Sashe 13
Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Tsuru tayi agefan gidan da ya ajiyeta tare da zabga uban tagumi,ji tayi cikinta yana wani kuuu sai alokacin ta tuna da yunwar dake dankare acikinta, gabas ta kalla kudu da arewa bata ga kowa ba dan haka a nutse ta juya baya taci abincinta, duk da bata wani ci mai yawaba cikinta ya riga ya cushe.zama ta cigaba dayi awajen ga tsoro da ya cika ta, fanfo ta hango daga dan nesa da ita da sauri ta karasa gun ta bude fanfon aiko ruwa ya zubo shaaa, cikin azama ta kafa kai tasha tayi nak, kana ta daura alwala ta dawo inda take, ta shimfida dan kwalin kanta tayi sallolin da ake binta kana ta dora da na filfilu, tana nan dai azaune har aka kira sallar magriba sai alokacin ta fara ganin mutane suna fitowa masallaci, wasu kuma sun dawo daga aiki, sai kuma taji hankalinta ya dan kwanta da taga jama'a musulmai suna hada-hadar shiga masallaci.
Sai da akayi sallar isha dayawan jama'a suka dinga fitowa daga masallacin,motace ta dallareta yayin da aka bude wawakekiyar kofar get din gidan da take rabe ajikinsa, cikin sauri ta mike saboda yadda idanunta suka mutu saboda hasken fitilar,
Bayan motar ta shige ne aka maida kofar aka rufe, sai kuma tsoro ya kamata, bintu sarkin kuka, take ta fara sana ar tata,sake bude kofar taga anyi da sauri ta zabura ganin wata girkakkiyar mata ta fito daga cikin gidan kai tsaye ta nufeta,bintu na ganin haka ta karawa kukanta sauti dan kuwa bintu matsoraciyace ta sosai, matar na zuwa ta jawo hannun bintu suka shiga cikin gidan, d'an da katawa matar tayi kana ta dubi bintu fuskarta babu yabo ba fallasa tace" kimin shiru ba wani abu zan miki ba mai gadine yasanar dani ya ganki ta CCTV tun dazu kina zaune banyi ma niyar kula kiba saida mai gidana ya dawo ya kuma yi min maganarki yace inzo na shigo dakeee...
Tofa yanzu aka fara wasan
Wai hannun wa bintu ta fadane? Shin zata samu nasarar shiga estate?idan ta shiga wace irin rayuwa take agidan ?a wane matsayin zata shiga?
Shin ya rayuwar abdallah zata kasance acikin ahlinsa? Anya kuwa abdallah zai iya zama cikin hayaniyar ahlinsa ko zai fece? Da gaske zai iya zabar abokiyar rayuwa acikin jikokin Alhaji baba? Wai kuwa Ina labarin dije?meye shirinsu Alhaji hashir ne da suke neman inda aka boye Alhaji abubakar? Ina hajiya zulaiha ta shige shin itama Bata gane gudan jinintaba abdallah?meye hakikanin zuciyar alhaji mansur ?akwai tambayoyin da bamuzo gabar yinsuba, ku biyoni Dan jin tarin amsoahinku.......
Comment.......
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ¼*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
Wannan page din kacokan na sa daukar dashi ga yan fans din KUDURAR ALLAH ina matukar godiya gareku Allah ya bar kauna love u lodi-lodi..,..
```Page 11 ```
Tunda ya kwanta bashi ya farka ba sai da yaji kiran sallar asuba acikin kunnensa, ahankali ya bude manyan idanunsa dasuka koma wata kala mai matukar kyau da burgewa saboda baccin da bai isheshi ba, cikin yar kasala ya mike daga kan lallausan gadon nasa ya nufi hanyar toilet dan dauro alwala, yana fitowa yaji ana taba nock din dakin, ahankali ya karasa jikin kofar yana mamakin kowaye acikin wannan lokaci, ga tsananin mamakinsa Alhaji baba ya gani tsaye yana doka masa nutsatstsan murmushi wanda yake gauraye da wata irin mashahuriyar kauna,cikin tsananin kulawa yace" abdallah jikana fito mutafi masallaci ba nisa bane acikin estate dinnan yake dannasan haryanzu akwai gajiya atare dakai!'jinjina kai kawai abdallah yayi tare da kama hannun Alhaji baba yana cewa na fito, ai da kasani baka zo har nan ka wahalal da kanka ba sai mu hadu amasallacin!'Alhaji baba ya gyada kansa ayayin da suke jerawa yace" abdallah daka yanzu duk sanda kaga banzo na ta da kai mun tafi sallar asuba ba to ka kaddara aranka ba lafiya ba, dan tun daga yau na wajibtawa kaina, sai dai kuma idan baka nan ko na mutu ko kuma kayi aure kayi nesa dani!'adai-dai lokacin sukazo kofar masallacin dan haka zancen nasu ya yanke.
