Sashe 73
Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin yanayin sa na ƙoƙarin ɓoye damuwar dake cikin zuciyar sa ya ɗan karyar da kan sa tare da cewa"inno tsoro ne kawai da ita san nan kuma,,sai ya ɗan yi shuru kamar yana lalubo abinda zai cewa innon,kana ya cigaba da cewa, sannan tana yawan tsorata ko mai tsoro ne yake bata,kamar dai bata jin daɗi!'ya ƙarasa maganar da ɗan kallon Bintun,inno cikin damuwa da tashin hankali tace"subhanallah me yake tsorata ki Bintu?ta juya tambayar ta kan Bintu, Bintu dai ta kasa magana sai hawaye,dan bata san mai zatace da inno ba,inno tace"anya ba makaraine suke san shafar ta ba?tayi maganar tana duban Abdallah,yayin da shi kuma ya zubawa Bintu idanu wanda maganar inno tayi saurin hasko masa wani abu makamancin abinda ta faɗa,(idan baku manta ba Abdallah yayi ilmin addini mai matukar zurfi,so dan haka yana da ilmin sanin sihiri ko jinnu saɓanin wasu ƴan bokon da zaku ga sam basu yadda da irin wannan abun ba, Abdallah yasan cewa sihiri gaskiya ne haka jinnu ma gaskiya ne,dan haka bai jahilci maganar inno ba)tsai yayi da ransa yana mai hasaso al al'amarin Bintu tabbas tana buƙatar addu'a,amma dai bai kawowa ranshi ga wanda yayiwa Bintu wani abu ba kawai dai yasan Bintu al'amarin ta yana buƙatar addu'a duba da yadda gaba ɗaya ta birkice ko addu'a bata son yi wanda shi kansa shaida ne akan Bintu ba haka take ba tun kafin suyi kusan ci da juna yasan tana da matukar riƙoda ibada,shi yasa yanzu bai sha wahalar gano yadda take sakaci da addu'a ba.
A hankali ya ɗauke idon sa daga kallon da ya ƙure Bintu da shi,ya maida kan inno tayi zukuɗi tana jiran amsar sa,sai da ya ɗan huro iska daga bakin sa kana yace"hakane inno addu'a ya kamata ayi mata,insha Allah gobe zamu fita akwai wani malamina zamuje gurin sa!'murmushi inno tayi dan da tayi tunanin Abdallah ba zai yadda da abinda tace"ba,yauwa hakan yayi Allah Ubangiji ya kareku daga sharrin mutum da aljan ya tsare bayanku da gaban ku yasa kusa zama abin kallo da tsoro a idon maƙiayan ku,Amin Abdallah ya amsa yana mai juyawa dan shiga falon sa,yayin da inno ta bar zuciyar Bintu cikin wani irin hali na tunani da,tsoro mai tsanani,a hankali ta ta taka tabi bayan sa,tana waiwayen inno da take ta Binta da wani irin murmushi mai cike da ma anoni masu tarin yawa,a haka ta shige falon wanda shine sanadin rabata da kallon inno,tana rufe ƙofar ta zame ajikinta tare da saka wani irin kuka mai taɓa zuciya wai ya zatayi idan akace yau binciken ta ya gano mata inno cikin mugayen da take zargi,ya zatayi da rayuwar ta idan akace yau macen da take ƙauna,takewa kallon tafi kowa ƙaunar ta,a cikin gidan nan, tabbas wannan fargabar ita zata jefata cikin wani mugun hali na damuwa,jin an kamota yasa ta ɗaga jiƙaƙƙun idanun ta tana kallon sa wanda shima ɗin kallon idanun take bayan ya samu nasarar ɗagota daga zaunewar da tayi,cikin neman agajin makusancin ta ta faɗa jikinsa tare da fashewa da kukan da take jin ta fara shi kenan har sai zuwa ranar da gaskiya ta baiyana,idan kuma gaskiyar ta baiyana a gaɓar da bazataso ba tabbas hawayenta bazasu taɓa daina zuba ba,tana ƙaunar inno har cikin ƙashi da jinin ta,kamata yayi suka fara tafiya har zuwa ɗakinsa zama yayi da ita ajikin sa,yayin da zuciyar sa take san gagarar ɓoye damuwar sa a wannan karon,wanda yake tunanin girman damuwar wannan lokacin ne yayi mata yawa,jingina yayi ya ɗan kashin giɗa ya kasa ce mata komai har yanzu dan bai san ta ina zai fara ba,
