Sashe 12
Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan shiru na dan wasu mintoci da fara tafiyarsu dady ya dan numfasa kana yace" abdallah ina mai baka shawara da kayi hakuri da duk abinda zaka gani ko katarar acikin gidan nan kasan shi gidane na jama'a da hada-hadarsu dan haka dole kajure hayaniya domin samun nasara akan kyakykyawan kudurinmu, anbaka bangare guda asashen kakarku hajiya zainab (inno) saboda itace babu kowa agabanta amma duk da haka kusan rabin yan mata da samarin gidan anan suke tarewa domin kamar nanne majalisarsu baccine kawai ke maidasu sashensu, to ni dai bansan meyasa aka baka masauki abangarenta ba,amma ni hakan yayi mun kasancewar kowa da kowa yana shiga bangarenta ma ana kowa nata ne tana kuma mu'amala da dukkan surukan gidan, kaga kenan a hasashena hakan wata babbar damace agareka da zaka samu kusanci da kowa na gidan zaka kuma kula da takun kowa, nasan kai mai basirane abdallah da kuma dogon hange bana jin ko dar akanka nasan insha Allah kaine da nasara akan makiyanku dan haka ka kula da ta kun kowa ko kallo mutum yayi agidan nan da ma'anarsa,ina maka fatan alkhari da nasara akan dukkanin rayuwar ka,san nan kayi min magana akan cewa kar gane wani abu akanka saboda kamannin ka da gidan da kuma mahaifinka, to wannan bako mai bane dan dukkanin su kansu ajuye yake anriga anmantar da dasu, sum manta wanene abubakar da wani gudan jininsa dan haka babu wanda zai ganeka sai wanda yay abun da kuma magoya bayansa dan haka inaso kasa ido sosai dan nasan su zasu iya ganoka amma bazasu taba nuna wata alama ba, suna da shiri akanka abdallah ka kiye!'
Adai-dai lokacin kuma suka karaso dan kareran get din da zai shiga da kai cikin ainahin estate din manyan masu gadi sojoji kusan biyarne akofar, kasancewar babu wanda baisan dady jafar ba yasa suka barsu suka shige kai tsaye zuwa get na biyu wanda daga shine kuma zakai ta ganin get-get na bangare bangare, batare da wani dogon bincikeba kai tsaye akabarsu suka shige bangaren Alhaji baba.
Alokaci daya abdallah yaji kansa yay wani irin mummunan sarawa da karfi tamkar ana buga masa guduma har sai da ya kai hannunsa ya dafe goshinsa, fahimtar hakanda dady yayi take yashiga karanto masa addu'a shima ahankali yake karanta innalillahi'wa'inna'ilaihiraji'un tare da allahumma ajirni fil musibati wa'aklifini khairan minha da la'ilaha'illa'anta subhanaka inni kuntu minazzalumin.kana ahankali sukayi sallama adai-dai lokacin da kofar ta zuge suka saka kai, yayin da sukaji wata kamilalliyar murya tana amsa musu,
Guri suka samu gaba dayansu akasa suka zube, saboda tsananin girmamawa ga tsohon dattijo mai tsananin mutumci da kamala.
Bayan sun gama gaisawa da dady ne, abdallah ya karayin kasa da kanshi kana ya gaishe da Alhaji baba, amsawa yayi cikin farin ciki da wani irin shauki na kauna da bege da lokaci daya ta saukarwa Alhaji baba.
Hannu ya mikawa abdallah yana cewa"zomana jikana abin alfaharina matso kaji dumin jikin kakanka!'abdallah bai kasance ragon namiji mai raunin zuciyaba amma ayau akuma gaban dattidon nan jiyake tamkar zai zubda hawayen tsananin tausayinsa da kuma kewarsa tare da zunzurutun kaunarsa hakanan yaji yana fargabar ranar da zai san cewa ya haifi bara gurbi acikin yayansa ya kuma hada iri da gubatacciyar zuria yana tsoron kar saboda bakin ciki ya hadiyi zuciya arasashi kowa ya huta.
Jin maganar Alhaji babane ya katseshi daga
dogon tunanin da ya fada yace" abdallah jikana kasaki jikinka kadauka cewa kana cikin gidanku kuma cikin ahlinkane, duk abinda zakayi kayishi kai tsaye amatsayinka na dan gidannan na kuma baka umarni duk wanda yay ba dai-dai ba acikin kannenka ka hukuntashi amatsayinka na babban yaya tunda yanzu babu wani babba saurayi da yay saura agaban mu duk suna da iyali!'ya karasa fada yana mai shafa kan abdallah.
