Sashe 19
Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Aɓangaren su Hajiya ladidi kuwa, yau Anty nafisa tayi sammakon zuwa gidan nasu,A yayin da suka ƙule A ɗaki suna ƙulla tsiyarsu, Anty nafisa tace"yanzu Hajiya taya zamu dinga isar da saƙonmu wajen wannan banzar yarinyar? kinga idan nace zan dinga kiranta muna keɓewa A kwai babbar matsala, kinsan gidan namu makiran suna da yawa, kuma baka ganesu kowa munafuncinsa yana cikinsa!'Hajiya ladidi tace" mafita ɗaya ce shine mubata waya!'to amma tayaya zamuyi hakan shima A kwai haɗari!'duk shiru sukayi suna tunanin mafita, can Anty nafisa tace yauwa na samo hanya!' Hajiya ladidi ta zuba mata ido tare da yi mata nuni da cewar tana sauraren ta,Anty nafisa tace" me zai hana nayiwa inno dabara na nuna mata ya kamata A bawa Zahra waya saboda ko wani uzurin zai taso na buƙatarta a kusa yayin da bata kusa!'tana direwa Hajiya ladidi tayi mata wani kallon bakya cikin haiyacinki,kana tace"nafisa A she baki da wayo so kike inno tayi wani tunani A kan haka?wannan ai ba dabara bace sam ki canza tunani!'Anty nafisa tace to Hajiya meye mafita?kinsan dai bazai yiwu mu bata waya A ɓoye ba,dan inno zata iya ganowa kuma kinsan bagidajiyar nan tsaf zata gayawa inno wanda ya bata!Hajiya ladidi taja iska ta furzar kana tace"mu bar wannan zancen nasan yadda zanyi!Anty nafisa tace dan Allah kigayamin me zakiyi kinji Hajiyata? Hajiya ladidi tace" Alhaji zan gayawa ya kamata ya kira Alhaji Baba yaji ya Zahra take, daga nan zai dinga kira akai akai danjin lafiyar yariyar, kinsan daga ƙarshe me zai faru? Anty nafisa ta girgiza kai, taci gaba da cewa daga nan zansa Alhaji ya siyo ƙaramar waya, zan sashi yaje gidan da kansa dan kaiwa Zahra wayar, wannan shirinane kuma zai tafi daidai da tsarina cikin sauƙi batare da zargin kowa A kanmu ba!wata shegiyar dariya Anty nafisa ta saki, tare da cewa, gaskiya Hajiyata kina da basira, wannan shirin yayi bari nayi sauri na koma dan gabatar da shirin mu na farko.
Dije inaso ki kasance cikin shiri dan muna gab da kutsawa cikin lamarin!'daga haka ta kashe wayar tare da jan motar ta bar gurin cikin shigar ta ta kullum.
A daidai wan nan lokacin, shi kuma Abokin aikin Hajiya ladidi bayan sun gama waya da'ita, ya sheƙe da wata mahaukaciyar dariya, yana mai cewa ladidi kin gama yawo tunda kika haɗa kai dani bayan Ni ɗin ma bani bane kin tabka babban kuskure kin kai kanki ga halaka, dan nasan yana gama samun Abinda yake so daga gareki sunanki sorry, Ni dai ana biyana zan canza sheƙa dama mu haka aikinmu ya gada, Hajiya ladidi kina ruwa, yayin da yakuma.sheƙewa da wata muguwar dariya, tabbas kinyi kuskure haɗa hanya da ƴan ƙungiyar jack masiface babba.
A hankali take ta kawa cikin sanɗa da kiyaye wa dan kar wani ya ganta,kuka mara sauti ta farayi yayin da taga hanyar ta ɓace mata, guduwa take sanyi dan tunda tayi mafarki da fafinta yana ƙara jaddada mata abinda ta manta wato sunan kakanta yana kuma sanar da'ita ba bacci ya kamata tayi ba, domin gaba ɗayan ta A ɗaure take A tsakanin makiya, haka kuma babban yaki ne A gabanta wanda ya tun karota da zafinsa.
Wannan shine dalilin da yasa take neman hanyar tserewa, domin zuwa ta fuskanci manyan ƙaddarorinta, sai kuma gashi kanta ya juye ta rasa hanyar tserewa.