Cikin tausayawa kanta da rayuwar da zata fuskanta nan gaba ta fara bashi labarin yadda sukayi da Dije,ba tare da ta ɓoye masa ko alif ba,ta gama maganar tana mai cusa kanta cikin jikinsa tana murzawa wanda hakan ne yake nuni da tsananin damuwar da take ciki,cikin muryar ta da ta dashe tace"Yahh Abdallah,yaya zanyi da wannan aiki da ya ɓullo min?kagayan ta ina zan fara bincikar matan da suka fi nunamin ƙauna ta gaskiya a cikin wannan duniyar,su kaɗai ne matan danasan sun fara ƙaunata bayan ƙaunar mahaifiyata,su kaɗai ne matan da suka karɓeni batare da ƙyama ba su kaɗai ne matan da suka fifita ƙaunata akan ƙaunar jikokin su batare da sun san Ni ɗin jinin su bane,su kaɗai ne matan da suka fara yarda dani alokacin da narasa yadda da amincin kowa a cikin gidan nan,sun maida Ni mutum sun maida Ni jikar su sun yi faɗa da jikokin su akaina,to kagayamin me yasa ba zan shiga wani hali ba duk ranar da akace wannan ƙauna ta munafunci ce ta yaudara ce ta ha inci ce,me kake tunanin zanyi a ranar, wallahi ba zan iya ɗauka ba,Ni bazan iya ba!'ta faɗa tana bugun ƙirjin shi tare da ƙara sakin wani marayan kuka mai ƙun tata zuciyar maiyin sa da kuma mai sauraren sa,hannun ta ya kama duka ya riƙe kana cikin wata irin murya da ta saukarwa da Bintu nutsuwa da kasala yace"Bint!'shiru tayi tare da yin luf tamkar wadda bata numfashi,hannu yasa ya shiga gyara mata lallausar sumar kanta wadda duk ta bar baje,kana yaci gaba da cewa',Bint injin ke musulma ce?jin jina kan ta yi batare da ta ɗago ba,yace"yauwa to kinga kuwa dole ki amshi ƙaddararki duk yadda yazo miki domin wannan shine cikar imaninki da cikarki musulma,kuma bawa baya taɓa tsallake wa ƙaddarar sa to ki ƙaddara haka taki ƙaddarar tazo kuma bazaki taɓa iya sauya ta ba,ko baki ga yadda Ni nake rayuwata ba?Bint kin san rayuwar da nayi kuwa kin san rayuwar ƙuncin da danayi kin san yadda aka ƙuntatawa rayuwata,kin san yadda nayi rayuwa a hannun kafurai alhalin Ni ina cikakken musulmi?kin san yadda zuciyata takeyi aduk lokacin da aka ƙuntatawa rayuwata da yin ibadar da batawa ba kuma addinin da ban yadda dashi ba, Bint amsar itace duk baki san wan nan ba baki san meye abinda na fuskanta a cikin rayuwata ba, taki kawai kika sani,dan haka ina so kiyi haƙuri,mu fuskanci abinda ke gaban mu abinda Dije ta gaya miki gaskiya ne,baka taɓa gane munafukin ka sai da dabaru,kuma baka taɓa gane masoyin ka na gaskiya sai kashi ga halin rayuwa,ɗago kanta yayi,yana kallon fuskar ta sauri tayi ta rufe idon ta saboda wani kallo da taga yana mata mai shiga cikin jiki da jini,ɗaga mata gira yayi cikin wani irin salo da shi kansa bai san ya iya shi ba, hakan ne ya bata kunya har ta maida kanta ta sunne ajikin sa,
Ɗaga ta yayi tare da cewa bamu ga ta bacci Bint muna da babban yaƙi agabanmu muna da buƙatun da muke nema Allah ya biya mana,dan haka dole mutashi mu roƙe shi kiyi haƙuri ki Kore duk abinda ke kawo miki farmaki da wasu wasi cikin zuciyarki kinji ko!'ya faɗa cikin matuƙar nuna kulawar sa gareta,
Kallon sa kawai take cike da mamakin sa,dama haka yake da matukar tausayi, tabbas tayi mamakin yadda akayi ya tsaya yana nuna kulawar sa akan ta kamar haka,mutumin da tasan baya yin shiri da duk wani abu da zai saka shi yin surutu mai tsayi,ta shi tayi kamar yadda ya Umar ce dan yan zu ya riga ya karya mata zuciya da kalaman sa, sai taji tana matuƙar san jin labarin sa dan ga dukkanin alamu ya sha gwagwarmaya da ƙalubale a cikin rayuwar sa.
