Sashe 41
Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Rahima ta zubawa Hajiya Babba ido tana sauraran labarin da take bata wanda take jinsa kamar alamara, wai Bintu da Ya Abdallah aure, kai ita zata iya cewa ma ta daɗe bata ji zancen da yayi mata daɗi kamar wannan ba,tace"Hajiya Babba wai wane irin ƙauna kikewa Bintu ne?kai tsaye tace"mata irin wannan ƙaunar da nakewa jikokina mafi soyuwa A zuciyata!'dariya Rahima tayi tare da cewa, gaskiya keda Inno ban san wanda yafi wani ƙaunar Bintu ba,sai dai kuma dukkan ku Alhaji Baba yafiku san Bintu!'hararar wasa tayi mata, tare da cewa ai shi ta huɗu yake nema ba dole yafi mu santa ba,amma mu kuma kishiyoyine kar ki manta,Rahima tace"lallai kam Hajjah ce kawai take kishi da Bintu dan dama duk tafiku kishi!'Hajiya Babba ta riƙe baki tana kallon Rahima cike da mamaki na gaske wai har ta fahimci Hajjah ta fisu kishi kai yaran yanzu sai abarsu.
Ji tayi kawai an rufeta da duka ta ko'ina ta kasa kare kanta saboda shammatar da sukayi mata,Taufiƙa cewa take wallahi ko za'a kashe Ni sai na huce baƙin ciki na najiya akanki wannan somin taɓine na bijirewa magana ta da kikayi, sauran mataki yana gaba saikinyi namar zuwanki cikin ahlin mu saina gurgunta rayuwarki kin zama abin tausayi a idanun masu imani!'kuka take sosai Bintu dan wallahi tana buguwa,da gudu inno ta shiga kiching ɗin tare da salallami tace"amma wallahi yaran nan baku da imani uban me tayi muku zaku kashe ta?anya kuwa wannan mummunar ɗabi'ar da kuka ɗauka zata kaiku ga cin nasarar rayuwa? gaskiya ina tausaya muku nan gaba domin da hannun ku zaku shuke abinda kuka girba!'ta janyo hannun Bintu suka fita daga kiching ɗin,tana mai jaddada musu Allah saiya sakawa Bintun,ko ajikinsu dan wata uwar harara da suke ta bankawa Bintun kamar idanunsu zasu faɗo..
Bintu fa ta shiga cikin matsatsi da takurar Anty Nafisa,duk inda tayi motsi sai taji ƙarar saƙonta ya shigo mata har wata ƴar rama tayi, kana ganinta kasan tana cikin damuwa ga damuwar su Taufiƙa dan ma Rahima tana taka musu birki to yanzu Rahiman ma ba ƙyaleta sukai ba.
Sunkuye take tana saka zanin gado a danƙareren gadon Oga Abdallah,jitayi wayarta na zumm zumm da sauri ta ɗauko ta buɗe saƙon Anty Nafisa ne kamar yadda ta canja salo har da barazana yanzu take aikomata, zubawa wayar ido tayi tamkar A cikinsa zata samo mafita,ya jima tsaye A bayanta duk da bai samu ganin saƙon ba amma yaci nasarar ganin sunan Anty Nafisa saman saƙon,ji tayi kawai anzare wayar daga hannunta,wata irin zabura tayi ta juya,tuni idanunta suka shige cikin nasa take kuwa jikinta yashiga rawa tamkar wadda ake kaɗawa ganga, idanunta har sun kawo ruwan hawaye tunda dama A kusa take,cikin rawar murya tace"dan Allah kabani wayana!'ko kallon inda take baiyi ba yaci gaba da sabgar gaban sa takalmin sa na motsa jiki ya shiga kuncewa, Bintu kuwa magiya har da kuka amma yayi funfurus,ƙarshe ma banɗaki ya shiga ya barta da tashin hankalin ta,ƙarshen zance ma dai tana kallo yasa wayar gaban aljihunsa ya fita da ita batare da ya kula ta ba,zama tayi taci kukanta kana ta koma ɗakinta.
