Sashe 74
Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A can ɓangaren inno kuwa,cike take da farin cikin ganin Umar ɗin,sai da ta cika gaban sa da kayan taɓawa,kana ta samu guri ta zauna,tana cewa Umari na saukar sassafe kenan kayo mana?ya buɗe baki daniyar bata amsa wayar sa ta fara ringin,dan haka ya fasa faɗar abinda zai faɗa tare da zato wayar,ɗagawa yayi duk da cewa ɓoyayyar nomba ce aka kirashi da ita,karawa yayi akunnen sa tare da yin sallama cikin kamilalliyar muryar shi,daga can ɓangaren akace, ina fata dai da Umar Balarabe nake magana?Abba Umar yace"nine Ina sauraren ka!'daga can aka kuma cewa,yauwa to ba komai ne yasa nakiraka ba sai kawai ɗan na tambayeka shin ka shirya haɗuwa da iyalansa da karasa su tsawon shekaru....
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ¼*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
```Page 44 ```
Wata irin zabura Abba Umar yayi tare da miƙewa tsaye,cikin tashin hankali da rawar baki yace"waye kai?sai dai ina kafin ya kuma cewa wani abu tuni ankashe wayar ɗif, Abba Umar gaba ɗaya ya ruɗe ya kasa yarda ma wayar ta mutu sai nanata hello yake, sai da inno ta tashi ta kama hannun sa tare da zaunar dashi cikin nuna kulawa tace"Umarina me yake faruwa ne?ka nutsu ai ina tunanin ankashe wayar,waye yakiraka a waya,yake son tada maka da hankali?hannu yasa ya goge zufar da take sauko masa kamar wanda aka sheƙawa ruwa,ya kasa amsawa inno tambayoyin ta,gaba ɗaya antayar masa da tsohon mikin dake dan ƙare cikin zuciyarsa,inno karki damu wata ƴar matsala ce daga wajen aikin mune!'to dan Allah ka kwantar da hankalin ka kar kace zaka saka yawan damuwa aranka kaji ko!'murmushi yayi wanda kana gani kasan na yaƙe ne,yace"shike nan inno,bari na wuce wajen Hajiya Babba,daga nan zan ɗan shiga na kwanta, sallamar Abdallah ce ta katse shi daga sallamar da sukeyi da inno, yana tafe hannun sa sarƙafe dana Bintu,inno tace"yauwa Abdallah zo ku gaisa da Abban ku Umar shine kuma ya baka auren Bintu!'ta faɗa tana kallon Bintu da ta rakuɓe a bayan Abdallah,tunda inno ta ambaci sunan Abba Umar ta shiga wani Irin yanayi na matuƙar shauƙi da ƙauna, A hankali ta fito daga bayan Abdallah tana takawa har zuwa gaban Abba Umar tare da durƙusawa kamar yadda taga Abdallah yayi,ƙasa tayi da kan ta tana sauraren bugun da zuciyarta keyi.
Abba Umar kuwa tunda ya zubawa Bintu da Abdallah ido ko ƙiftawa ya kasayi,kuma baya fatan abinda zai rabashi da kallon waɗan nan yara da yake kallon su tamkar wasu taurari acikin idaniyar sa,muryoyin su ne da suka gaida shi atare suka yanke masa tunani da ɗimuwar da ya shiga,cikin wani irin fillin da zuciyar shi ta shiga ya dora hannayen sa duka biyun a kawunan su,yana wani irin murmushi mai ɗauke da wani irin yanayi na tsananin tausayin kansa,yace"sannun ku ƴaƴana tunda kuke cikin gidan nan bamu taɓa haɗuwa ba sai yau,ko da yake Allah ne bai nufa tun can zamu gana ba sai yau ɗin,ina fata dai kuna lafiya? gaba ɗaya suka amsa atare har ɗan duban junan su sukayi saboda yadda suke yawan haɗa baki gurin faɗar abu alokaci guda, Abdallah ne ya fara tashi ganin Abba Umar ɗin yayi hanyar fita,itama tashi tayi tabi su A baya Abdallah yace"inno zamu tafi sai mun dawo!'tace"to Allah ya kiyaye ya bada sa'a ya amsa da Amin kana suka fita gaba ɗayansu.
