Sashe 22
Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bintu tayi luf jikin Hajiya Babba, yayin da wata irin ƙauna me haɗe da kewa ta lulluɓe zuciyar ta tanajin kamar ta dauwama tare da wannan mata mai tsananin kyau kamala kirki da nagarta, muryar Rahima ce ta katse mata tunani da cewa kai Hajiya Babba dama nasan haka zaki min shi yasa tunda kike cewa na kawo miki Bintu naƙi kawota nasan fada zata ƙwacen A gurinki!'Hajiya Babba tayi ɗan murmushi irin nasu na manya tana ta ɗan shafa kan Bintu, yarinyar ta shiga ranta sosai tanajin shauƙin ƙaunarta tamkar su Raihana.
Sun daɗe A sashen Hajiya Babba, Bintu ta sake sosai da ita saboda yadda Hajiya ta sakar mata fuska ta nuna mata ƙauna ta zahiri da ba ɗini, haka da zasu tafi Hajiya ta Haɗa mata kayan amfani sosai kana sukayi sallama, Hajiya taji kewar yaran sosai.
Kewayawa sukeyi cikin Babban ESTATE ɗin, Raihana tana nuna mata kowane ɓangare da kuma me shi, sunzo dai dai ta wajen hanyar da zaka miƙa ka koma ta cikin wannan ɗakin, Bintu ta da kata, yayin da ta zubawa hanyar ido tana tuno abinda ya faru ranar tamkar A lokacin yake faruwa,sai da Raihana ta taɓata kana ta dawo haiyacinta tare da cewa Raihana gurin nan ya burgeni muje ta wajen mu zaga, naga kamar lambuneee......
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ¼*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
```Page 17 ```
A tsorace Rahima take duban Bintu cikin tabbatar mata da abinda zata faɗa, tace" ke Bintu ki rufa mana Asiri kin san kuwa babu wanda yake iya bi ta wajan nan!' Bintu cikin tsananin mamaki tace" to saboda me? kuma waye ya hana zuwa gurin?Raihana tace" babu wanda ya hana, hasalima ba A taɓa yiwa kowa gargaɗi da zuwa wajen ba, nima haka nataso nagani ba wanda yake iya zuwa, sai dai ban taɓa tunanin yin tawajen ba kuma bantaɓa ganin wani yaje ba ko zancen babu wanda ya taɓa yi balle musan dalili!' tunda ta fara magana Bintu take kallon bakinta cike da maɗaukakin mamaki da tarin al'ajabi,to ya akayi ita taje wurin harma take tunanin ƙara kusan tar wurin? wai meyake faruwa A cikin gidan nan? dole ta saka ido akan ɗakin nan dan ita ɗin cikakkiyar shaida ce A kan rashin gaskiyar dake tattare A cikin ɗakin,dole tasan waye mai shi da yadda akayi aka samar da shi,
Rahima ce ta dubeta cikin nutsuwa tace"yaya dai koda matsalane? Amma idan kinji kina san zuwa zaki iya zuwa amma Ni dai bazanje ba, da sauri Bintu tace a'a nima bazani ba muje kawai.
Cikin takunsa na ƙasaita yake tun karar ƙofar da zata sadashi da office ɗin sa wayar sa dake ringin ya ɗora A kunnen sa kana ya fara magana cikin ingantacciyar muryar sa me daɗin saurare, yanzu zan shiga office ɗin inaso katuran dukkan bayanan ta cikin e-mail ɗina zan duba!' abinda yace kenan ya katse kiran, A dai-dai lokacin kuma ya ƙara so office ɗin da sauri sakatariyar sa ta tashi ta buɗe masa ƙofar tare da cewa good morning sir!' kamar dai kullum bai saurareta ba yay shigewarsa,binsa tayi da ido kana tayi ƙwafa tare da cewa kai Dr Abdallah matarka ta shiga uku da nunƙufurci,( niko nace ke kibar irin su Abdallah idan suka tashi basu iya soyayya ba)
Bayan ya É—an yi wasu muhimman abubuwa sai kuma ya janyo laptop É—insa ya shiga duba baya nan da Aka turo masa,lumshe idanunsa yayi A yayinda ya gama duba duk bayanan da aka turo masa akan binciken Bintu.
