← Book details Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 106 OF 120

Sashe 106

Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Murya yaji daga bayanshi Muryar da ba zai taɓa mantawa da itaba Muryar da ko a mafarki yajita sai ya ganeta,Muryar da yake kwana yake tashi da begen sake jinta,itace take cewa ƙarya kike yi Nafisa ba'a taɓa canja Ƙudurar Allah,kuma baza a taɓa sakewa tuwo sunaba,kin yi sake domin kuwa Bintu ta zama zakanyar dake juya akalar rayuwarki, Bintu Umar Balarabe kenan ƴar da kika so salwantar da rayuwarta,itace ta dawo gareki domin tona asirin ki na mugun nufi akan bawan Allah!'cewar fafi kenan da ya ɗora maganarsa daga inda Ammi Laila ta tsaya,tashin hankali wanda ba'a sa masa rana Hajja dai bata san sanda jikin ta ya jiƙe da fitsari ba saboda tsabar tashin hankali dan tasan zuwan Dije taron nan tare kuma da su Laila ba Alkhairi bane a gareta,wato dama Dije ce ta gudu da su Laila ke nan?daɓas haka Nafisa ta koma ta zauna yayin da zufa ke ta zubo mata tamkar wadda ake ruwan sama akanta,yayin da fafi ya rugume Bintu tare da mahaigiyarshi da matar shi ciki kewa da shaukin ganin juna,shi kuwa Abba Umar sunkuyawa yayi tare da yin sujjadar shukurr,yana ɗagowa ya tarar da Bintu tsakiyar su shi da Laila ta rasa wajen wanda zata fara nufa,sai wasu irin hawaye da take fitarwa wanda ta tabbata na tsananin farinciki ne,yau gata ga iyayenta duka biyu babu hijabi tsakaninta dasu,ba ta ankaraba taji sun lulluɓeta duka su biyun sun rungume ta atsakiyar su,baka jin komai sai koke koken dake fita ƙasa ƙasa, wasu kuma da yawa mamaki ya hanasu kataɓus wasu kuma har yanzu basu fuskanci kan lamarin ba,Alhaji Baba kuwa yana zaune yana kallon ikon Allah, sai kuma ya jiyo da kallon sa kan Abdallah tare da cewa, Abdallah me nake gani haka mai ke faruwane?ya kamata ku FAHIMTAR dani, na shiga ɗimuwa da ruɗani na kasancewar ganin Umar ɗina da ɗiya har da mata idan banyi kuskuren fahimta ba!'Abdallah yace"Alhaji Baba ka kwantar da hankalin kazaka fahimci komai dan kuwa yanzu za a warware maka zare da abawa kuma abinda ka fahimta ba kayi kuskure ba,Bintu jikarka ce ta cikin jinin ka ɗiyar ɗan ka Abba Umar!'kabbara akasa tare da tu ajjubin wannan al'amari,inno da Hajiya Babba kuwa kukan farinciki suka saka,ko wacce na san ƙarajin Bintu ajikin ta A matasayinta na cikakkiyar jikar su,shima Alhaji Baba ɗagowa yayi ya kalli iyaye da ɗiyar tasu da suke cikin wani irin shauƙi na kasancewa da junan su,yace"Umar ku zauna kayi min bayanin abinda ka lulluɓemin!'zama sukayi gaba ɗayansu sai dai Abba Umar ya kasa haɗa ido da mahaifin nasa domin yasan shi ɗin mai laifine a gareshi.

Acan gefe kuma Hajiya zulaihat ce rabe babu abinda take sai kukan tunawa dana ta iyalan kuma gudan jinin ta,tausayin Bintu da ƙaunarta take ji har cikin zuciyar ta,yayin da Abdallah yakeji kamar ya tashi yaje ya rugumeta ya lallasheta yace"yi haƙuri Ammina kema naki farincikin yana kusa dake,amma ya fisan gabatar da komai daki daki idan ba haka ba abun zai cuɗe da yawa har a rasa abinda za 'aji dashi,amma dai ai sannu bata hana zuwa,mai da idanunsa kan Bintu yayi wanda yaji ajikinshi cewa itama idanun ta na kansa,ai kuwa suna haɗa ido yaga tayi masa wani irin kallo mai haɗe da wani irin shauƙi da kewa da bege gami da jinjina,lumshe idanun yayi tare da aika mata da sakon da ya kusa shiɗar da ita, Muryar Abba Umar ce ta karaɗe falon da fara bawa mahaifinsa hakura da neman gafarar sa dana mahaifiyar sa,kana ya ɗora da basu ainahin cikakken labarin haɗuwar sa da Laila da aurensu,kamar dai yadda Fafi ya sanar da Bintu,yana rufe bakin sa,Anty Nafisa ta zunduma wani irin ihu tamkar wata zararriya, Abdallah ne yayi mata tsawar da tasaka ta nutsuwa ba tare da ta shiryawa hakan ba,kana ya ɗora mata da cewa,muna jiran jin ta bakin ki ki sanar damu yadda akayi kika sa aje a kashe Bintu da mahaifiyar ta harma da Fafi?shuru tayi tamkar wadda ake magana da kurma,daga ƙarshe ma tace"ita sam sharri za ayi mata bata san komai akan wannan batu ba,kallon Bintu yayi tare da yi mata wata alama,cikin ƙan ƙanin lokaci kuwa akaji sautin Muryar Anty Nafisa ta cikin waya tamkar alokacin take magana,tsit falon yayi masu al'ajabi nayi masu fargaba nayi dan Hajjah ƙiris ya rage ta fara zawo bayan fitarin da ta lantaya,ta riga ta saddakar da cewa yaufa babu mafita kuma ranar tonon sililice,ranar jin kunya ranar nadama wadda bata taɓa tunanin cewa zata risketa ba,haka abin yake a ɓangaren Dady Habib da sauran makiran estate.