Suna tafe da Abdallah da Abba Umar suna taɓa hira,tunda yake cikin gidan bai taɓa yin hira ko wata doguwar magana da ƴaƴan Alhaji Baba ba,Amma ƙaunar Baffan nasa da ban take azuciyar sa,ji yake tamkar da mahaifin sa yake magana,shi yasa yakejin wani irin nishadi da farin ciki mai yawa a zuciyar sa,Bintu ma dai tana cikin shauƙin ƙaunar mahaifin nata ji take tamkar taje ta rungume shi tace Abbana ina sonka,acikin wannan hali Dady Habib ya same su,shima cikin biyayya suka gaida shi,am sawa yayi fuska cike da fara'a yace"kai kam Umar kaci sa ar ƴaƴan naka har rakiya suke maka,mu da muke tare da su kullum har yanzu sun kasa sakin jiki damu kamar waɗan da zamu cinye su!'ya fadi maganar cikin yanayin zolaya,ɗan ƙasa da kai Abdallah yayi bai ce komai ba haka nan fuskar sa ba yabo ba fallasa,Abba Umar yace"kasan haɗuwar jini ya faɗa shima cikin zolayar yana miƙawa ɗan uwan nasa hannu dan su daɗa gaisawa,daga nan dai sukayi sallama ya wuce part ɗin Hajiya Babba Dady Habib ma ya shiga falon inno,
Abdallah ya kalli Bintu lokacin da yaga tabi bayan mahaifin nata da kallo,kamo hannun ta yayi cike da tausayi, suna ƙoƙarin shiga motar da Yahya tuni ya buɗe musu yana jira su shiga ya ja,sai ga Dije da sauri har da ɗan hakinta daga Ni dai tayi gudu kafin ta cimma su,tsayawa sukayi gaba ɗaya suna kallon ta sai da ta samu daidaituwar numfashin ta kana suka gaisa da Abdallah Bintu ma gaida ta tayi,Dije tace"ko zaku bani minti biyu zan ɗan yi magana da Bintu? Abdallah ya saki hannun Bintu tare da cewa babu damuwa!'motar ya shiga,ita kuma Bintu suka keɓe da Dije,duban Bintu tayi cikin nutsuwa tace"Bintu ko da hanyar da zaki bi dan bin sahu na A yau? Bintu tace"ban fahimta ba!' ɗan numfasawa Dije tayi tare da ɗan duba hagu da daman ta kana tawa bintu bayanin abinda take nufi da kuma manufar ta naso ta bi bayan nata a yau,sai a san nan Bintu ta fahimci Dije da manufar ta,cikin fargaba da sanyin jiki tace" anya kuwa Mama Dije babu matsala?Dije tace"Bintu wai me yasa kwana biyu naga gaba ɗaya baki da ƙwarin gwiwa ne? mai yake faruwa dake?ko tun maganar mu ta juya ne ya sauya ki haka?wato dai nasihuna basu shiga kunnan ki ba ko? Bintu ta goge hawayen da suke ƙoƙarin zubo mata tace"mama Dije kiyi haƙuri zanyi duk abinda kika Umar ce Ni,amma zan fara gaya masa sai musan shirin da zamuyi wajen bin naki,in yaso idan ta sanar dake inda zaku haɗu sai ki sanar dani ta hanyar kira ko text!'dije tace"insha Allah Bintu, kuma insha Allah mune da nasara lokacin mu ya fara, su sun gama nasu mu kuma yanzu muka fara namu,da haka suka rabu, tunda ta shiga motar tayi jugum ta kasa gaya masa komai,cikin taushin murya ya kira sunan ta tare da zuba mata narkakkun idanun sa, masu saka ta yin abu koda bata so ba,masu saka mata nutsuwa da saukar mata da kasala,hakan ne yasa ta shiga sanar dashi maganar dasu kayi da Dije,ba tare da yace"mata komai ba ya ɗauki waya ya kira, tare da cewa yauwa kazo min da mashin ɗin yanzu ina buƙatar sa cikin gaggawa!'daga haka ya kashe wayar, tafiya suka farayi domin fita daga cikin ESTATE ɗin.