Sun daɗe suna salloli duk da dai Bintu dauriya kawai take yi, amma sam bata jin daɗin jikinta da dukkanin rayuwar ta,amma cikin taimakon jarumin mijinta mai tsananin riƙo da addinin sa mai kishin addinin sa ta samu ƙwarin gwiwar ganawa da ubangijin ta,cikin ƙarfin hali da miƙa lamuran su gare shi,basu suka kwanta ba sai misalin ƙarfe uku na dare,daga nan suka sami yin Bacci cikin salama da nutsuwar zuciya,
A cikin wannan safiyar kuma da ta waye Abba Umar ya dawo daga ƙasar Italiya,wanda hakan ba ƙaramin daɗi yayiwa Anty Nafisa ba, tunda ta riga ta sakawa ranta zata yi abinda Bintu ta shawar ta mata,hakan ne yasa tayi masa shirye-shiryen da ta daɗe bata yi masa irin sa ba,shi kansa sai da yayi mamakin hakan,amma dai bai kawo komai cikin zuciyar sa ba,lokacin da ya gama shirin sa ya fito tsaf dashi dan zuwa gaida mahaifinsa da iyayen sa mata har ta gama yi masa duk wani shiri,sai dai yace tayi haƙuri yaje ya gaida iyayen sa,dole tayi masa fatan dawowa lafiya duk da zaƙuwar da tayi suyi maganar datake cin ranta,
Sai da ya fara zuwa ɓangaren Hajjah kana ya fito ya shiga ɓangaren inno,wanda a daidai lokacin ne kuma Bintu da Abdallah suka fito dan zuwa gurin malamin sa malam Nuhu da yace zasu je,tunda ta doso falon ta dinga jin zuciyar ta na wani irin bugu wanda har saida ta dafe ƙirjinta, cikin kulawa Abdallah ya ruƙota ganin tana ƙoƙarin faɗuwa,kallon sa tayi idanun ta cike taf da ƙwalla, ɗan girgiza mata kai yayi kana yasa hannu ya goge mata wadda ta fara zubowa kan fuskarta,tare da jan hannun ta suka fito falon tare da ƴar guntuwar sallama saman leban sa,
A can ɓangaren Dije kuwa tun bayan rabuwar su da Bintu uwar ɗakinta tayi mata waya da ɓoyayyar nomba kamar yadda ta saba,ta sanar da ita a safiyar yau ɗin tana son su haɗu, sai dai bata gaya mata inda zasu haɗu ba, tasan dai sai tabar gidan zata faɗa mata kamar yadda ta saba yi,shi yasa tunda ta tashi take sauri dan tana son haɗuwa da Bintu,saboda tunanin da tayi,akan haɗuwar su da Hajiyar yau,zata gayawa Bintu ta yi ƙoƙarin biyota a baya,tunanin ta anan kuwa,tasan Bintu tana da tunani da wayo,idan taga koda bayan matar zata iya ƙoƙarin shaida ta aduk inda ta ganta, shi yasa take son lallai Bintu tabi ta ayau, tana ganin hakan ma kamar wata hanya ce zata sauƙaƙa musu aiki,cikin hanzari ta gama duk aiyukan ta,tare da kimtsawa ta fita dan zuwa sashen inno,
A hankali ya ɗauke idon sa daga kallon da ya ƙure Bintu da shi,ya maida kan inno tayi zukuɗi tana jiran amsar sa,sai da ya ɗan huro iska daga bakin sa kana yace"hakane inno addu'a ya kamata ayi mata,insha Allah gobe zamu fita akwai wani malamina zamuje gurin sa!'murmushi inno tayi dan da tayi tunanin Abdallah ba zai yadda da abinda tace"ba,yauwa hakan yayi Allah Ubangiji ya kareku daga sharrin mutum da aljan ya tsare bayanku da gaban ku yasa kusa zama abin kallo da tsoro a idon maƙiayan ku,Amin Abdallah ya amsa yana mai juyawa dan shiga falon sa,yayin da inno ta bar zuciyar Bintu cikin wani irin hali na tunani da,tsoro mai tsanani,a hankali ta ta taka tabi bayan sa,tana waiwayen inno da take ta Binta da wani irin murmushi mai cike da ma anoni masu tarin yawa,a haka ta shige falon wanda shine sanadin rabata da kallon inno,tana rufe ƙofar ta zame ajikinta tare da saka wani irin kuka mai taɓa zuciya wai ya zatayi idan akace yau binciken ta ya gano mata inno cikin mugayen da take zargi,ya zatayi da rayuwar ta idan akace yau macen da take ƙauna,takewa kallon tafi kowa ƙaunar ta,a cikin gidan nan, tabbas wannan fargabar ita zata jefata cikin wani mugun hali na damuwa,jin an kamota yasa ta ɗaga jiƙaƙƙun idanun ta tana kallon sa wanda shima ɗin kallon idanun take bayan ya samu nasarar ɗagota daga zaunewar da tayi,cikin neman agajin makusancin ta ta faɗa jikinsa tare da fashewa da kukan da take jin ta fara shi kenan har sai zuwa ranar da gaskiya ta baiyana,idan kuma gaskiyar ta baiyana a gaɓar da bazataso ba tabbas hawayenta bazasu taɓa daina zuba ba,tana ƙaunar inno har cikin ƙashi da jinin ta,kamata yayi suka fara tafiya har zuwa ɗakinsa zama yayi da ita ajikin sa,yayin da zuciyar sa take san gagarar ɓoye damuwar sa a wannan karon,wanda yake tunanin girman damuwar wannan lokacin ne yayi mata yawa,jingina yayi ya ɗan kashin giɗa ya kasa ce mata komai har yanzu dan bai san ta ina zai fara ba,