Abdallah jinjina kai kawai yayi tare da kwantar da kanshi akafadar kakan nasa yana mai jin wata yar sangarta na shigarsa nakasan cewarsa tare da kakan nasa.
Cikin lokaci kankani babban holl dinsu da suke taruwa dan taro muhimmi ya cika makil, saboda sanarwar Alhaji baba na cewar duk wanda yake nan kusa har yan kaduna yana bukatar ganinsu cikin gaggawa,wadanda sukai nisa kamar na kano ko wata kasa haka akayi connecting dan suma su sami damar jin abinda ya hada taron.
Kowa ya nutsu yana sauraron bayanin Alhaji baba ta macrophon,kowa ya gamsu da abinda yasanar dasu har wasu suna cewa ai da ko awaya yasar musu ma ya wadatar.
Alhaji baba yayi gyaran murya kana yace"dalilina na cewa lallai sai kowa yazo shine inaso ku dauki abun da muhimmanci kuma kowa yasan cewa abdallah shima jika naneeee
(Waiyo ni fadima sauri nayi na zubawa mutanen dake dankare a holl din Ido ko zan samu nasarar riga su abdallah gano bara gurbin cikin zuriar Alhaji balarabe sai dai kash babu wanda ya nuna wani abu afuskarsa da zai sa na diga masa ayar tambaya,kai wadannan mutane ko suwaye akwai shu'umai)
Abdallah ya zubawa fuskoki da yawa ido ko shima zai fahimci wani sauyi daga wata fuska saboda jin furucin Alhaji baba, sai dai shi din ma babu abinda ya fuskanta.
Ahlin Alhaji balarabe sun karbi abdallah da hannu bibiyu, anan ya dinga ganin wata kauna akan fuskokinsu kansa ya daure matuka dan yakasa fuskantar gaskiyar kauna da akasinta, duk abu daya yake gani dauke a fuskokinsu, dady ane, ma da dady jafar yasan bai gamsu da zuwan abdallah ba, bai fahimci komai afuskarsa ba.
Ahaka taron ya watse kowa na kokarin ganin ya nunawa abdallah shi mai kaunarsa ne baka da zuci, Alhaji baba da kansa ya rakashi har bangaren inno ya sadashi da hadadden dakinsa kana yace" yayi wanka ga abinci nan ya dade da rigashi zuwa sannan ya kwanta ya huta.
Godiya abdallah yayi wa Alhaji baba,shi kuma ya juya ya fita yana mai tunasar dashi karya sake yi mai godiya. wadawa yayi bisa lumtsumeman gadon da yasamu wata iriyar shimfida ta alfarma da wani hadadden bedsheet,kansane yaji yana neman barewa gida biyu saboda yawan hayaniyar da yashaka yau shi tunda yake bai taba shiga hayaniya irin wannan ba dole dady yay ta bashi hakuri da tausarsa akan ya jure ashe yasan komai akan yawan hayaniyar gidan anya kuwa zai jura?
Tashi yay yana layi ya nufi bayi jikinsa duk babu kwari hutu kawai yake bukata yanzu dan wannan hayaniyar tasa duk san aikinsa yaji ba zai iya fita aiki gobe ba.
