Sashe 55
Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
A wannan halin ya shigo ya sameta wanda bata san shigowar sa ba sai sallamar sa da taji akanta, wata irin zabura tayi tana neman gurin tsira daga tarkon da Abdallah ya ɗana mata,yana tsaye hannun sa soke cikin aljihun sa yana kallon yadda take ta dubi-dubi dan neman mafaka da ta rasa mafakar kawai sai ta fara tsiyayar da hawaye dan a hakikanin gaskiya tana matuƙar jin kunyar haɗa ido da Oga Abdallah,zama yayi kusa da ita wanda hakan ya kuma jefa zuciyar ta cikin wani irin bugu da fargaba,kawai sai ta sukuyar da kanta tana ta faman jajjan towel ɗin dake jikinta dan ya ƙara rufe mata jikin ta,cikin muryar sa da take fita ɗaɗɗaya da yanayin sa na muskilin namiji me tsananin aji da kwarjini yace"a karo na biyu zan kuma tambayarki idan kuma kika kawo min wasa sai na zaneki anan gurin tare da allura mai zafi guda biyar!'ɗagowa tayi ta ɗan saci kallon sa sai taga ashe idanunsa suna kanta,maida kanta tayi tare da cewa zan faɗa maka duk abinda ka tambayeni!'wai kuma sai yaji wani abu A ransa ganin yadda tayi magana cikin rauni, ya rasa me yasa yake da rauni da yawa akan yarinyar nan, cikin tausasa murya yace"ki nutsu ki cire tsoron ko mai ki bani amsa yadda ya kamata!'jin jina masa kai tayi tare da cewa to cikin rawar muryarta,ɗan gyara zaman sa yayi kana yace"wane irin aiki Nafisa ta sakaki kiyi mata san nan wanene mutumin da kike zargi suna aiki da Hajiya ladidi?da sauri ta dube shi cike da mamakin yadda akayi yasan abin da take ɓoye masa,ɗan ɗage mata gira yayi ganin yadda take masa kallon mamaki, sunkuyar da kanta tayi cikin jin kunya tare da cewa,Hajiya ladidi bata buɗe min zan can ba kawai tayi suɓutar bakine shiyasa nayi tunanin bayan Anty Nafisa a kwai wanda suke shirya wani al amarin tare, amma kuma nayi mamakin yadda akayi suke munafuntar junansu ita da Anty Nafisa,daga baya kuma nayi tunanin yadda zuciyoyin su suke babu abinda bazasu iya aikatawa junansu ba indai akan burukan sune,cikin ƙara yin ƙasa da murya ta fara bashi labarin yadda sukayi da Anty Nafisa tun daga farko har ƙarshe,cikin tsananin mamaki yake duban Bintun shi dama bai san komai a kan Nafisa ba kawai dai cikin salon aiki ne ya bigi cikin Bintun dan kar tayi tunanin ɓoye masa ko bashi labarin ƙarya,tashi yayi ya shiga zaga ɗakin hannun sa a dunƙule cikin juna kan sa ya kulle to amma idan hakane anya kuwa babu hannun Nafisa a saka masa guba?to kuma ta yaya zata kashe shi bayan cewa tayi sai Bintu taƙi yadda ko kuma ta gayawa wani sirrinta san nan zata aikata mata wani mummunan abu?kuma idan yayi la akari da yadda ita ma ta nunawa Bintu tana san sanin wanda yasa ta aikata wannan aiki sai kuma tunanin sa ya juya,kai wannan al'amari da matuƙar ɗaure kai yake dole ne ya bin ciki wanda ya saka masa gubar nan dan yana da yaƙini cewa shima zai zama jigo cikin binciken su zai ƙara faɗaɗa musu hanyar bincike cikin sauki tare da samun nasara,komawa yayi ya zauna inda ya tashi tare da duban Bintu da itama take ta binsa da kallo,yace"kin san me nake so dake? Bintu ta girgiza kanta ya ɗora mata da cewa inaso ki rage tsoro dan hakan shine zai kawo mana nasara cikin aikin mu,cikin sanyin murya tace"babu abinda zan iya taimaka maka dashi akan kyakykyawar niyarka ta binciko ruɓaɓɓun ƙwayayen dake cikin ahlinku?kallon bakinta yake dan baya iya jurar kallon ƙwayar idanunta,yace"kina ganin zaki iya taimaka mana?zan taimaka maka saboda raina fansane ga waɗanda aka cuta acikin ahlin nan!'a yanzun