Tunda ya shiga ɓangaren Hajiya Babba bai samu wata cikakkiyar nutsuwa ba saboda hankalin sa ya rabu kashi kashi,ga tunanin wan da yayi masa waya ga kuma tunanin hotan Bintu da ta kasa ɓacewa daga fuskar sa da zuciyar sa,ba tare da ya cika lokacin da Yakamata ya kai ba,ya miƙe yana cewa Hajiya Babba Ni zan je na ɗan kwanta ina so zan ɗan yi bacci!'hajiya bata takura masa da tambayar sa meke damun saba dan tasan tatsuniyar gizo bata wuce ƙoƙi, addu'a kawai tabishi da ita,
Wayar Bintu ce ta ɗau haske alamar shigowar saƙo, tare suka kai hannun su kan wayar ita da Abdallah,wani irin musayar kallo suka tsaya yi ga hannayen su a haɗe kan waya, Bintu ce ta fara janye idanun ta da hannunta,tana kuma jin wannan yanayin na shigar ta,ɗaukar wayar yayi ya buɗe sakon da ya shigo,sai yaga daga Anty Nafisa ne saƙon,ɗan satar kallon ta yayi sai yaga gaba ɗaya hankalin ta baya kan sa,hakan ne yasa ya buɗe saƙon tare da karantawa A hankali batare da Bintu taji ba,
Bintu na gamsu da shawarar ki zan tambayi Umar damuwar sa ko zai gaya min duk da cewa na aikata wani abu daban batare da sanin ki ba,ba dan komai kuma nayi haka ba sai dan inaso in zunguro damuwarsa tare da bugar cikin sa akan abinda nake tunani a game da shi,to bai shigo ba dai har yanzu ina jiran sa domin ganin ko aikina yayi kyau,ba lallai bane sai kinji komai amma dai nasa ankirashi awaya an bugi cikin sa tare da zunguro damuwar sa yadda idan ya shigo na tambaye shi ba zai taɓa iya ɓoye min ba,a wannan karon dai nayi abin kirki nayi abu da basirata ba basirar Bintu ba,daga haka ta saka alamar dariya,ɗagowa yayi daga kallon wayar sai karaf ya tsinci fararen idanunta akan sa,kawar da kan sa yayi tare da kashe wayar dan baiga amfanin wan nan saƙo ba kuma yana ganin kamar zai iya tada hankalin ruɗaɗɗiyar Bint ɗin tasa,kar bar wayar tayi daga hannun sa tana cewa waye ya turo saƙo?bai damu dan ta karɓi wayar ba kasan cewar ya riga ya goge saƙon,hakan ne yasa bata ga komai ba,sai dai kallon tuhuma da tabi kyakykyawar fuskar sa da shi,lumshe idanun sa yayi, yayi tamkar bai san me take nufi ba,ita kuma hakan ne yabata damar cigaba da kare wa fuskar sa kallo tare da kaifafa kallonta akan ɗan zagayayyen gemun sa da yake matuƙar burgeta, a rayuwar ta tana son wan nan Abu a fuskar Abdallah shi yasa take yawan satar kallon sa,dan sam bata gajiya da kallon fuskar tasa,jitayi yace"kallon fa?wani irin kunya ne ya rufeta wanda yasa tayi saurin rufe kanta cikin hijabin ta kuma shine dalilin da yasa bata kuma ɗagowa ba har suka je inda zasu,a nan ɗin ma daƙyar tafita daga motar sai faman sinƙe kai takeyi.
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ¼*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
```Page 44 ```
Wata irin zabura Abba Umar yayi tare da miƙewa tsaye,cikin tashin hankali da rawar baki yace"waye kai?sai dai ina kafin ya kuma cewa wani abu tuni ankashe wayar ɗif, Abba Umar gaba ɗaya ya ruɗe ya kasa yarda ma wayar ta mutu sai nanata hello yake, sai da inno ta tashi ta kama hannun sa tare da zaunar dashi cikin nuna kulawa tace"Umarina me yake faruwa ne?ka nutsu ai ina tunanin ankashe wayar,waye yakiraka a waya,yake son tada maka da hankali?hannu yasa ya goge zufar da take sauko masa kamar wanda aka sheƙawa ruwa,ya kasa amsawa inno tambayoyin ta,gaba ɗaya antayar masa da tsohon mikin dake dan ƙare cikin zuciyarsa,inno karki damu wata ƴar matsala ce daga wajen aikin mune!'to dan Allah ka kwantar da hankalin ka kar kace zaka saka yawan damuwa aranka kaji ko!'murmushi yayi wanda kana gani kasan na yaƙe ne,yace"shike nan inno,bari na wuce wajen Hajiya Babba,daga nan zan ɗan shiga na kwanta, sallamar Abdallah ce ta katse shi daga sallamar da sukeyi da inno, yana tafe hannun sa sarƙafe dana Bintu,inno tace"yauwa Abdallah zo ku gaisa da Abban ku Umar shine kuma ya baka auren Bintu!'ta faɗa tana kallon Bintu da ta rakuɓe a bayan Abdallah,tunda inno ta ambaci sunan Abba Umar ta shiga wani Irin yanayi na matuƙar shauƙi da ƙauna, A hankali ta fito daga bayan Abdallah tana takawa har zuwa gaban Abba Umar tare da durƙusawa kamar yadda taga Abdallah yayi,ƙasa tayi da kan ta tana sauraren bugun da zuciyarta keyi.