Ko da aka idar da sallah sun jima aciki suna karatun alkur'ani Alhaji baba ba karamin dadi yajiba da yasamu abdallah yadda yake tsammata, wato mai tsananin ilmin addini da kuma aiki dashi,saida gari ya danyi haske kana suka fito Alhaji baba har kofar dakinshi ya kuma rakashi kana ya dubeshi cike da kauna, yace"abdallah kaje ka kwanta za'akawo maka kayan karinka idan katashi nasan yanzu kana bukatar hutu!' ahankali abdallah yace"na gode!' alhaji baba bai saurareshi ba ya wuce dan komawa bangarensa.
Lumshe manyan idanunsa yayi wanda suke cike da zara-zaran eyelashes,yana mai jin kansa awata duniya ta daban, gashi dai acikin yan uwansa kuma mahaifarsa amma bayajin farinciki da walwala atare dashi, abu daya yaji tun shigowarshi gidan shine kauna da tausayin Alhaji baba sai kewa ta mahaifansa da ta lulllubeshi,yana jin kewar mahaifiyarshi saidai bazai iya haduwa da ita ba ahalin yanzu domin bazai iya jurar ganinta batare da ya nuna tsananin kewarta da dokinta agareshi ba,ko ita ma ta mantashi?ko tana tunanin sa ahalin yanzu?kwanciya yayi asaman gadonsa yana mai shafo tattausar sumar kansa da tai matukar kayatuwa wadda tai dai-dai da dan siririn sajen da ya kawata fuskarsa ma'abociyar kwarjini da haiba, rufe idanunsa yay yana mai kokarin gayyato bacci ko yasamu kansa ya daina masa ciwo.
Kaiwa take tana komowa kamar mai safa da marwa, can dai kuma ta zauna,tana mai cije bakinta ta rasa ma wani irin tunani zatayi karfa garin sanyin jiki tabari abubuwa su cakude mata, kai Ina ai haka ma baza ta taba faruwa ba,duk yakin da nakeyi shekara da shekaru amma ace lokaci daya wasu banzaye suzo sucini da yaki ina bazan taba barin haka ta faruba, sai na ga abinda ya turewa buzu nadi!' takarasa fada tana fitar da wani irin zazzafan huci.
Majalisar da take kasancewa afalon inno ce yau take ta tafka mahawara kowa da a bokin yinsa kasancewar bikin da yake ta da da matsowa dan yau sauran kwana goma afara shagalin bikin,shiyasa idan suka zauna basu da wani zance idan ba na yadda bikin zai kasance ba, amare hudu angwaye hudu sai dai dake da akwai zumunci tsakanin iyayen amaren da angwayen yasa komai za ayishi ahade dan haka suke cewa' bikin mutum takwas za'ayi 'acikin estate din na Alhaji balarabe,
Khadija da haulat yayan nana karama wadda suke kira da hajiya mama sai kuma yarinyar aunty hafsa, ita kuma suna mata lakani da maman maiduguri, ita kuma zata aurar da rukayya babbar yarta, yayan maman maiduguri gaba daya su hudun suna nan cikin estate kamar yadda duk dan da aka haifa ba daga cikin estate ba to sai yay kaura ya dawo cikin yan uwansa, shiyasa yaran gidan gaba daya suka taso awaje guda, sai Abdurrahim d'aga hajiya zulaiha yayan rahima, suna matukar ji da bikin nan kasancewar sun kwana biyu ba'ayi biki a estate din ba.