Cikin tausayawa kanta da rayuwar da zata fuskanta nan gaba ta fara bashi labarin yadda sukayi da Dije,ba tare da ta ɓoye masa ko alif ba,ta gama maganar tana mai cusa kanta cikin jikinsa tana murzawa wanda hakan ne yake nuni da tsananin damuwar da take ciki,cikin muryar ta da ta dashe tace"Yahh Abdallah,yaya zanyi da wannan aiki da ya ɓullo min?kagayan ta ina zan fara bincikar matan da suka fi nunamin ƙauna ta gaskiya a cikin wannan duniyar,su kaɗai ne matan danasan sun fara ƙaunata bayan ƙaunar mahaifiyata,su kaɗai ne matan da suka karɓeni batare da ƙyama ba su kaɗai ne matan da suka fifita ƙaunata akan ƙaunar jikokin su batare da sun san Ni ɗin jinin su bane,su kaɗai ne matan da suka fara yarda dani alokacin da narasa yadda da amincin kowa a cikin gidan nan,sun maida Ni mutum sun maida Ni jikar su sun yi faɗa da jikokin su akaina,to kagayamin me yasa ba zan shiga wani hali ba duk ranar da akace wannan ƙauna ta munafunci ce ta yaudara ce ta ha inci ce,me kake tunanin zanyi a ranar, wallahi ba zan iya ɗauka ba,Ni bazan iya ba!'ta faɗa tana bugun ƙirjin shi tare da ƙara sakin wani marayan kuka mai ƙun tata zuciyar maiyin sa da kuma mai sauraren sa,hannun ta ya kama duka ya riƙe kana cikin wata irin murya da ta saukarwa da Bintu nutsuwa da kasala yace"Bint!'shiru tayi tare da yin luf tamkar wadda bata numfashi,hannu yasa ya shiga gyara mata lallausar sumar kanta wadda duk ta bar baje,kana yaci gaba da cewa',Bint injin ke musulma ce?jin jina kan ta yi batare da ta ɗago ba,yace"yauwa to kinga kuwa dole ki amshi ƙaddararki duk yadda yazo miki domin wannan shine cikar imaninki da cikarki musulma,kuma bawa baya taɓa tsallake wa ƙaddarar sa to ki ƙaddara haka taki ƙaddarar tazo kuma bazaki taɓa iya sauya ta ba,ko baki ga yadda Ni nake rayuwata ba?Bint kin san rayuwar da nayi kuwa kin san rayuwar ƙuncin da danayi kin san yadda aka ƙuntatawa rayuwata,kin san yadda nayi rayuwa a hannun kafurai alhalin Ni ina cikakken musulmi?kin san yadda zuciyata takeyi aduk lokacin da aka ƙuntatawa rayuwata da yin ibadar da batawa ba kuma addinin da ban yadda dashi ba, Bint amsar itace duk baki san wan nan ba baki san meye abinda na fuskanta a cikin rayuwata ba, taki kawai kika sani,dan haka ina so kiyi haƙuri,mu fuskanci abinda ke gaban mu abinda Dije ta gaya miki gaskiya ne,baka taɓa gane munafukin ka sai da dabaru,kuma baka taɓa gane masoyin ka na gaskiya sai kashi ga halin rayuwa,ɗago kanta yayi,yana kallon fuskar ta sauri tayi ta rufe idon ta saboda wani kallo da taga yana mata mai shiga cikin jiki da jini,ɗaga mata gira yayi cikin wani irin salo da shi kansa bai san ya iya shi ba, hakan ne ya bata kunya har ta maida kanta ta sunne ajikin sa,
Ɗaga ta yayi tare da cewa bamu ga ta bacci Bint muna da babban yaƙi agabanmu muna da buƙatun da muke nema Allah ya biya mana,dan haka dole mutashi mu roƙe shi kiyi haƙuri ki Kore duk abinda ke kawo miki farmaki da wasu wasi cikin zuciyarki kinji ko!'ya faɗa cikin matuƙar nuna kulawar sa gareta,
Kallon sa kawai take cike da mamakin sa,dama haka yake da matukar tausayi, tabbas tayi mamakin yadda akayi ya tsaya yana nuna kulawar sa akan ta kamar haka,mutumin da tasan baya yin shiri da duk wani abu da zai saka shi yin surutu mai tsayi,ta shi tayi kamar yadda ya Umar ce dan yan zu ya riga ya karya mata zuciya da kalaman sa, sai taji tana matuƙar san jin labarin sa dan ga dukkanin alamu ya sha gwagwarmaya da ƙalubale a cikin rayuwar sa.