Dady jafar yace"Abdallah ya kamata mu fara zurfafa binciken mu akan Dadinku Mansur,dan gaskiya al'amarinsa akwai ayar tambaya,ko ya ka gani?ɗan kashin giɗa yayi jikin haɗaɗɗiyar kujerar sa kana cikin miskilar maganar sa yace"Dady ta manyan muke yanzu, ba tashi ba,nuna masa wayar da ya karɓa A hannun Bintu yayi tare da cewa wannan wayar zata temaka mana wajen samun abinda muke san sani, duk da ban binciki wayar ba me wayar nake san bincika domin iya waya baza ta gamsar damu komai ba!'Dady jafar yace"Abdallah dole kacire duk wani tunani A ranka game da yarinyar nan ka sako mana ita cikin al'amarin nan,kaga yanzu kana da iko A kan ta tunda ta kusa zama matarka nan da ƴan kwanaki!'ɗan lumshe idanunsa yayi kana ya fara da cewa, Dady nifa yarinyar nan zan aureta ne kawai saboda kariya ga haɗarin da nake san sakota aciki dan haka da komai ya dai-daita nan da wani ɗan lokaci zan rabu da ita ta samu mijin da yakeso ta aura idan ma Sayyid ɗin ne Ni zan tsaya mata ta aureshi tunda kaga saboda tana sonsa har Alhaji Baba takewa gaddama shine kuma zata haɗa shirinta dani ya ɗan ja tsuka tare da cewa dan haka ka daina yimin batun ta maras kunya kawai!'Dady jafar murmushi yayi tare da cewa to shike nan idan lokacin yayi ko Ni da kaina zan ne mawa Sayyid aurenta dan shine halaccin da zamu iya yimata bayan ta tai maka mana!'miƙewa yayi yana tattaro takardunsa ko yanzun ma zaka iya bashi ita!'daga haka ya fita ya bar Dadin A cikin office ɗin, murmushi Dady jafar yayi sosai tare da cewa Allah ya nunamin wannan rana.
Wasan ɓuya sukeyi domin ta riga tasan yagama bincika wayarta hankalin ta tashe yake tasan kashin ta ya bushe a wajen Oga Abdallah,shiyasa duk hanyar da tasan zasu haɗu taƙi bi acikin kwana guda,shi kansa ya fahimci haka amma ya riga ya gama shirin sa na kamata A hannu duk wannan gudun da takeyi sai dai idan bai shirya kamata ba.
Bintuna ki kwantar da hankalin ki ki natare da mai taimakon tsanin ki kuma mai tallafar rayuwarki,kuma muna nan araye Ni da mamanki gaskiya ce kawai zata baiyana mu ki dage da addu'a al'amarin gidan nan bai fi ƙarfin ƙudurar Allah ba,dan haka ina mai sanar dake ki cire tsoro ki tunkari matsalar ki,babu wanda ya isa yaga bayan rayuwarki sai lokacin ki yayi, wannan dai dayake taimaka miki cikin dukkanin matsalar da kika shiga shi zai cigaba da taimakon ki tare da taimakon Allah buwayi gagara misali,akwai ƙalubale a gaban ki Bintu karki wasa da addu'a Allah ya cigaba da taimakonki ya kuma kareki daga sharrin su!'zufa ce ta shiga keto mata buɗe idanunta tayi daga mafarkin da tayi da fafin ta tare da ambatan sunan Allah,a hankali maganganun da fafin yayi mata suka dunga dawowa cikin kunnuwanta,to me fafi yake nufi shine wa?waye wanda yake taimakonta?miƙewa tayi daga saman gadon cikin zurfafa tunani, Oga Abdallah kenan fafi yake nufi shine wanda yake yawan gaya mata zai zo dan tallafa mata?to ya akayi suka kasan ce guri ɗaya? Ƙudurar Allah kenan,duk abinda nake nema sai ya kasan ce yana tare dani kai masha Allah da ƘUDURARSA da kuma dogara dashi tabbas wanda ya maida lamuransa ga Allah zai ta ganin dai dai arayuwarsa, Allah kaine abin godiya,sai dai kuma tunani da ya sare mata gwiwa bai wuce wayar ta dake hannun sa ba,idan yaga saƙonnin dake ciki zai ɗora mata mummunan zargi,ko dai gaya masa zatayi?to kuma idan yaƙi yadda fa?tashi tayi kawai ta ɗauro alwala dan miƙa kukanta ga jallah wa'azza.