Tunda aka sauke ta atashar bulayi kawai take acikinta batasan ko Ina ba batasan kowa ba, batasan inda zata nufa ba, can kusa da wata mai abinci ta samu ta rabe sai baza manyan idanunta take taga ta inda Allah zai kawo mai agazamata, da dai taga zaman take ga yunwa na nukurkusarta kawai sai taciro naira dari biyu ta kara matsawa kusa da mai abincin tare da yi mata sallama!' alokaci daya kuma tana mika mata gudar dari biyu tace"abani abinci!matar mai abinci ta bi bintu da wani irin kallon yau naga India mai jin hausa,girgiza kanta matar tayi tana mai cewa' yi hakuri 'yan mata bamu da irin abincin ku anan sai dai kije restaurant' a canne suke yin kowane irin abinci!'ta karasa maganar da juyawa tana kallon mutanen da suka taru arumfar abincin nata, kallon bintu suke cike da farinciki yayin da wasu suke musun cewa ai amisha ce wasu kuwa suce ai pretty ce,
Bintu ta rasa inda zatasa kanta kawai sai tafashe da kuka!' saboda ita bata saba shiga cikin jama'a ba, balle wadannan da suke tai mata surutu aka, ganin haka yasa wani babban dan union ya sa wasu samari suka kori mutanen,
Matar nan mai abinci ta dubi bintu tace" yan mata Ina zakijene na ga kamar kin dade acikin tashar nan ko kin manta hanyane?da sauri bintu ta daga kanta!' matar tace"ayya to bari nasa yarinyata ta nuna miki hanya,juyawa tayi ta kalli budurwar dake tsaye agefanta tana saurarensu, tace" basira maza jeki ki nuna mata hanya ki saka ta a keke napep, ta fada masa sunan anguwar da zai kaita dan naga alama bakuwace batasan ko'inaba!'ta mikawa basira wata leda tana cewa" ga wannan sai ki bata idan zata iya cin abincin mu!'bintu cikin shagwababbiyar muryarta da ta riga ta sangarce agun baffa da fafi tace"na gode mama Allah ya saka miki da alkhari!' mai abinci cikin jin dadi tace"babu damuwa ki gaida gida Allah ya kiyaye!'ta amsa da amin tare da jin dadin karamcin da mama mai abinci tayi mata.
Tun kan ma su fita daga cikin tashar suka samu mai napep,basira ta dubi bintu tace" wace anguwa za'akaiki? bintu shiru tayi tana son ta tuna sunan anguwar da fafi ya gaya mata amma ikon Allah shaf ta manta,mai keke yace"Ina gafa wannan hausarce tayi mata nauyi bari na lissafo mata sunan anguwanni ko zataji ta fada!'kafun ma basira ta tanka masa ya shiga lissafo manyan anguwannin masu kudi da fada aji, bintu tanajinsa har yanzu bai fadi makamanciyar sunan anguwar da zataje ba .gajiyar da tayine yasa yana cewa'mai tama sule tace"muje nan zani!'me napep yace au wai dama kinajin hausa kan uba alkur an ban zaci ta'iya hausaba kudurar Allah kenan!'basira tace da Allah mazarkwaila sarkin zaki wuce kuje ka kaita ka'ishi mutane da surutu kamar ba gobe!'dariya yayi kawai dan yasan gaskiya ta fada, mikawa bintu ledar take away tayi gami dayiwa junansu sallama,mai napep yaja suka wuce.
Hajiya anzo mai tama a'ina zaki sauka?ahankali bintu take bin anguwar da kallo,tare da manya-nanyan gidajen da sukayi mata kawanya,tunani take idan ta sauka to Ina zata nufa?wa tasani acikin wannan haddadiyar anguwa ?amma abin da tasanine dole ta sauka tunda itane ta zabi akawota nan din, dan haka tace da mai napep ya sauketa,burki yaja akofar wani haddaden gida yana mai cewa" hajiya kudinki naira dari uku!' batare da tace"komai ba ta mika masa dari biyun dazu da mai abinci bata karba ba,yana amsa ya figi napep dinsa ya kara gaba.
Adai-dai lokacin kuma suka karaso dan kareran get din da zai shiga da kai cikin ainahin estate din manyan masu gadi sojoji kusan biyarne akofar, kasancewar babu wanda baisan dady jafar ba yasa suka barsu suka shige kai tsaye zuwa get na biyu wanda daga shine kuma zakai ta ganin get-get na bangare bangare, batare da wani dogon bincikeba kai tsaye akabarsu suka shige bangaren Alhaji baba.
Alokaci daya abdallah yaji kansa yay wani irin mummunan sarawa da karfi tamkar ana buga masa guduma har sai da ya kai hannunsa ya dafe goshinsa, fahimtar hakanda dady yayi take yashiga karanto masa addu'a shima ahankali yake karanta innalillahi'wa'inna'ilaihiraji'un tare da allahumma ajirni fil musibati wa'aklifini khairan minha da la'ilaha'illa'anta subhanaka inni kuntu minazzalumin.kana ahankali sukayi sallama adai-dai lokacin da kofar ta zuge suka saka kai, yayin da sukaji wata kamilalliyar murya tana amsa musu,
Guri suka samu gaba dayansu akasa suka zube, saboda tsananin girmamawa ga tsohon dattijo mai tsananin mutumci da kamala.