Tana cikin wannan zagaye ne tazo ta wajen wani ɗaki, sai lokacin kuma shegen tsoronta ya dawo, dan lokacin wajen misalin ɗaya da rabi na dare ne,juyawa tayi da niyar komawa,sai dai me wani irin jijjiga taji gaba ɗaya gurin nayi da sauri ta juya dan ganin meyake faruwa, dan saboda tsananin tsoro ji tayi ta kasa guduwa,wani irin razanannen ihu ta saki wanda A tunanin ta cikin mintuna zataga an kewaye ta, sai dai ga mamakinta ko kare baiyi haushi ba, zuciyar ta ce ta shiga wani irin bugu da sauri da sauri yayin da tayi arba da ɗakin nan yana wani irin juyi tare da fitar da wani irin hayaƙi, cikin kiɗimewa ta tattara dukkanin ƙarfinta ta sheƙa da wani irin A zababben gudu na fitar hankali wanda kawai tsintar kanta tayi A cikin ɗakinta......
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ¼*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
```Page 15 ```
Tamkar A mafarki haka yake ganin Al'amarin,ihun da Bintun take har cikin tsakiyar kansa, juyi kawai yake tsakiyar tattausan gadon,bakinsa ɗauke da addu'o'i, lokaci ɗaya kuma komai ya tsaya cak tamkar ɗauke war nefa, A hankali ya tashi zaune hannun sa dafe da kansa, wannan Al'amari bakaramin hautsina masa tunani yayi ba, to me hakan yake nufi?me ya kawo wannan yarinyar cikin mafarkinsa?meye haɗin ta da wannan ɗakin? meye kuma A cikin ɗakin?Anya kuwa ba abinda yake zargi A kan yarinyar bane Allah ya nuna masa? tabbas hakan yana nuna masa turo ta A kayi, to amma waye ya turota? me aka turota ta aikata masa? komawa yayi da baya ya jingina da fuskar gadon tare da tattaro bedsheet ɗin ya ciku kuyeshi ya watsa shi ƙasa, miƙewa yayi ya fara zagaye ɗakin yana furzar da wani irin zazzafan huci daga bakinsa, idanunsa har sun sauya kala saboda tsananin zafin zuciya, lailai dolene ya binciki yarinyar nan,A sannu zai kamata da lefi dumu-dumu, bathroom ya faɗa ya ɗauro Alwala ya kama jera na filfilu.
Tunawa da Abinda ta gani yasa ta kuma rikicewa jikinta ya shiga wata iriyar kakkarwa, cikin ƙanƙanin lokaci zazzaɓi ya rufeta, A matuƙar tsora ce take da gidan nan, wannan wane irin gidane suka kawoni? ta faɗa cikin kakkarwar jiki da tashin hankalin da yaƙi barinta, raɓewa tayi can ƙarshen ɗakin tanajin kamar A lokacin abun yake faruwa, runtse idanun ta tayi, cikin tashin hankali tace"wayyo Allah katemakeni ka kuɓutar dani daga hannun waɗan nan mutane, ya Allah katemakeni ka tsareni daga shiga haɗarin gidan nan, ka kawo min mafita cikin gaggawa!'kuka tasaki me matuƙar bantausai da karya zuciyar mai imani,A hankali cikin jin tsoro da ɗar-ɗar take takawa har zuwa cikin bathroom,Alwala tayi ta fito ta shinfiɗa sallaya ta tada kabbara domin miƙa Al'Amuranta gurin sarki Allah buwayi gagara misali.
Garau ta tashi washe gari tayi aikinta kamar yadda ta saba, ta haɗa karinsa ta nufi falonsa da tunanin ya fita motsa jiki kamar yadda ta saba zuwa ta tarar ya tafi, shi yasa basu fiya haɗuwa ba,tana shiga falon ta ɗan yi jim, kana kuma ta wuce ta jera kayan karin,juyowa tayi bayan ta A jiye da nufin ƙara Sachin ɗin falon dan ganin inda bai gyaruba ta kuma kimtsawa, saboda tun kan ya farka take shigowa ta gyara falon idan ya fita motsa jiki kuma sai ta gyara ɗakin da wankin toilet, dafe ƙirjinta tayi tare da saurin ja da baya ganin mutum kwance yayi luf cikin kushin, A kimtse yake cikin kayan motsa jiki damtsensa sai glowing yake idanunsa A rufe tamkar mai bacci, murguɗa ɗan ƙaramin bakinta tayi tare da motsashi A hankali tace"haka kawai sai mutum ya dinga bani tsoro kuma bani da damar yin ihu ko kuka sai A fizgeni a wulla waje,mutum sai kace kurma ba abinda ya iya sai ɗacin rai!