Abba Umar kuwa tunda ya zubawa Bintu da Abdallah ido ko ƙiftawa ya kasayi,kuma baya fatan abinda zai rabashi da kallon waɗan nan yara da yake kallon su tamkar wasu taurari acikin idaniyar sa,muryoyin su ne da suka gaida shi atare suka yanke masa tunani da ɗimuwar da ya shiga,cikin wani irin fillin da zuciyar shi ta shiga ya dora hannayen sa duka biyun a kawunan su,yana wani irin murmushi mai ɗauke da wani irin yanayi na tsananin tausayin kansa,yace"sannun ku ƴaƴana tunda kuke cikin gidan nan bamu taɓa haɗuwa ba sai yau,ko da yake Allah ne bai nufa tun can zamu gana ba sai yau ɗin,ina fata dai kuna lafiya? gaba ɗaya suka amsa atare har ɗan duban junan su sukayi saboda yadda suke yawan haɗa baki gurin faɗar abu alokaci guda, Abdallah ne ya fara tashi ganin Abba Umar ɗin yayi hanyar fita,itama tashi tayi tabi su A baya Abdallah yace"inno zamu tafi sai mun dawo!'tace"to Allah ya kiyaye ya bada sa'a ya amsa da Amin kana suka fita gaba ɗayansu.
Suna tafe da Abdallah da Abba Umar suna taɓa hira,tunda yake cikin gidan bai taɓa yin hira ko wata doguwar magana da ƴaƴan Alhaji Baba ba,Amma ƙaunar Baffan nasa da ban take azuciyar sa,ji yake tamkar da mahaifin sa yake magana,shi yasa yakejin wani irin nishadi da farin ciki mai yawa a zuciyar sa,Bintu ma dai tana cikin shauƙin ƙaunar mahaifin nata ji take tamkar taje ta rungume shi tace Abbana ina sonka,acikin wannan hali Dady Habib ya same su,shima cikin biyayya suka gaida shi,am sawa yayi fuska cike da fara'a yace"kai kam Umar kaci sa ar ƴaƴan naka har rakiya suke maka,mu da muke tare da su kullum har yanzu sun kasa sakin jiki damu kamar waɗan da zamu cinye su!'ya fadi maganar cikin yanayin zolaya,ɗan ƙasa da kai Abdallah yayi bai ce komai ba haka nan fuskar sa ba yabo ba fallasa,Abba Umar yace"kasan haɗuwar jini ya faɗa shima cikin zolayar yana miƙawa ɗan uwan nasa hannu dan su daɗa gaisawa,daga nan dai sukayi sallama ya wuce part ɗin Hajiya Babba Dady Habib ma ya shiga falon inno,
Abdallah ya kalli Bintu lokacin da yaga tabi bayan mahaifin nata da kallo,kamo hannun ta yayi cike da tausayi, suna ƙoƙarin shiga motar da Yahya tuni ya buɗe musu yana jira su shiga ya ja,sai ga Dije da sauri har da ɗan hakinta daga Ni dai tayi gudu kafin ta cimma su,tsayawa sukayi gaba ɗaya suna kallon ta sai da ta samu daidaituwar numfashin ta kana suka gaisa da Abdallah Bintu ma gaida ta tayi,Dije tace"ko zaku bani minti biyu zan ɗan yi magana da Bintu? Abdallah ya saki hannun Bintu tare da cewa babu damuwa!'motar ya shiga,ita kuma Bintu suka keɓe da Dije,duban Bintu tayi cikin nutsuwa tace"Bintu ko da hanyar da zaki bi dan bin sahu na A yau? Bintu tace"ban fahimta ba!' ɗan numfasawa Dije tayi tare da ɗan duba hagu da daman ta kana tawa bintu bayanin abinda take nufi da kuma manufar ta naso ta bi bayan nata a yau,sai a san nan Bintu ta fahimci Dije da manufar ta,cikin fargaba da sanyin jiki tace" anya kuwa Mama Dije babu matsala?Dije tace"Bintu wai me yasa kwana biyu naga gaba ɗaya baki da ƙwarin gwiwa ne? mai yake faruwa dake?ko tun maganar mu ta juya ne ya sauya ki haka?wato dai nasihuna basu shiga kunnan ki ba ko? Bintu ta goge hawayen da suke ƙoƙarin zubo mata tace"mama Dije kiyi haƙuri zanyi duk abinda kika Umar ce Ni,amma zan fara gaya masa sai musan shirin da zamuyi wajen bin naki,in yaso idan ta sanar dake inda zaku haɗu sai ki sanar dani ta hanyar kira ko text!'dije tace"insha Allah Bintu, kuma insha Allah mune da nasara lokacin mu ya fara, su sun gama nasu mu kuma yanzu muka fara namu,da haka suka rabu, tunda ta shiga motar tayi jugum ta kasa gaya masa komai,cikin taushin murya ya kira sunan ta tare da zuba mata narkakkun idanun sa, masu saka ta yin abu koda bata so ba,masu saka mata nutsuwa da saukar mata da kasala,hakan ne yasa ta shiga sanar dashi maganar dasu kayi da Dije,ba tare da yace"mata komai ba ya ɗauki waya ya kira, tare da cewa yauwa kazo min da mashin ɗin yanzu ina buƙatar sa cikin gaggawa!'daga haka ya kashe wayar, tafiya suka farayi domin fita daga cikin ESTATE ɗin.