Yarinyar nan kenan duk labarinta da ta bayar na ƙaryane? to me hakan yake nufi?gashi dai an binciko masa komai akanta sai dai Abu ɗaya ne basu samu ba, shine A salin inda suka fara zama,wato daga inda suka tawo,A yadda samu bayanan ance ba asan inda fafinta yayi ba kawai anwayi garine anga baya nan, daga nan ita ma Bintun ko kwana ɗaya bata ƙaraba ta gudu daga garin, hatta da gidan da suka zauna sai da aka ɗauka aka turo masa.
Jinjina kansa yayi cikin takaicin da ya tokare masa maƙoshi yace"dolene nasan koke wacece!' ƙofar office ɗin aka turo tare da yin sallama, A hankali ya buɗe idanunsa dake alumshe har sun canja kala saboda ɓacin rai,Dady jafar ne ya shigo yayin da yake ƙoƙarin zama yace"Abdallah banaso kasaka damuwa mai yawa A cikin ranka har yayi maka sanadin wata cutar,ka riga da kasani koda ba Ahlinka bane bincike yazaman maka dole tunda aikin kane, kariga da kasan cewa aikin likitacin nan kaje kayi shine musamman dan ɓatar da hankalin mutane akan ainihin aikin ka amma kuma kaga hakan yazame maka aikin lada ta ɓangarori biyu, ga ladan nemo lafiya ga na nemo gaskiya,dan haka Abdallah ina baka shawara kasaki jikinka da mutane gidan nan musamu abinda muke nema, ko ita wannan yarinyar Bintu kamata yayi ka ɗan sake mata ko yayane dan hakan shine zai bamu damar sanin abinda yake tare da ita!'
Ɗan furzar da iska yayi daga bakinsa kana yace" Dady bazan iyaba mukin dake cikin zuciya ta bazai bari ba ina jin ƙuna da gaske bazan iya sakar musu jiki ba Dady,ita kanta yarinyar mamakinta ƙara cushe min tunani yake!'Dady jafar ya dafa hannunsa kana yace"Abdallah karkayi saurin zargi dan bashi da kyau kafini sanin hakan,Ni inaji kawai kamar da abinda ya kawota gidan na daban bawai Abinda kake zargi ba,amma dai bincike shi zai nuna mana komai,bari na koma office ni!'Abdallah yace" nima fita zanyi Ni da Yahya akwai aikin da zamuje!'ok to ba damuwa sai mu fita tare kawai,
Gaba ɗaya Bintu ta saka kanta cikin tunanin yadda za ai ta san wace ce dije,zama tayi A gefan gadonta,tana mai cigaba da lalubo mafita, can kuma sai tunanin wannan matar ya faɗo mata, to ita kuma wannan ko wace?gashi tun ranar bata kuma ganin ta ba, kamar an mintsine ta haka ta miƙe da sauri,tana ganin cewa tunani daga zaune bazai yi mata ba gara ta fita ko Allah ya taimaketa taci karo da abinda zai warware mata gaddama,
Kai tsaye ta fita bayan ta sanar da inno zata ɗan zaga ta gaji da zaman guri ɗaya, har inno tana cewa ko duk kewar Ƙawarta Rahima ne ya dameta, saboda Rahiman sunje mai duguri ita da amna da Hajjah yayar amna ɗin ta haihu, murmushi kawai tayiwa inno ta fita daga ɗakin da cewa sai na dawo inno!'
tafe take tana saƙa da warwara,cikin ranta harma batasan ta bangaji mutum ba sai dai taji kalmar subhanallah,da sauri ta maida hankalinta kan matar,wani irin farin cikine ya rufeta yayin da ta haɗa ido da matar nan,wanda hakan sai da ya nuna A kan ƙawa tacciyat fuskarta,Dije ma murmushine ɗauke A kan fuskarta,cikin fara'a Bintu ta duƙa har ƙasa ta gaida Dije,cikin farin cikin girmamawar da Bintu tayi mata ta amsa tare da cewa sarkin kuka ina kukan? Bintu tayi ƙasa da kanta tana murmushi, yayin da take tunanin ga mafita Allah ya kawo mata,to' amma ta ina zata fara wannan tambaya ba tare da tayi mata wani mummunan zargi ba, Dije ta katse mata tunani da cewa ƴan mata meye sunanki? wata ɓoyayyiyar ajiyar zuciya Bintu ta sauke saboda jin tambayar da matar tayi mata,A hankali tace" sunana Bintu kuma Ni ƴar aikin inno ce,cike da gamsuwa Dije tace masha Allah duk da tariga tasan komai game da Bintun amma bata nuna mata haka ba, gabas ta duba ta dubi yamma kana cikin ta ka tsantsan dije ta miƙawa Bintun hannu kamar zasu gaisa amma sai Bintu taji ta bar mata wata yar takadda A cikin hannunta lokaci ɗaya Bintu ta fahimci Abinda Dije take nufi wato tana son isar mata da wani saƙo ne shiyasa tayi hakan,juyawa Dije tayi da niyar tafiya,Bintu tayi saurin cewa dan Allah mama meye sunanki? Sunana Dije! yayin da taci gaba da tafiya batare da ko waigeba,
Abin baƙaramin mamaki ya bawa Bintu ba, dama wannan ce Dijen da take ta nema? Ita kam wace irin me Sa'a ce da A duk lokacin da take neman Abu sai taga ashema abin yana kusa da ita ko tana tare dashi, lallai wannan shi ake kira da ƘUDURAR ALLAH.