A hankali ya shiga buÉ—e lumsassun idanunsa masu dawo da mutum cikin nutsuwar sa, ya É—ora su Akan kyakkyawar fuskar Bintu,tsaf yaji duk abinda tace, saboda shi Abdullah ya kasance daga cikin mutane masu tsananin ji, dan haka bai sha wahalar jin duk abinda take faÉ—a ba.
Cikin rikecewar da kaifafan idanunsa masu tsananin maiƙo da sheƙi suka sakata,cikin yanayin fargaba da matsanancin tsoro da ya saukar mata A lokaci ɗaya, cikin sanɗa ta taka dan tsira daga waɗan nan shu'uman idanuwan nasa da suke neman kassara duk wata gaɓar da ke gudanar da jini A cikin jikinta,
Wata tsadaddiyar murya taji tamkar amsa sarewa acikin kunnuwanta,wadda ta saka gaba ɗaya ragowar kuzarin dake tare da ita ya ƙarasa malalewa,cak ta tsaya A inda take batare da ta ƙara wani ƙwaƙwƙwaran motsi ba, cikin yanayin maganarsa na fitar da magana ɗai ɗaya tamkar wanda akasashi yi dole,yace"karki sake ganina ki tsorata,numfashinta bai gama dai dai tuwa ba ya kuma rigirgizo mata tambayar da ta motsa ƴan hanjin cikinta, tare da wata iriyar juyowa sosai tana fuskantar sa, yayin da idanuwan nan suka kuma fitowa cikin firgici da tsoro,sai da ya gama karantar yanayin ta tsaf kana ya kuma mai maita mata tambayar,yace" dake nake jiya misalin ƙarfe biyu me ya fita dake waje har kina neman fasawa mutane kunnuwa da shegen ƙaranki,me kikeso kishiga kiyi A wannan ɗakin? hantar cikinta ya kuma kaɗawa, to ma wai miyene na jin tsoron bayan nasan ban yi komai ba,wata ƙila ma shine yake wani mugun abun A cikin ɗakin, idan ba haka ba me yasa da yaji ihun nawa baizo ya tai makeni ba?kuma ya akai yasan na fita? kai wannan mutumin A kwai baƙin mugu!' gigitacciyar tsawar da ya buga mata ne yasa ta dawo haiyacinta,ya nunata da yatsa yana cewa duk ranar da na tabbatar da rashin gaskiyar ki to ki tabbatar da cewa sai nayi gutsi-gutsi da namanki A cikin gidan nan,wuce ki fitamin A falo!tun kan ma ya gama rufe bakinsa ta arta da wani shegen gudu,bata tsaya A ko'ina ba sai tsakiyar gadonta tana maida numfashi me cike da razanar da tayi da Abdallah, Allah kafitar dani daga cikin wannan gida na mutane marasa tsoron ka, kowa munafiki ne A wannan gidan, duk basu da gaskiya, duba Irin kallon da wannan Ammin Rahiman takeyi min dagani itama so take tasani wani mugun aikin!'
Dije inaso ki kasance cikin shiri dan muna gab da kutsawa cikin lamarin!'daga haka ta kashe wayar tare da jan motar ta bar gurin cikin shigar ta ta kullum.
A daidai wan nan lokacin, shi kuma Abokin aikin Hajiya ladidi bayan sun gama waya da'ita, ya sheƙe da wata mahaukaciyar dariya, yana mai cewa ladidi kin gama yawo tunda kika haɗa kai dani bayan Ni ɗin ma bani bane kin tabka babban kuskure kin kai kanki ga halaka, dan nasan yana gama samun Abinda yake so daga gareki sunanki sorry, Ni dai ana biyana zan canza sheƙa dama mu haka aikinmu ya gada, Hajiya ladidi kina ruwa, yayin da yakuma.sheƙewa da wata muguwar dariya, tabbas kinyi kuskure haɗa hanya da ƴan ƙungiyar jack masiface babba.