Wani irin kuka Nafisa takeyi kukan kaico da nadama,babu abun da ya kuma haukatata da wani irin fitinan nan kuka sai labarin da taji ya ɗora musu akan yadda yayi da saban aikin da ta bayar na kashe su shida su Hajjo da Bintu,da yadda ya kuɓutar da rayuwar su dake Allah yayi da sauran rayuwar su agaba sai ya bashi dabara da tunani da nasara akan mutanen har yayi nasarar juyar da hankalin su.

Tsit falon ya yayi baka jin komai sai fitar numfashi, wasu mai daɗi wasu na fargaba wasu kuma na tunanin makoma,kamar dai Anty Nafisa da tata ta riga ta ƙare acikin ESTATE ɗin Alhaji Baba,gyaran murya Alhaji Baba yayi tare da cewa zo nan ƴata Laila nasa Miki Albarka!'a hankali Laila ta ja jikinta ta matsa kusa da Alhaji Baba Wanda ya ɗan dafa hannun sa akanta ya shiga yi mata addu'oi da fatan Alkhairi arayuwarta baki ɗaya,haka abin ya kasance a wajen Hajiya Babba da inno,sai dai Hajjo ta kasa kataɓus bare ta samu damar sawa Lailan albarka kamar yadda sauran ƴan uwanta ko tace kishiyoyin ta sukayi,itama Lailan bataji zata iya kar ɓar Albarkar bakin Hajjah ba dan haka sai ta koma mazaunin ta ba tare da ta ƙarasa gaban Hajjan ba,masu ƙarfin halin magana ne suke iya tofa albarkacin bakinsu,Alhaji Baba yayi gyaran murya tare da ɗan gyara zaman sa kana yace"Abdallah ka gama gabatar da abinda kake son GABATAR wa ko da sauran bayanai a tare da kai?jinjina kansa yayi cikin ɗan motsa bakin sa yace"Alhaji Baba a kwai abubuwa masu tarin yawa da kuma mamaki acikin wannan zaman namu ƘUDURAR ALLAH CE take kan bayyana har yanzu da sauran mu,sai dai yanzu na miƙa ragamar bayanin Hannun Baffa Hashir ko Alhaji Nasir ga kuma Alhaji Kabir duk wanda yayi magana acikin su ya wadatar tunda bakin duk ɗaya ne!'yayi shuru yana mai zubawa kyakykyawar fuskar Bintu idanu,sunkuyar da kanta tayi saboda yadda kallon nasa ke tasar mata da duk wata tsiga ta jiki da kasala,yayin da su Alhaji Nasir suka shiga share zufa wanda basu san ma ta inda take zubo musu ba,haka kuma gaba ɗaya falon su aka sawa idanu Baba Ahmad da dai sauran ahlin Baffa Hashir duk tsumayi suke suji abinda tosffin nasu su kuma suka aikata,dan kuwa ga alamun rashin gaskiya nan tsaf akan fuskokin su,shima dai Alhaji Baba ido ya sawa ɗan uwan nasa da kuma aminan sa guda biyu mafi kusanci agareshi,Dady Mansur ne yace"ku muke sauraro ku wakilta ɗaya daga cikin ku idan kuma bazaku iya fada ba muna da hanyar sanin komai ba tare da mun wahalaba!'Abdallah yace"Dady inaga kawai a kunna wayar!"Dady jafar ne ya miƙowa Dady Mansur wayar dake hannun sa,karɓa yayi tare da kunnata cikin sakanni sai ga muryar Alhaji Sama'ila na fitowa tun daga farkon fara aikin da Samira tayi na sirri har zuwa inda ya sanar da ita komai akan diamon,wayar tana tsayawa falon ya rude da surutai daga masu Allah wadai sai masu fatan shiriya iyalan su kuwa kuka suke sosai da irin wannan tozarcin da Baffa Hashir da Baba nura suka janyo musu,gaba ɗaya sai sukaji duk sun mozanta acikin mutane,da ƙyar Alhaji Baba ya tsawatar falon ya kuma ɗaukar shuru na wasu ƴan sakanni kana cikin wata irin murya wanda take nuni da tsananin halin baƙin ciki da takaicin da yake ciki yace"sannu Nasiru sannun ku Hashir!''' ɗan shuru yayi saboda wani abu mai ɗaci da ya tokare maƙogaran sa,daga bisani yaci gaba da cewa, abokai na da ƴan uwana sune suka zama masu ha intata muna fukaina masu san ganin bayana,hannu yasa ya ɗan goge ƙwallar dake son fallasa halin da zuciyar shi take ciki,kana ya cigaba da cewa nasan akan wannan dalilin ne na rasa gidan jinina ɗan da babu kamarsa sai dai kwatankwacin sa zan iya yafe komai amma banda wanda ya rabani da ɗan da kuma jikana,amma ku kuje babu komai rayuwace,na barku da Allah tunda yanzu ma ba dabarata ce ta fallasaku ba ƙarshen makircin kune yazo,dan Allah ba ya barin mai zalinci,na gode Allah da rahamar sa agareni na gode Allah da ya kawo min Abdallah cikin zuri'a ta!'ya faɗa yana sakin wani ɗan murmushi na samun sukuni da yayi azuciyar sa a sakamakon yawan ambatan Allah.
Chapter 106 · 0% Book details