Tunda ya shiga ɓangaren Hajiya Babba bai samu wata cikakkiyar nutsuwa ba saboda hankalin sa ya rabu kashi kashi,ga tunanin wan da yayi masa waya ga kuma tunanin hotan Bintu da ta kasa ɓacewa daga fuskar sa da zuciyar sa,ba tare da ya cika lokacin da Yakamata ya kai ba,ya miƙe yana cewa Hajiya Babba Ni zan je na ɗan kwanta ina so zan ɗan yi bacci!'hajiya bata takura masa da tambayar sa meke damun saba dan tasan tatsuniyar gizo bata wuce ƙoƙi, addu'a kawai tabishi da ita,
Wayar Bintu ce ta ɗau haske alamar shigowar saƙo, tare suka kai hannun su kan wayar ita da Abdallah,wani irin musayar kallo suka tsaya yi ga hannayen su a haɗe kan waya, Bintu ce ta fara janye idanun ta da hannunta,tana kuma jin wannan yanayin na shigar ta,ɗaukar wayar yayi ya buɗe sakon da ya shigo,sai yaga daga Anty Nafisa ne saƙon,ɗan satar kallon ta yayi sai yaga gaba ɗaya hankalin ta baya kan sa,hakan ne yasa ya buɗe saƙon tare da karantawa A hankali batare da Bintu taji ba,
Bintu na gamsu da shawarar ki zan tambayi Umar damuwar sa ko zai gaya min duk da cewa na aikata wani abu daban batare da sanin ki ba,ba dan komai kuma nayi haka ba sai dan inaso in zunguro damuwarsa tare da bugar cikin sa akan abinda nake tunani a game da shi,to bai shigo ba dai har yanzu ina jiran sa domin ganin ko aikina yayi kyau,ba lallai bane sai kinji komai amma dai nasa ankirashi awaya an bugi cikin sa tare da zunguro damuwar sa yadda idan ya shigo na tambaye shi ba zai taɓa iya ɓoye min ba,a wannan karon dai nayi abin kirki nayi abu da basirata ba basirar Bintu ba,daga haka ta saka alamar dariya,ɗagowa yayi daga kallon wayar sai karaf ya tsinci fararen idanunta akan sa,kawar da kan sa yayi tare da kashe wayar dan baiga amfanin wan nan saƙo ba kuma yana ganin kamar zai iya tada hankalin ruɗaɗɗiyar Bint ɗin tasa,kar bar wayar tayi daga hannun sa tana cewa waye ya turo saƙo?bai damu dan ta karɓi wayar ba kasan cewar ya riga ya goge saƙon,hakan ne yasa bata ga komai ba,sai dai kallon tuhuma da tabi kyakykyawar fuskar sa da shi,lumshe idanun sa yayi, yayi tamkar bai san me take nufi ba,ita kuma hakan ne yabata damar cigaba da kare wa fuskar sa kallo tare da kaifafa kallonta akan ɗan zagayayyen gemun sa da yake matuƙar burgeta, a rayuwar ta tana son wan nan Abu a fuskar Abdallah shi yasa take yawan satar kallon sa,dan sam bata gajiya da kallon fuskar tasa,jitayi yace"kallon fa?wani irin kunya ne ya rufeta wanda yasa tayi saurin rufe kanta cikin hijabin ta kuma shine dalilin da yasa bata kuma ɗagowa ba har suka je inda zasu,a nan ɗin ma daƙyar tafita daga motar sai faman sinƙe kai takeyi.