A hankali take ta kawa cikin sanɗa da kiyaye wa dan kar wani ya ganta,kuka mara sauti ta farayi yayin da taga hanyar ta ɓace mata, guduwa take sanyi dan tunda tayi mafarki da fafinta yana ƙara jaddada mata abinda ta manta wato sunan kakanta yana kuma sanar da'ita ba bacci ya kamata tayi ba, domin gaba ɗayan ta A ɗaure take A tsakanin makiya, haka kuma babban yaki ne A gabanta wanda ya tun karota da zafinsa.
Wannan shine dalilin da yasa take neman hanyar tserewa, domin zuwa ta fuskanci manyan ƙaddarorinta, sai kuma gashi kanta ya juye ta rasa hanyar tserewa.
Tana cikin wannan zagaye ne tazo ta wajen wani ɗaki, sai lokacin kuma shegen tsoronta ya dawo, dan lokacin wajen misalin ɗaya da rabi na dare ne,juyawa tayi da niyar komawa,sai dai me wani irin jijjiga taji gaba ɗaya gurin nayi da sauri ta juya dan ganin meyake faruwa, dan saboda tsananin tsoro ji tayi ta kasa guduwa,wani irin razanannen ihu ta saki wanda A tunanin ta cikin mintuna zataga an kewaye ta, sai dai ga mamakinta ko kare baiyi haushi ba, zuciyar ta ce ta shiga wani irin bugu da sauri da sauri yayin da tayi arba da ɗakin nan yana wani irin juyi tare da fitar da wani irin hayaƙi, cikin kiɗimewa ta tattara dukkanin ƙarfinta ta sheƙa da wani irin A zababben gudu na fitar hankali wanda kawai tsintar kanta tayi A cikin ɗakinta......
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ¼*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
```Page 15 ```
Tamkar A mafarki haka yake ganin Al'amarin,ihun da Bintun take har cikin tsakiyar kansa, juyi kawai yake tsakiyar tattausan gadon,bakinsa ɗauke da addu'o'i, lokaci ɗaya kuma komai ya tsaya cak tamkar ɗauke war nefa, A hankali ya tashi zaune hannun sa dafe da kansa, wannan Al'amari bakaramin hautsina masa tunani yayi ba, to me hakan yake nufi?me ya kawo wannan yarinyar cikin mafarkinsa?meye haɗin ta da wannan ɗakin? meye kuma A cikin ɗakin?Anya kuwa ba abinda yake zargi A kan yarinyar bane Allah ya nuna masa? tabbas hakan yana nuna masa turo ta A kayi, to amma waye ya turota? me aka turota ta aikata masa? komawa yayi da baya ya jingina da fuskar gadon tare da tattaro bedsheet ɗin ya ciku kuyeshi ya watsa shi ƙasa, miƙewa yayi ya fara zagaye ɗakin yana furzar da wani irin zazzafan huci daga bakinsa, idanunsa har sun sauya kala saboda tsananin zafin zuciya, lailai dolene ya binciki yarinyar nan,A sannu zai kamata da lefi dumu-dumu, bathroom ya faɗa ya ɗauro Alwala ya kama jera na filfilu.
Tunawa da Abinda ta gani yasa ta kuma rikicewa jikinta ya shiga wata iriyar kakkarwa, cikin ƙanƙanin lokaci zazzaɓi ya rufeta, A matuƙar tsora ce take da gidan nan, wannan wane irin gidane suka kawoni? ta faɗa cikin kakkarwar jiki da tashin hankalin da yaƙi barinta, raɓewa tayi can ƙarshen ɗakin tanajin kamar A lokacin abun yake faruwa, runtse idanun ta tayi, cikin tashin hankali tace"wayyo Allah katemakeni ka kuɓutar dani daga hannun waɗan nan mutane, ya Allah katemakeni ka tsareni daga shiga haɗarin gidan nan, ka kawo min mafita cikin gaggawa!'kuka tasaki me matuƙar bantausai da karya zuciyar mai imani,A hankali cikin jin tsoro da ɗar-ɗar take takawa har zuwa cikin bathroom,Alwala tayi ta fito ta shinfiɗa sallaya ta tada kabbara domin miƙa Al'Amuranta gurin sarki Allah buwayi gagara misali.