Bayan sun gama gaisawa da dady ne, abdallah ya karayin kasa da kanshi kana ya gaishe da Alhaji baba, amsawa yayi cikin farin ciki da wani irin shauki na kauna da bege da lokaci daya ta saukarwa Alhaji baba.
Hannu ya mikawa abdallah yana cewa"zomana jikana abin alfaharina matso kaji dumin jikin kakanka!'abdallah bai kasance ragon namiji mai raunin zuciyaba amma ayau akuma gaban dattidon nan jiyake tamkar zai zubda hawayen tsananin tausayinsa da kuma kewarsa tare da zunzurutun kaunarsa hakanan yaji yana fargabar ranar da zai san cewa ya haifi bara gurbi acikin yayansa ya kuma hada iri da gubatacciyar zuria yana tsoron kar saboda bakin ciki ya hadiyi zuciya arasashi kowa ya huta.
Jin maganar Alhaji babane ya katseshi daga
dogon tunanin da ya fada yace" abdallah jikana kasaki jikinka kadauka cewa kana cikin gidanku kuma cikin ahlinkane, duk abinda zakayi kayishi kai tsaye amatsayinka na dan gidannan na kuma baka umarni duk wanda yay ba dai-dai ba acikin kannenka ka hukuntashi amatsayinka na babban yaya tunda yanzu babu wani babba saurayi da yay saura agaban mu duk suna da iyali!'ya karasa fada yana mai shafa kan abdallah.
Abdallah jinjina kai kawai yayi tare da kwantar da kanshi akafadar kakan nasa yana mai jin wata yar sangarta na shigarsa nakasan cewarsa tare da kakan nasa.
Cikin lokaci kankani babban holl dinsu da suke taruwa dan taro muhimmi ya cika makil, saboda sanarwar Alhaji baba na cewar duk wanda yake nan kusa har yan kaduna yana bukatar ganinsu cikin gaggawa,wadanda sukai nisa kamar na kano ko wata kasa haka akayi connecting dan suma su sami damar jin abinda ya hada taron.
Kowa ya nutsu yana sauraron bayanin Alhaji baba ta macrophon,kowa ya gamsu da abinda yasanar dasu har wasu suna cewa ai da ko awaya yasar musu ma ya wadatar.
Alhaji baba yayi gyaran murya kana yace"dalilina na cewa lallai sai kowa yazo shine inaso ku dauki abun da muhimmanci kuma kowa yasan cewa abdallah shima jika naneeee
(Waiyo ni fadima sauri nayi na zubawa mutanen dake dankare a holl din Ido ko zan samu nasarar riga su abdallah gano bara gurbin cikin zuriar Alhaji balarabe sai dai kash babu wanda ya nuna wani abu afuskarsa da zai sa na diga masa ayar tambaya,kai wadannan mutane ko suwaye akwai shu'umai)
Abdallah ya zubawa fuskoki da yawa ido ko shima zai fahimci wani sauyi daga wata fuska saboda jin furucin Alhaji baba, sai dai shi din ma babu abinda ya fuskanta.
Ahlin Alhaji balarabe sun karbi abdallah da hannu bibiyu, anan ya dinga ganin wata kauna akan fuskokinsu kansa ya daure matuka dan yakasa fuskantar gaskiyar kauna da akasinta, duk abu daya yake gani dauke a fuskokinsu, dady ane, ma da dady jafar yasan bai gamsu da zuwan abdallah ba, bai fahimci komai afuskarsa ba.
Ahaka taron ya watse kowa na kokarin ganin ya nunawa abdallah shi mai kaunarsa ne baka da zuci, Alhaji baba da kansa ya rakashi har bangaren inno ya sadashi da hadadden dakinsa kana yace" yayi wanka ga abinci nan ya dade da rigashi zuwa sannan ya kwanta ya huta.
Godiya abdallah yayi wa Alhaji baba,shi kuma ya juya ya fita yana mai tunasar dashi karya sake yi mai godiya. wadawa yayi bisa lumtsumeman gadon da yasamu wata iriyar shimfida ta alfarma da wani hadadden bedsheet,kansane yaji yana neman barewa gida biyu saboda yawan hayaniyar da yashaka yau shi tunda yake bai taba shiga hayaniya irin wannan ba dole dady yay ta bashi hakuri da tausarsa akan ya jure ashe yasan komai akan yawan hayaniyar gidan anya kuwa zai jura?