Hayaniya suke sosai sun cika falon da shegen musu, mazansu da mata kowa so yake asaurari zancensa dan haka hayaniyar tayi yawa har hawa kai takeyi, hatta inno da bata cika damuwa da harkokin hayaniyar suba yau sai da taji sun dameta,
Ahankali yake bude shanyayyun idanunsa da har yanzu suke cike taf da bacci dan ko karyawa har yanzu baiyi ba tun da suka dawo daga masallaci da Alhaji baba wani bacci mai cike da mafarkai kala-kala yay awan gaba dashi, shine bai farka ba sai yanzu da wata iriyar gigitacciyar hayaniya mai fasa kwanyar kai ta farkar dashi, hannu yasa ya dafe saman goshinsa yana jin hayaniyar har tsakiyar kokon kansa,mikewa yayi ya nufi tailed, wanka yayi kusan minti arba'i kana ya fito yana sanye da rigar wanka sai karamin towel ahannu yana tsane kanshi,.cikin mintuna talatin yagama shirinsa tsaf cikin shigar kananun kaya wanda sukabi zubin jikinshi da kyakykyawar kirarshi ta sadaukan maza, yayi matukar kyau na ban mamaki tamkar ka daukeshi ka gudu, ya feshe jikinsa da manyan hadaddun turarukansa masu kamshi, falonsa ya fita, inda ya kara jin sautin hayaniyar tamkar afalon akeyi, runtse idanunsa yayi yana mai jin wani irin zafi aranshi tare da takaici,gashi ba gwanin magaba ballentana yace zai musu magana,Amma tunda hakane abun lallai yaran nan zasuci kaniyarsu tunda ba yadda zaiyi, zaman gurin dole ya kamashi dolene ya dauki mataki idan ba haka ba babu shakka yaran nan zasu kasheshi da wannan kadadinnasu mara tushe da ma'ana,dan bai dauki hakan ako mai ba sai tsabar rashin tarbiya.
Kadan ya tattaba kayan karin da aka kawo masa, shima tea kawai ya sha, sakamakon rashin sanin daka Ina abincin suke, tashi yayi ya nufi hanyar fita babban falon cikin takunshi mai cike da nutsuwa da wata irin ta kama, kai kace sarkine amma shi bai san duk yana wannan ba, dan haka halittarshi take,
Wani irin sassanyan kamshine ya farayiwa kofofin hancinsu sallama kana ginshirarren takunsa mai cike da nutsuwa sai kuma kwarjininshi da ilhama wanda rabbi ya bashi sai kuma kyakykyawar fuskarshi mai cike da haiba, kai bazakace ya taba sanin yadda ake murmushi ba,
Sai da akayi sallar isha dayawan jama'a suka dinga fitowa daga masallacin,motace ta dallareta yayin da aka bude wawakekiyar kofar get din gidan da take rabe ajikinsa, cikin sauri ta mike saboda yadda idanunta suka mutu saboda hasken fitilar,
Bayan motar ta shige ne aka maida kofar aka rufe, sai kuma tsoro ya kamata, bintu sarkin kuka, take ta fara sana ar tata,sake bude kofar taga anyi da sauri ta zabura ganin wata girkakkiyar mata ta fito daga cikin gidan kai tsaye ta nufeta,bintu na ganin haka ta karawa kukanta sauti dan kuwa bintu matsoraciyace ta sosai, matar na zuwa ta jawo hannun bintu suka shiga cikin gidan, d'an da katawa matar tayi kana ta dubi bintu fuskarta babu yabo ba fallasa tace" kimin shiru ba wani abu zan miki ba mai gadine yasanar dani ya ganki ta CCTV tun dazu kina zaune banyi ma niyar kula kiba saida mai gidana ya dawo ya kuma yi min maganarki yace inzo na shigo dakeee...
Tofa yanzu aka fara wasan
Wai hannun wa bintu ta fadane? Shin zata samu nasarar shiga estate?idan ta shiga wace irin rayuwa take agidan ?a wane matsayin zata shiga?