Jinta tayi sawai saboda kusan kwana da tayi tana miƙa kukanta gurin Allah assamadu,shi yasa taji ƙuncin dake ranta duk babu ta tattara komai ta barwa Allah tasan zai kawo mata mafita mai kyau arayuwarta,cikin ƙanƙanin lokaci ta gama shiryawa ogan nata kayan karin kumallo wainar masa tayi masa wadda tayi matuƙar kyau da laushi sai kunun tsamiya da suyar chips da ƙwai ta haɗa masa ruwan liptom,kana taje ta shirya komai cikin nutsuwa, cikin ɗakin ta shiga ta fara da wanke toilet,sannan ta gyara ɗakin kan kace meye ya ɗauki ƙamshi da haske tsaftar Bintu ta musamman ce saboda bata da ƙwuya ko mai a nutse take yinsa shi yasa zaka ga komai tsaf bata barin datti ko ta allura ce,
shiyasa duk ƙaƙalen Abdallah bai taɓa ganin kuskure a tsaftar Bintu ba,ya riga ya yadda da ita ta wannan ɓangaren ya bata maki ɗari bisa ɗari,ɗan dube dube ta fara so take ta gani ko zata ga inda ya ajiye wayar ta, har su ƙarƙashin gado sai da ta duba duk da gyaran ta har nan bata bari ba,me kike nema? taji muryarsa daga bayanta da sauri ta ɗago tana rarraba manyan idanuwan ta masu tamkar zaiba, tashi tayi tana son barin ɗakin,jingina yayi da ƙofar alamun dai ba zai bata hanya ba,tura ɗan ƙaramin bakinta tayi tare da cewa sharewa nayi!'ɗan ƙara girman idanunsa yayi akan ta batare da yace mata komai ba sannan kuma bai bata hanya ba,ɗan matsawa tayi daf dashi tace" zan tafi inno tana jirana!'saurin sunkuyar da kanta tayi saboda kaifin idanunsa,gaba ɗaya jikinta ya fara rawa saboda kusancin su yanayin da take shiga da zarar sun fara musayar numfashi shi yake ƙara yawa har wani sanyi takeji can cikin ƙashi da ɓargonta, da ta rasa mafitar ta tatserewa shu'uman idanunsa kawai sai ta fara sana ar tata,ɗan ɗage gira yayi yana ƙara zurfafa duban sa akanta,kana kuma ya taɓe bakinsa tare da cewa ke gyare sarkin kuka,tambayar ki nayi fa,cikin sangar tacciyar murya tace"to wuce wa zanyi!'bata hanya yayi batare da ya kuma tanka mata ba,da gudu ta fita,batare da ko waiwaye ba,jinjina kansa yayi tare da cewa lokacin kamaki ne baiyi ba.
Ji tayi kawai an rufeta da duka ta ko'ina ta kasa kare kanta saboda shammatar da sukayi mata,Taufiƙa cewa take wallahi ko za'a kashe Ni sai na huce baƙin ciki na najiya akanki wannan somin taɓine na bijirewa magana ta da kikayi, sauran mataki yana gaba saikinyi namar zuwanki cikin ahlin mu saina gurgunta rayuwarki kin zama abin tausayi a idanun masu imani!'kuka take sosai Bintu dan wallahi tana buguwa,da gudu inno ta shiga kiching ɗin tare da salallami tace"amma wallahi yaran nan baku da imani uban me tayi muku zaku kashe ta?anya kuwa wannan mummunar ɗabi'ar da kuka ɗauka zata kaiku ga cin nasarar rayuwa? gaskiya ina tausaya muku nan gaba domin da hannun ku zaku shuke abinda kuka girba!'ta janyo hannun Bintu suka fita daga kiching ɗin,tana mai jaddada musu Allah saiya sakawa Bintun,ko ajikinsu dan wata uwar harara da suke ta bankawa Bintun kamar idanunsu zasu faɗo..
Bintu fa ta shiga cikin matsatsi da takurar Anty Nafisa,duk inda tayi motsi sai taji ƙarar saƙonta ya shigo mata har wata ƴar rama tayi, kana ganinta kasan tana cikin damuwa ga damuwar su Taufiƙa dan ma Rahima tana taka musu birki to yanzu Rahiman ma ba ƙyaleta sukai ba.