Tana shiga ɗakinta kai tsaye toilet ta faɗa ta ɗaura alwalar azhar, bayan tayi sallah tayi addu'o'inta tare da ƙara miƙa godiyar ta ga sarki Allah jalla wa'azza mai iko buwayi gagara misali haƙiƙa tayi yaƙinin cewa Addu'ar Umminta da fafi da Baffa Jauro sune suke tasiri A kanta da kuma wadda take cigaba dayi dare da rana batare da ƙosawaba,kuma tayi yaƙinin Allah zai ci gaba da kareta da bata nasara A rayuwar ta har ta kai ga cin nasara A kan kyakkyawar manufarta,daga nan kiching ta nufa ta kama aikin shiryawa oganta Abdallah Abincinsa tanayi tana tasbihi, zuciyar ta na ƙara samun ƙarfi da nutsuwa.
A can ɓangaren Hajiya ladidi kuwa ta hana Aunty nafisa yawan zirga zirga A ɓangaren inno, duk dan kar A gano tsakaninta da Bintu dan A cewar Hajiya ladidi yawan tsanar da tayiwa Bintu ma zata iya sawa A saka musu ido tunda bata iya ɓoye tsanarta wa Bintu ba,yayin da kuma take jin daɗin yadda Bintu ta karbi aikin hankali kwance batare da ta ƙara nuna musu rashin amincewa ba yake matuƙar yi mata daɗi, har tana ganin kamar dan Bintun taje taga daula ne yasa ta canja ra'ayin ta,tana ganin indai hasashenta ya zama gaskiya to lallai nan gaba idan aikin Bintu yanayin kyau batare da wani kuskureba zata iya jawo ta cikin tafiyar, saboda ta fahimci yarinyar tana da matuƙar baiwa ta basira da kaifin tunani.
Sun daɗe A sashen Hajiya Babba, Bintu ta sake sosai da ita saboda yadda Hajiya ta sakar mata fuska ta nuna mata ƙauna ta zahiri da ba ɗini, haka da zasu tafi Hajiya ta Haɗa mata kayan amfani sosai kana sukayi sallama, Hajiya taji kewar yaran sosai.
Kewayawa sukeyi cikin Babban ESTATE ɗin, Raihana tana nuna mata kowane ɓangare da kuma me shi, sunzo dai dai ta wajen hanyar da zaka miƙa ka koma ta cikin wannan ɗakin, Bintu ta da kata, yayin da ta zubawa hanyar ido tana tuno abinda ya faru ranar tamkar A lokacin yake faruwa,sai da Raihana ta taɓata kana ta dawo haiyacinta tare da cewa Raihana gurin nan ya burgeni muje ta wajen mu zaga, naga kamar lambuneee......
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ¼*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
```Page 17 ```
A tsorace Rahima take duban Bintu cikin tabbatar mata da abinda zata faɗa, tace" ke Bintu ki rufa mana Asiri kin san kuwa babu wanda yake iya bi ta wajan nan!' Bintu cikin tsananin mamaki tace" to saboda me? kuma waye ya hana zuwa gurin?Raihana tace" babu wanda ya hana, hasalima ba A taɓa yiwa kowa gargaɗi da zuwa wajen ba, nima haka nataso nagani ba wanda yake iya zuwa, sai dai ban taɓa tunanin yin tawajen ba kuma bantaɓa ganin wani yaje ba ko zancen babu wanda ya taɓa yi balle musan dalili!' tunda ta fara magana Bintu take kallon bakinta cike da maɗaukakin mamaki da tarin al'ajabi,to ya akayi ita taje wurin harma take tunanin ƙara kusan tar wurin? wai meyake faruwa A cikin gidan nan? dole ta saka ido akan ɗakin nan dan ita ɗin cikakkiyar shaida ce A kan rashin gaskiyar dake tattare A cikin ɗakin,dole tasan waye mai shi da yadda akayi aka samar da shi,
Rahima ce ta dubeta cikin nutsuwa tace"yaya dai koda matsalane? Amma idan kinji kina san zuwa zaki iya zuwa amma Ni dai bazanje ba, da sauri Bintu tace a'a nima bazani ba muje kawai.