Shin ya rayuwar abdallah zata kasance acikin ahlinsa? Anya kuwa abdallah zai iya zama cikin hayaniyar ahlinsa ko zai fece? Da gaske zai iya zabar abokiyar rayuwa acikin jikokin Alhaji baba? Wai kuwa Ina labarin dije?meye shirinsu Alhaji hashir ne da suke neman inda aka boye Alhaji abubakar? Ina hajiya zulaiha ta shige shin itama Bata gane gudan jinintaba abdallah?meye hakikanin zuciyar alhaji mansur ?akwai tambayoyin da bamuzo gabar yinsuba, ku biyoni Dan jin tarin amsoahinku.......
Comment.......
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ¼*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
Wannan page din kacokan na sa daukar dashi ga yan fans din KUDURAR ALLAH ina matukar godiya gareku Allah ya bar kauna love u lodi-lodi..,..
```Page 11 ```
Tunda ya kwanta bashi ya farka ba sai da yaji kiran sallar asuba acikin kunnensa, ahankali ya bude manyan idanunsa dasuka koma wata kala mai matukar kyau da burgewa saboda baccin da bai isheshi ba, cikin yar kasala ya mike daga kan lallausan gadon nasa ya nufi hanyar toilet dan dauro alwala, yana fitowa yaji ana taba nock din dakin, ahankali ya karasa jikin kofar yana mamakin kowaye acikin wannan lokaci, ga tsananin mamakinsa Alhaji baba ya gani tsaye yana doka masa nutsatstsan murmushi wanda yake gauraye da wata irin mashahuriyar kauna,cikin tsananin kulawa yace" abdallah jikana fito mutafi masallaci ba nisa bane acikin estate dinnan yake dannasan haryanzu akwai gajiya atare dakai!'jinjina kai kawai abdallah yayi tare da kama hannun Alhaji baba yana cewa na fito, ai da kasani baka zo har nan ka wahalal da kanka ba sai mu hadu amasallacin!'Alhaji baba ya gyada kansa ayayin da suke jerawa yace" abdallah daka yanzu duk sanda kaga banzo na ta da kai mun tafi sallar asuba ba to ka kaddara aranka ba lafiya ba, dan tun daga yau na wajibtawa kaina, sai dai kuma idan baka nan ko na mutu ko kuma kayi aure kayi nesa dani!'adai-dai lokacin sukazo kofar masallacin dan haka zancen nasu ya yanke.
Ko da aka idar da sallah sun jima aciki suna karatun alkur'ani Alhaji baba ba karamin dadi yajiba da yasamu abdallah yadda yake tsammata, wato mai tsananin ilmin addini da kuma aiki dashi,saida gari ya danyi haske kana suka fito Alhaji baba har kofar dakinshi ya kuma rakashi kana ya dubeshi cike da kauna, yace"abdallah kaje ka kwanta za'akawo maka kayan karinka idan katashi nasan yanzu kana bukatar hutu!' ahankali abdallah yace"na gode!' alhaji baba bai saurareshi ba ya wuce dan komawa bangarensa.
Lumshe manyan idanunsa yayi wanda suke cike da zara-zaran eyelashes,yana mai jin kansa awata duniya ta daban, gashi dai acikin yan uwansa kuma mahaifarsa amma bayajin farinciki da walwala atare dashi, abu daya yaji tun shigowarshi gidan shine kauna da tausayin Alhaji baba sai kewa ta mahaifansa da ta lulllubeshi,yana jin kewar mahaifiyarshi saidai bazai iya haduwa da ita ba ahalin yanzu domin bazai iya jurar ganinta batare da ya nuna tsananin kewarta da dokinta agareshi ba,ko ita ma ta mantashi?ko tana tunanin sa ahalin yanzu?kwanciya yayi asaman gadonsa yana mai shafo tattausar sumar kansa da tai matukar kayatuwa wadda tai dai-dai da dan siririn sajen da ya kawata fuskarsa ma'abociyar kwarjini da haiba, rufe idanunsa yay yana mai kokarin gayyato bacci ko yasamu kansa ya daina masa ciwo.