Sunkuye take tana saka zanin gado a danƙareren gadon Oga Abdallah,jitayi wayarta na zumm zumm da sauri ta ɗauko ta buɗe saƙon Anty Nafisa ne kamar yadda ta canja salo har da barazana yanzu take aikomata, zubawa wayar ido tayi tamkar A cikinsa zata samo mafita,ya jima tsaye A bayanta duk da bai samu ganin saƙon ba amma yaci nasarar ganin sunan Anty Nafisa saman saƙon,ji tayi kawai anzare wayar daga hannunta,wata irin zabura tayi ta juya,tuni idanunta suka shige cikin nasa take kuwa jikinta yashiga rawa tamkar wadda ake kaɗawa ganga, idanunta har sun kawo ruwan hawaye tunda dama A kusa take,cikin rawar murya tace"dan Allah kabani wayana!'ko kallon inda take baiyi ba yaci gaba da sabgar gaban sa takalmin sa na motsa jiki ya shiga kuncewa, Bintu kuwa magiya har da kuka amma yayi funfurus,ƙarshe ma banɗaki ya shiga ya barta da tashin hankalin ta,ƙarshen zance ma dai tana kallo yasa wayar gaban aljihunsa ya fita da ita batare da ya kula ta ba,zama tayi taci kukanta kana ta koma ɗakinta.
Dady jafar yace"Abdallah ya kamata mu fara zurfafa binciken mu akan Dadinku Mansur,dan gaskiya al'amarinsa akwai ayar tambaya,ko ya ka gani?ɗan kashin giɗa yayi jikin haɗaɗɗiyar kujerar sa kana cikin miskilar maganar sa yace"Dady ta manyan muke yanzu, ba tashi ba,nuna masa wayar da ya karɓa A hannun Bintu yayi tare da cewa wannan wayar zata temaka mana wajen samun abinda muke san sani, duk da ban binciki wayar ba me wayar nake san bincika domin iya waya baza ta gamsar damu komai ba!'Dady jafar yace"Abdallah dole kacire duk wani tunani A ranka game da yarinyar nan ka sako mana ita cikin al'amarin nan,kaga yanzu kana da iko A kan ta tunda ta kusa zama matarka nan da ƴan kwanaki!'ɗan lumshe idanunsa yayi kana ya fara da cewa, Dady nifa yarinyar nan zan aureta ne kawai saboda kariya ga haɗarin da nake san sakota aciki dan haka da komai ya dai-daita nan da wani ɗan lokaci zan rabu da ita ta samu mijin da yakeso ta aura idan ma Sayyid ɗin ne Ni zan tsaya mata ta aureshi tunda kaga saboda tana sonsa har Alhaji Baba takewa gaddama shine kuma zata haɗa shirinta dani ya ɗan ja tsuka tare da cewa dan haka ka daina yimin batun ta maras kunya kawai!'Dady jafar murmushi yayi tare da cewa to shike nan idan lokacin yayi ko Ni da kaina zan ne mawa Sayyid aurenta dan shine halaccin da zamu iya yimata bayan ta tai maka mana!'miƙewa yayi yana tattaro takardunsa ko yanzun ma zaka iya bashi ita!'daga haka ya fita ya bar Dadin A cikin office ɗin, murmushi Dady jafar yayi sosai tare da cewa Allah ya nunamin wannan rana.
Wasan ɓuya sukeyi domin ta riga tasan yagama bincika wayarta hankalin ta tashe yake tasan kashin ta ya bushe a wajen Oga Abdallah,shiyasa duk hanyar da tasan zasu haɗu taƙi bi acikin kwana guda,shi kansa ya fahimci haka amma ya riga ya gama shirin sa na kamata A hannu duk wannan gudun da takeyi sai dai idan bai shirya kamata ba.