Cikin takunsa na ƙasaita yake tun karar ƙofar da zata sadashi da office ɗin sa wayar sa dake ringin ya ɗora A kunnen sa kana ya fara magana cikin ingantacciyar muryar sa me daɗin saurare, yanzu zan shiga office ɗin inaso katuran dukkan bayanan ta cikin e-mail ɗina zan duba!' abinda yace kenan ya katse kiran, A dai-dai lokacin kuma ya ƙara so office ɗin da sauri sakatariyar sa ta tashi ta buɗe masa ƙofar tare da cewa good morning sir!' kamar dai kullum bai saurareta ba yay shigewarsa,binsa tayi da ido kana tayi ƙwafa tare da cewa kai Dr Abdallah matarka ta shiga uku da nunƙufurci,( niko nace ke kibar irin su Abdallah idan suka tashi basu iya soyayya ba)
Bayan ya É—an yi wasu muhimman abubuwa sai kuma ya janyo laptop É—insa ya shiga duba baya nan da Aka turo masa,lumshe idanunsa yayi A yayinda ya gama duba duk bayanan da aka turo masa akan binciken Bintu.
Yarinyar nan kenan duk labarinta da ta bayar na ƙaryane? to me hakan yake nufi?gashi dai an binciko masa komai akanta sai dai Abu ɗaya ne basu samu ba, shine A salin inda suka fara zama,wato daga inda suka tawo,A yadda samu bayanan ance ba asan inda fafinta yayi ba kawai anwayi garine anga baya nan, daga nan ita ma Bintun ko kwana ɗaya bata ƙaraba ta gudu daga garin, hatta da gidan da suka zauna sai da aka ɗauka aka turo masa.
Jinjina kansa yayi cikin takaicin da ya tokare masa maƙoshi yace"dolene nasan koke wacece!' ƙofar office ɗin aka turo tare da yin sallama, A hankali ya buɗe idanunsa dake alumshe har sun canja kala saboda ɓacin rai,Dady jafar ne ya shigo yayin da yake ƙoƙarin zama yace"Abdallah banaso kasaka damuwa mai yawa A cikin ranka har yayi maka sanadin wata cutar,ka riga da kasani koda ba Ahlinka bane bincike yazaman maka dole tunda aikin kane, kariga da kasan cewa aikin likitacin nan kaje kayi shine musamman dan ɓatar da hankalin mutane akan ainihin aikin ka amma kuma kaga hakan yazame maka aikin lada ta ɓangarori biyu, ga ladan nemo lafiya ga na nemo gaskiya,dan haka Abdallah ina baka shawara kasaki jikinka da mutane gidan nan musamu abinda muke nema, ko ita wannan yarinyar Bintu kamata yayi ka ɗan sake mata ko yayane dan hakan shine zai bamu damar sanin abinda yake tare da ita!'
Ɗan furzar da iska yayi daga bakinsa kana yace" Dady bazan iyaba mukin dake cikin zuciya ta bazai bari ba ina jin ƙuna da gaske bazan iya sakar musu jiki ba Dady,ita kanta yarinyar mamakinta ƙara cushe min tunani yake!'Dady jafar ya dafa hannunsa kana yace"Abdallah karkayi saurin zargi dan bashi da kyau kafini sanin hakan,Ni inaji kawai kamar da abinda ya kawota gidan na daban bawai Abinda kake zargi ba,amma dai bincike shi zai nuna mana komai,bari na koma office ni!'Abdallah yace" nima fita zanyi Ni da Yahya akwai aikin da zamuje!'ok to ba damuwa sai mu fita tare kawai,
Gaba ɗaya Bintu ta saka kanta cikin tunanin yadda za ai ta san wace ce dije,zama tayi A gefan gadonta,tana mai cigaba da lalubo mafita, can kuma sai tunanin wannan matar ya faɗo mata, to ita kuma wannan ko wace?gashi tun ranar bata kuma ganin ta ba, kamar an mintsine ta haka ta miƙe da sauri,tana ganin cewa tunani daga zaune bazai yi mata ba gara ta fita ko Allah ya taimaketa taci karo da abinda zai warware mata gaddama,
Kai tsaye ta fita bayan ta sanar da inno zata ɗan zaga ta gaji da zaman guri ɗaya, har inno tana cewa ko duk kewar Ƙawarta Rahima ne ya dameta, saboda Rahiman sunje mai duguri ita da amna da Hajjah yayar amna ɗin ta haihu, murmushi kawai tayiwa inno ta fita daga ɗakin da cewa sai na dawo inno!'