Kaiwa take tana komowa kamar mai safa da marwa, can dai kuma ta zauna,tana mai cije bakinta ta rasa ma wani irin tunani zatayi karfa garin sanyin jiki tabari abubuwa su cakude mata, kai Ina ai haka ma baza ta taba faruwa ba,duk yakin da nakeyi shekara da shekaru amma ace lokaci daya wasu banzaye suzo sucini da yaki ina bazan taba barin haka ta faruba, sai na ga abinda ya turewa buzu nadi!' takarasa fada tana fitar da wani irin zazzafan huci.
Majalisar da take kasancewa afalon inno ce yau take ta tafka mahawara kowa da a bokin yinsa kasancewar bikin da yake ta da da matsowa dan yau sauran kwana goma afara shagalin bikin,shiyasa idan suka zauna basu da wani zance idan ba na yadda bikin zai kasance ba, amare hudu angwaye hudu sai dai dake da akwai zumunci tsakanin iyayen amaren da angwayen yasa komai za ayishi ahade dan haka suke cewa' bikin mutum takwas za'ayi 'acikin estate din na Alhaji balarabe,
Khadija da haulat yayan nana karama wadda suke kira da hajiya mama sai kuma yarinyar aunty hafsa, ita kuma suna mata lakani da maman maiduguri, ita kuma zata aurar da rukayya babbar yarta, yayan maman maiduguri gaba daya su hudun suna nan cikin estate kamar yadda duk dan da aka haifa ba daga cikin estate ba to sai yay kaura ya dawo cikin yan uwansa, shiyasa yaran gidan gaba daya suka taso awaje guda, sai Abdurrahim d'aga hajiya zulaiha yayan rahima, suna matukar ji da bikin nan kasancewar sun kwana biyu ba'ayi biki a estate din ba.
Hayaniya suke sosai sun cika falon da shegen musu, mazansu da mata kowa so yake asaurari zancensa dan haka hayaniyar tayi yawa har hawa kai takeyi, hatta inno da bata cika damuwa da harkokin hayaniyar suba yau sai da taji sun dameta,
Ahankali yake bude shanyayyun idanunsa da har yanzu suke cike taf da bacci dan ko karyawa har yanzu baiyi ba tun da suka dawo daga masallaci da Alhaji baba wani bacci mai cike da mafarkai kala-kala yay awan gaba dashi, shine bai farka ba sai yanzu da wata iriyar gigitacciyar hayaniya mai fasa kwanyar kai ta farkar dashi, hannu yasa ya dafe saman goshinsa yana jin hayaniyar har tsakiyar kokon kansa,mikewa yayi ya nufi tailed, wanka yayi kusan minti arba'i kana ya fito yana sanye da rigar wanka sai karamin towel ahannu yana tsane kanshi,.cikin mintuna talatin yagama shirinsa tsaf cikin shigar kananun kaya wanda sukabi zubin jikinshi da kyakykyawar kirarshi ta sadaukan maza, yayi matukar kyau na ban mamaki tamkar ka daukeshi ka gudu, ya feshe jikinsa da manyan hadaddun turarukansa masu kamshi, falonsa ya fita, inda ya kara jin sautin hayaniyar tamkar afalon akeyi, runtse idanunsa yayi yana mai jin wani irin zafi aranshi tare da takaici,gashi ba gwanin magaba ballentana yace zai musu magana,Amma tunda hakane abun lallai yaran nan zasuci kaniyarsu tunda ba yadda zaiyi, zaman gurin dole ya kamashi dolene ya dauki mataki idan ba haka ba babu shakka yaran nan zasu kasheshi da wannan kadadinnasu mara tushe da ma'ana,dan bai dauki hakan ako mai ba sai tsabar rashin tarbiya.
Kadan ya tattaba kayan karin da aka kawo masa, shima tea kawai ya sha, sakamakon rashin sanin daka Ina abincin suke, tashi yayi ya nufi hanyar fita babban falon cikin takunshi mai cike da nutsuwa da wata irin ta kama, kai kace sarkine amma shi bai san duk yana wannan ba, dan haka halittarshi take,
Wani irin sassanyan kamshine ya farayiwa kofofin hancinsu sallama kana ginshirarren takunsa mai cike da nutsuwa sai kuma kwarjininshi da ilhama wanda rabbi ya bashi sai kuma kyakykyawar fuskarshi mai cike da haiba, kai bazakace ya taba sanin yadda ake murmushi ba,