Garau ta tashi washe gari tayi aikinta kamar yadda ta saba, ta haɗa karinsa ta nufi falonsa da tunanin ya fita motsa jiki kamar yadda ta saba zuwa ta tarar ya tafi, shi yasa basu fiya haɗuwa ba,tana shiga falon ta ɗan yi jim, kana kuma ta wuce ta jera kayan karin,juyowa tayi bayan ta A jiye da nufin ƙara Sachin ɗin falon dan ganin inda bai gyaruba ta kuma kimtsawa, saboda tun kan ya farka take shigowa ta gyara falon idan ya fita motsa jiki kuma sai ta gyara ɗakin da wankin toilet, dafe ƙirjinta tayi tare da saurin ja da baya ganin mutum kwance yayi luf cikin kushin, A kimtse yake cikin kayan motsa jiki damtsensa sai glowing yake idanunsa A rufe tamkar mai bacci, murguɗa ɗan ƙaramin bakinta tayi tare da motsashi A hankali tace"haka kawai sai mutum ya dinga bani tsoro kuma bani da damar yin ihu ko kuka sai A fizgeni a wulla waje,mutum sai kace kurma ba abinda ya iya sai ɗacin rai!
A hankali ya shiga buÉ—e lumsassun idanunsa masu dawo da mutum cikin nutsuwar sa, ya É—ora su Akan kyakkyawar fuskar Bintu,tsaf yaji duk abinda tace, saboda shi Abdullah ya kasance daga cikin mutane masu tsananin ji, dan haka bai sha wahalar jin duk abinda take faÉ—a ba.
Cikin rikecewar da kaifafan idanunsa masu tsananin maiƙo da sheƙi suka sakata,cikin yanayin fargaba da matsanancin tsoro da ya saukar mata A lokaci ɗaya, cikin sanɗa ta taka dan tsira daga waɗan nan shu'uman idanuwan nasa da suke neman kassara duk wata gaɓar da ke gudanar da jini A cikin jikinta,
Wata tsadaddiyar murya taji tamkar amsa sarewa acikin kunnuwanta,wadda ta saka gaba ɗaya ragowar kuzarin dake tare da ita ya ƙarasa malalewa,cak ta tsaya A inda take batare da ta ƙara wani ƙwaƙwƙwaran motsi ba, cikin yanayin maganarsa na fitar da magana ɗai ɗaya tamkar wanda akasashi yi dole,yace"karki sake ganina ki tsorata,numfashinta bai gama dai dai tuwa ba ya kuma rigirgizo mata tambayar da ta motsa ƴan hanjin cikinta, tare da wata iriyar juyowa sosai tana fuskantar sa, yayin da idanuwan nan suka kuma fitowa cikin firgici da tsoro,sai da ya gama karantar yanayin ta tsaf kana ya kuma mai maita mata tambayar,yace" dake nake jiya misalin ƙarfe biyu me ya fita dake waje har kina neman fasawa mutane kunnuwa da shegen ƙaranki,me kikeso kishiga kiyi A wannan ɗakin? hantar cikinta ya kuma kaɗawa, to ma wai miyene na jin tsoron bayan nasan ban yi komai ba,wata ƙila ma shine yake wani mugun abun A cikin ɗakin, idan ba haka ba me yasa da yaji ihun nawa baizo ya tai makeni ba?kuma ya akai yasan na fita? kai wannan mutumin A kwai baƙin mugu!' gigitacciyar tsawar da ya buga mata ne yasa ta dawo haiyacinta,ya nunata da yatsa yana cewa duk ranar da na tabbatar da rashin gaskiyar ki to ki tabbatar da cewa sai nayi gutsi-gutsi da namanki A cikin gidan nan,wuce ki fitamin A falo!tun kan ma ya gama rufe bakinsa ta arta da wani shegen gudu,bata tsaya A ko'ina ba sai tsakiyar gadonta tana maida numfashi me cike da razanar da tayi da Abdallah, Allah kafitar dani daga cikin wannan gida na mutane marasa tsoron ka, kowa munafiki ne A wannan gidan, duk basu da gaskiya, duba Irin kallon da wannan Ammin Rahiman takeyi min dagani itama so take tasani wani mugun aikin!'