tafe take tana saƙa da warwara,cikin ranta harma batasan ta bangaji mutum ba sai dai taji kalmar subhanallah,da sauri ta maida hankalinta kan matar,wani irin farin cikine ya rufeta yayin da ta haɗa ido da matar nan,wanda hakan sai da ya nuna A kan ƙawa tacciyat fuskarta,Dije ma murmushine ɗauke A kan fuskarta,cikin fara'a Bintu ta duƙa har ƙasa ta gaida Dije,cikin farin cikin girmamawar da Bintu tayi mata ta amsa tare da cewa sarkin kuka ina kukan? Bintu tayi ƙasa da kanta tana murmushi, yayin da take tunanin ga mafita Allah ya kawo mata,to' amma ta ina zata fara wannan tambaya ba tare da tayi mata wani mummunan zargi ba, Dije ta katse mata tunani da cewa ƴan mata meye sunanki? wata ɓoyayyiyar ajiyar zuciya Bintu ta sauke saboda jin tambayar da matar tayi mata,A hankali tace" sunana Bintu kuma Ni ƴar aikin inno ce,cike da gamsuwa Dije tace masha Allah duk da tariga tasan komai game da Bintun amma bata nuna mata haka ba, gabas ta duba ta dubi yamma kana cikin ta ka tsantsan dije ta miƙawa Bintun hannu kamar zasu gaisa amma sai Bintu taji ta bar mata wata yar takadda A cikin hannunta lokaci ɗaya Bintu ta fahimci Abinda Dije take nufi wato tana son isar mata da wani saƙo ne shiyasa tayi hakan,juyawa Dije tayi da niyar tafiya,Bintu tayi saurin cewa dan Allah mama meye sunanki? Sunana Dije! yayin da taci gaba da tafiya batare da ko waigeba,
Abin baƙaramin mamaki ya bawa Bintu ba, dama wannan ce Dijen da take ta nema? Ita kam wace irin me Sa'a ce da A duk lokacin da take neman Abu sai taga ashema abin yana kusa da ita ko tana tare dashi, lallai wannan shi ake kira da ƘUDURAR ALLAH.
Tana shiga ɗakinta kai tsaye toilet ta faɗa ta ɗaura alwalar azhar, bayan tayi sallah tayi addu'o'inta tare da ƙara miƙa godiyar ta ga sarki Allah jalla wa'azza mai iko buwayi gagara misali haƙiƙa tayi yaƙinin cewa Addu'ar Umminta da fafi da Baffa Jauro sune suke tasiri A kanta da kuma wadda take cigaba dayi dare da rana batare da ƙosawaba,kuma tayi yaƙinin Allah zai ci gaba da kareta da bata nasara A rayuwar ta har ta kai ga cin nasara A kan kyakkyawar manufarta,daga nan kiching ta nufa ta kama aikin shiryawa oganta Abdallah Abincinsa tanayi tana tasbihi, zuciyar ta na ƙara samun ƙarfi da nutsuwa.
A can ɓangaren Hajiya ladidi kuwa ta hana Aunty nafisa yawan zirga zirga A ɓangaren inno, duk dan kar A gano tsakaninta da Bintu dan A cewar Hajiya ladidi yawan tsanar da tayiwa Bintu ma zata iya sawa A saka musu ido tunda bata iya ɓoye tsanarta wa Bintu ba,yayin da kuma take jin daɗin yadda Bintu ta karbi aikin hankali kwance batare da ta ƙara nuna musu rashin amincewa ba yake matuƙar yi mata daɗi, har tana ganin kamar dan Bintun taje taga daula ne yasa ta canja ra'ayin ta,tana ganin indai hasashenta ya zama gaskiya to lallai nan gaba idan aikin Bintu yanayin kyau batare da wani kuskureba zata iya jawo ta cikin tafiyar, saboda ta fahimci yarinyar tana da matuƙar baiwa ta basira da kaifin tunani.