Bintuna ki kwantar da hankalin ki ki natare da mai taimakon tsanin ki kuma mai tallafar rayuwarki,kuma muna nan araye Ni da mamanki gaskiya ce kawai zata baiyana mu ki dage da addu'a al'amarin gidan nan bai fi ƙarfin ƙudurar Allah ba,dan haka ina mai sanar dake ki cire tsoro ki tunkari matsalar ki,babu wanda ya isa yaga bayan rayuwarki sai lokacin ki yayi, wannan dai dayake taimaka miki cikin dukkanin matsalar da kika shiga shi zai cigaba da taimakon ki tare da taimakon Allah buwayi gagara misali,akwai ƙalubale a gaban ki Bintu karki wasa da addu'a Allah ya cigaba da taimakonki ya kuma kareki daga sharrin su!'zufa ce ta shiga keto mata buɗe idanunta tayi daga mafarkin da tayi da fafin ta tare da ambatan sunan Allah,a hankali maganganun da fafin yayi mata suka dunga dawowa cikin kunnuwanta,to me fafi yake nufi shine wa?waye wanda yake taimakonta?miƙewa tayi daga saman gadon cikin zurfafa tunani, Oga Abdallah kenan fafi yake nufi shine wanda yake yawan gaya mata zai zo dan tallafa mata?to ya akayi suka kasan ce guri ɗaya? Ƙudurar Allah kenan,duk abinda nake nema sai ya kasan ce yana tare dani kai masha Allah da ƘUDURARSA da kuma dogara dashi tabbas wanda ya maida lamuransa ga Allah zai ta ganin dai dai arayuwarsa, Allah kaine abin godiya,sai dai kuma tunani da ya sare mata gwiwa bai wuce wayar ta dake hannun sa ba,idan yaga saƙonnin dake ciki zai ɗora mata mummunan zargi,ko dai gaya masa zatayi?to kuma idan yaƙi yadda fa?tashi tayi kawai ta ɗauro alwala dan miƙa kukanta ga jallah wa'azza.
Jinta tayi sawai saboda kusan kwana da tayi tana miƙa kukanta gurin Allah assamadu,shi yasa taji ƙuncin dake ranta duk babu ta tattara komai ta barwa Allah tasan zai kawo mata mafita mai kyau arayuwarta,cikin ƙanƙanin lokaci ta gama shiryawa ogan nata kayan karin kumallo wainar masa tayi masa wadda tayi matuƙar kyau da laushi sai kunun tsamiya da suyar chips da ƙwai ta haɗa masa ruwan liptom,kana taje ta shirya komai cikin nutsuwa, cikin ɗakin ta shiga ta fara da wanke toilet,sannan ta gyara ɗakin kan kace meye ya ɗauki ƙamshi da haske tsaftar Bintu ta musamman ce saboda bata da ƙwuya ko mai a nutse take yinsa shi yasa zaka ga komai tsaf bata barin datti ko ta allura ce,
shiyasa duk ƙaƙalen Abdallah bai taɓa ganin kuskure a tsaftar Bintu ba,ya riga ya yadda da ita ta wannan ɓangaren ya bata maki ɗari bisa ɗari,ɗan dube dube ta fara so take ta gani ko zata ga inda ya ajiye wayar ta, har su ƙarƙashin gado sai da ta duba duk da gyaran ta har nan bata bari ba,me kike nema? taji muryarsa daga bayanta da sauri ta ɗago tana rarraba manyan idanuwan ta masu tamkar zaiba, tashi tayi tana son barin ɗakin,jingina yayi da ƙofar alamun dai ba zai bata hanya ba,tura ɗan ƙaramin bakinta tayi tare da cewa sharewa nayi!'ɗan ƙara girman idanunsa yayi akan ta batare da yace mata komai ba sannan kuma bai bata hanya ba,ɗan matsawa tayi daf dashi tace" zan tafi inno tana jirana!'saurin sunkuyar da kanta tayi saboda kaifin idanunsa,gaba ɗaya jikinta ya fara rawa saboda kusancin su yanayin da take shiga da zarar sun fara musayar numfashi shi yake ƙara yawa har wani sanyi takeji can cikin ƙashi da ɓargonta, da ta rasa mafitar ta tatserewa shu'uman idanunsa kawai sai ta fara sana ar tata,ɗan ɗage gira yayi yana ƙara zurfafa duban sa akanta,kana kuma ya taɓe bakinsa tare da cewa ke gyare sarkin kuka,tambayar ki nayi fa,cikin sangar tacciyar murya tace"to wuce wa zanyi!'bata hanya yayi batare da ya kuma tanka mata ba,da gudu ta fita,batare da ko waiwaye ba,jinjina kansa yayi tare da cewa lokacin kamaki ne baiyi ba.