Tashi yay yana layi ya nufi bayi jikinsa duk babu kwari hutu kawai yake bukata yanzu dan wannan hayaniyar tasa duk san aikinsa yaji ba zai iya fita aiki gobe ba.
Tunda aka sauke ta atashar bulayi kawai take acikinta batasan ko Ina ba batasan kowa ba, batasan inda zata nufa ba, can kusa da wata mai abinci ta samu ta rabe sai baza manyan idanunta take taga ta inda Allah zai kawo mai agazamata, da dai taga zaman take ga yunwa na nukurkusarta kawai sai taciro naira dari biyu ta kara matsawa kusa da mai abincin tare da yi mata sallama!' alokaci daya kuma tana mika mata gudar dari biyu tace"abani abinci!matar mai abinci ta bi bintu da wani irin kallon yau naga India mai jin hausa,girgiza kanta matar tayi tana mai cewa' yi hakuri 'yan mata bamu da irin abincin ku anan sai dai kije restaurant' a canne suke yin kowane irin abinci!'ta karasa maganar da juyawa tana kallon mutanen da suka taru arumfar abincin nata, kallon bintu suke cike da farinciki yayin da wasu suke musun cewa ai amisha ce wasu kuwa suce ai pretty ce,
Bintu ta rasa inda zatasa kanta kawai sai tafashe da kuka!' saboda ita bata saba shiga cikin jama'a ba, balle wadannan da suke tai mata surutu aka, ganin haka yasa wani babban dan union ya sa wasu samari suka kori mutanen,
Matar nan mai abinci ta dubi bintu tace" yan mata Ina zakijene na ga kamar kin dade acikin tashar nan ko kin manta hanyane?da sauri bintu ta daga kanta!' matar tace"ayya to bari nasa yarinyata ta nuna miki hanya,juyawa tayi ta kalli budurwar dake tsaye agefanta tana saurarensu, tace" basira maza jeki ki nuna mata hanya ki saka ta a keke napep, ta fada masa sunan anguwar da zai kaita dan naga alama bakuwace batasan ko'inaba!'ta mikawa basira wata leda tana cewa" ga wannan sai ki bata idan zata iya cin abincin mu!'bintu cikin shagwababbiyar muryarta da ta riga ta sangarce agun baffa da fafi tace"na gode mama Allah ya saka miki da alkhari!' mai abinci cikin jin dadi tace"babu damuwa ki gaida gida Allah ya kiyaye!'ta amsa da amin tare da jin dadin karamcin da mama mai abinci tayi mata.
Tun kan ma su fita daga cikin tashar suka samu mai napep,basira ta dubi bintu tace" wace anguwa za'akaiki? bintu shiru tayi tana son ta tuna sunan anguwar da fafi ya gaya mata amma ikon Allah shaf ta manta,mai keke yace"Ina gafa wannan hausarce tayi mata nauyi bari na lissafo mata sunan anguwanni ko zataji ta fada!'kafun ma basira ta tanka masa ya shiga lissafo manyan anguwannin masu kudi da fada aji, bintu tanajinsa har yanzu bai fadi makamanciyar sunan anguwar da zataje ba .gajiyar da tayine yasa yana cewa'mai tama sule tace"muje nan zani!'me napep yace au wai dama kinajin hausa kan uba alkur an ban zaci ta'iya hausaba kudurar Allah kenan!'basira tace da Allah mazarkwaila sarkin zaki wuce kuje ka kaita ka'ishi mutane da surutu kamar ba gobe!'dariya yayi kawai dan yasan gaskiya ta fada, mikawa bintu ledar take away tayi gami dayiwa junansu sallama,mai napep yaja suka wuce.
Hajiya anzo mai tama a'ina zaki sauka?ahankali bintu take bin anguwar da kallo,tare da manya-nanyan gidajen da sukayi mata kawanya,tunani take idan ta sauka to Ina zata nufa?wa tasani acikin wannan haddadiyar anguwa ?amma abin da tasanine dole ta sauka tunda itane ta zabi akawota nan din, dan haka tace da mai napep ya sauketa,burki yaja akofar wani haddaden gida yana mai cewa" hajiya kudinki naira dari uku!' batare da tace"komai ba ta mika masa dari biyun dazu da mai abinci bata karba ba,yana amsa ya figi napep dinsa ya kara gaba.