Sun daɗe suna salloli duk da dai Bintu dauriya kawai take yi, amma sam bata jin daɗin jikinta da dukkanin rayuwar ta,amma cikin taimakon jarumin mijinta mai tsananin riƙo da addinin sa mai kishin addinin sa ta samu ƙwarin gwiwar ganawa da ubangijin ta,cikin ƙarfin hali da miƙa lamuran su gare shi,basu suka kwanta ba sai misalin ƙarfe uku na dare,daga nan suka sami yin Bacci cikin salama da nutsuwar zuciya,
A cikin wannan safiyar kuma da ta waye Abba Umar ya dawo daga ƙasar Italiya,wanda hakan ba ƙaramin daɗi yayiwa Anty Nafisa ba, tunda ta riga ta sakawa ranta zata yi abinda Bintu ta shawar ta mata,hakan ne yasa tayi masa shirye-shiryen da ta daɗe bata yi masa irin sa ba,shi kansa sai da yayi mamakin hakan,amma dai bai kawo komai cikin zuciyar sa ba,lokacin da ya gama shirin sa ya fito tsaf dashi dan zuwa gaida mahaifinsa da iyayen sa mata har ta gama yi masa duk wani shiri,sai dai yace tayi haƙuri yaje ya gaida iyayen sa,dole tayi masa fatan dawowa lafiya duk da zaƙuwar da tayi suyi maganar datake cin ranta,
Sai da ya fara zuwa ɓangaren Hajjah kana ya fito ya shiga ɓangaren inno,wanda a daidai lokacin ne kuma Bintu da Abdallah suka fito dan zuwa gurin malamin sa malam Nuhu da yace zasu je,tunda ta doso falon ta dinga jin zuciyar ta na wani irin bugu wanda har saida ta dafe ƙirjinta, cikin kulawa Abdallah ya ruƙota ganin tana ƙoƙarin faɗuwa,kallon sa tayi idanun ta cike taf da ƙwalla, ɗan girgiza mata kai yayi kana yasa hannu ya goge mata wadda ta fara zubowa kan fuskarta,tare da jan hannun ta suka fito falon tare da ƴar guntuwar sallama saman leban sa,
A can ɓangaren Dije kuwa tun bayan rabuwar su da Bintu uwar ɗakinta tayi mata waya da ɓoyayyar nomba kamar yadda ta saba,ta sanar da ita a safiyar yau ɗin tana son su haɗu, sai dai bata gaya mata inda zasu haɗu ba, tasan dai sai tabar gidan zata faɗa mata kamar yadda ta saba yi,shi yasa tunda ta tashi take sauri dan tana son haɗuwa da Bintu,saboda tunanin da tayi,akan haɗuwar su da Hajiyar yau,zata gayawa Bintu ta yi ƙoƙarin biyota a baya,tunanin ta anan kuwa,tasan Bintu tana da tunani da wayo,idan taga koda bayan matar zata iya ƙoƙarin shaida ta aduk inda ta ganta, shi yasa take son lallai Bintu tabi ta ayau, tana ganin hakan ma kamar wata hanya ce zata sauƙaƙa musu aiki,cikin hanzari ta gama duk aiyukan ta,tare da kimtsawa ta fita dan zuwa sashen inno,