ido kamar tanaso ta ciro mutanen dake ciki,zama yayi a kusa da ita tare da ɗan taɓa ta zabura tayi cikin tura baki tace"nikam ka bani tsoro ma!'yace"fita zanyi amma bazan jima ba!'da sauri tace"ba tare zamu tafiba?girgiza mata kai yayi tare dayi mata alama da girarsa, karyar da kai tayi kamar wata sabuwar marainiya,kana tace"ayya Yah Abdallah kasan fa ko ina tare muke zuwa meyasa yanzun bazaka dani ba? kai tsaye ya bata amsa da cewa nan ba gurin zuwan matan aure bane!'zaro idanu tayi tare da cewa to ai kai ma mijin aurene nikam tsoro nakeji bazan iya zama ba!'tashi ki tafi wajen inno!'ya faɗa yana miƙewa,tashi tayi jiki a sanyaye sai murza idanu da takeyi alamun dai tana son yin kuka,tsayawa yayi tare da zuba mata ido,shifa sam bashi da wata zarra akan abinda ya shafi BINTU,shi yasa yake kokarin ganin yayi abinda zai faranta mata,itace sanadin farin cikin sa da duk wata walwala da ya tsinci kansa aciki,kamo hannun ta yayi a hankali yayi mata masauƙi cikin faffaɗan ƙirjinsa,wani abu yake ji game da ita yana daɗa tsikarar zuciyarsa,mutsu mutsun da take ne yasa shi ɗago kanta sai yaga hawaye shaɓe shaɓe kan kyakkyawar fuskar ta,bakinsa ya kai kan fuskarta ya shiga share mata hawayen da harshensa, wanda ɗumin harshen nasa ya saukar mata da wata irin kasala da mutuwar jiki, cikin wata irin murya yake cewa ke Bint kin san zafin wannan kuwa kin san raɗadin zubar wayenki kuwa?bata fahimci mai yake nufi ba dan haka sai ta shiga girgiza masa kai,ɗan ware idanun sa yayi akan ta,daga nan kuma ya samu kansa da zura harshen sa cikin bakinta,take jikin ta ya shiga karkarwa,ganin ƙafafunta na san kasa ɗaukar ta yasa ta kuma rikoshi da kyau daga nan salon ya kuma sauyawa da wani irin mayataccen sumba mai ruɗa zuciya da gangar jiki,ba ga ogan ba,baga yarinyar ogan ba,wani irin mahaukacin salo yakewa Bint din tasa wanda shi kansa baibsan daga ina ya iyasaba,nema yake ya kasa control ɗin kansa akan Bintu,duk wani ƙarfin shi ƙare wa yake a duk lokacin da ya kasance da ita,suna cikin wannan halin basu ankara ba saijin kiran sallar magriba sukayi a tsakar kansu,wanda dole ta sa su rabuwa da juna,kawar da kanta tayi saboda kunyar abin da tayi,leƙa fuskarta yayi tare da cewa my ukty, na fasa fitar bazan barki ke ɗaya ba,da sauri ta juyo da fuskarta gareshi sai caraf ta kuma tsinkayar bakinsa cikin nata,amma ba sha yake ba tsayawa yayi yana kallon cikin idanun ta da ta kasa kallon sa,a hankali ya miƙe da ita ajikin sa ya nufi hanyar bedroom ɗinsa,sai da ya shiga kana ya sake ta tare da shigewa toilet,yana fitowa yace"kiyi alwala masallaci zanje yanzu zan dawo!'kai ta ɗaga mishi kamar wata ƙadangaruwa dan bakinta da jikin ta duka amace suke da irin zazzafan kulawar Abdallah agareta.
Duk da cewa zuciyar ta ba anutse take ba hakan bai hanata son aiwatar da niyar ta ba,shirinta takeyi ta haɗa duk wani abu da zai iya zame mata arziki dan wucewa dashi,jira takeyi kawai gari ya waye ta fece,tana cikin wannan shirin kuma katsaham ta samu waya daga Alhaji Baba cewa yana buƙatar ta gobe da misalin goma a falonsa,(kasancewar Abdallah ya dawo da taron da safiya saboda wani tunani da yayi)jikin ta asanyaye ta amsa tare da ajiye wayar,ta gumi ta zabga tana tunanin abinda yasa ake hada taro rana tsaka,wata zuciyar tace mata ko dai mutuwar Umar ce ta samesu shi yasa ake son sanar da ita cikin nutsuwa, wannan tunanin da tayi ne yasa ta kwashewa da wata shegiyar dariya,wadda ita agurin ta ta cin nasara ce,yanzu hankalin ta ya kwanta sai kuma tsimayin abinda zai faru gobe.
Yana cikin filin jirgin sama na malam Aminu Kano ya samu wayar mahaifin sa,nasan kasancewar sa a gobe ƙarfe goma na safe cikin falon sa,cikin ladabi ya sanar da Alhaji Baba ai yana Kano saukar sa ke nan dan haka insha Allahu zai halarci taron,daga nan jirgin da zai kaishi Abuja ya wuce,yana sauka bai wuce ko ina ba sai gidan dasu Hajja suke,cikin girmamawa ya sanar da Hajjo cewa su shirya zai zo ya ɗauke su gobe dan zuwa estate zai gabatar dasu a wajen Alhaji Baba,
Duk wanda ya kamata yasan da wannan gagarumin taron ya sani har ma waɗan da Abdallah baicewa Alhaji Baba ya sanar dasuba, duk saida yasanar dasu ƴaƴan Hajja waɗan da suke nesa da yawa ne kawai bai ce lallai sai sunzo ba,Hajja kuwa ba ƙaramin tashin hankali ta shiga ba,babu yadda batayi da Alhaji Baba ya sanar da ita ko taron na meye,amma yaƙi cewa da ita komai, hasalima sai ya ɓoye mata cewa Abdallah ne ya haddasa taron,ganin yaki sanar da ita dalilin kawai sai ta rabu dashi dan bata son ta tsaurara bincike har ya ɗora mata ayar tambaya,waɗan da basu razana da kiran Alhaji Baba sune masu zuciziyar zinare, zuciyar da babu komai acikin ta sai Alkhairi,to Allah dai ya jiyar da mu Alkhairi a wannan zama na falon Alhaji Baba cewar da yawa daga cikin ahalin wannan estate ke nan.