kallon idanun ta yake kai tsaye saboda yadda yaga wutar fansa na ci daga cikin kyawawan idanun ta yayin da suka cika da ƙwallar da take dauriya dan kar ta zubo saboda tun daga yanzu take san zama jaruma me yaƙi afilin daga,tunda yanzu ta samu tallafin gwarzan miji jarumi mara tsoro,dan haka ita ma ya zama dole ta cire duk wata fargaba domin fuskantar gagarumin yaƙin dake gabansu, cikin tausasa harshe yace"kin tabbata dai kin karɓi aikin da Nafisa ta baki ko?jinjina masa kai tayi,yace da kyau kin fara naki aikin tun daga yanzu da wannan ƙudurin nata zamu mamayeta,san nan ina so lallai zamu haɗu da Dije amma ba yanzu ba saboda haɗuwa da ita sai an saka lura da taka tsan tsan,ita kuma Hajiya ladidi cikin wayo zamu sa ta faɗi wanda suke tare dashi!'Bintu tace"oga a kwai tunanin da nayi akan mu amalar sirri tsakanin Hajiya ladidi da Anty Nafisa,taci gaba da cewa me zai hana tunda dukkan su basa son ɗayan su yasan sirrin ɗayansu mu kuma mubi wannan hanyar dan haɗa su faɗa, wanda Ni aganina zamu iya samun wasu muhimman sirrika ta hanyar tunzura zuciyoyin su,wanda zamuyi hakan ne cikin dabara batare da sun san daga inda abin ya fito ba!'duban ta yake cike da mamakin basirar ta tana da kaifin tunani tabbas ba karamin ci gaba zata kawo cikin wannan tafiyar ba,amma haka nan yake jin tsoron zaƙewarta cikin lamarin yana gudun kar wani abu ya yasame ta saboda ita yarinyace mai cike da ƙuriciya,hannu yasa ya shafa fuskarsa tare da jan dogon numfashi kana yace kinyi tunani mai kyau amma bake zakiyi wannan aikin ba!saboda me to wazaiyi?,ta faɗa duk alokaci ɗaya,haɗe fuskarsa ya kumayi tare da cewa kar su cutar dake kuma wadda ta san kan aiki zan saka tayi!'sakato tayi tana kallonsa yayin da ya tashi yana ƙoƙarin shiga toilet,har ya shige bata daina mamakin sa ba ita dai a iya sanin ta da shi bai cika bawa abu muhimmanci ba ballantana bada amsa amma yau shine ya zauna yake doguwar magana da ita har da su bata amsa kai harda ma ƙarin iyayi wai kar acutar da ita,ko da ike ai ɓangaren aikin sa aka taɓa wanda shi dama idan kaga dogon zan cen sa to akan aikin sane, taɓe baki tayi tana mai tuna ranar da tasan aikin da yake bayan aikin asibintin da tasan shine aikin sa, tasha mamaki lokacin da taga ID card ɗin sa tare da cikakken sunansa shi yasa abin bai dame ta ba tunda dama ta riga ta sani,ta shi tayi ta ɗauki ƙaramin tawul ɗin ta ta rufa kana ta fita daga ɓangaren.
Wata irin mahaukaciyar dariya ya bushe da ita, tare da cewa lallai yaro bai san wuta ba sai ya taka yan zu aka fara wasan su atunanin su zasu iya rusani?tabbas kunyi gan yancin fara yaƙata domin bazaku taɓa cin nasara akaina ba,haƙiƙa naji daɗin wannan himma taku domin ta haka ne zan cimma burina dole kune ginshiƙin burina daku zanyi garkuwa domin sanin inda wannan ɓoyayyan sirri yake wanda ake tunanin bamu san dashi ba,hhhh ya kuma bushewa da wata ibilishiyar dariya tare da cewa Ni da nake da Jack ga kuma shugaba ai babu abinda zai gagareni samu adunayar nan (wa iya zubilla Allah ka shirya waɗanda suka ɓata dan Alfarmar shugaba)duk ta inda kuka ɓullo sai na ɓullo muku, Abubakar dole ka buɗe baki kasanar dani inda sirrin nan yake a ina aka ɓoyeshi?lokacin faɗarka yayi saboda fansar rayuwar yaronka da ƴar ɗan uwanka, lokacin ta shinka ya kusa saboda biyan buƙatata da nasamu kuma shikenan zan ƙara saka domin nasamu abinda ya hanani kasheka,ɗan taɓa kan kyakkyawan mutumin da yake a daskare kamar ƙanƙara yayi,sai ga wani irin farin hayaƙi na fitowa daga jikin sa idanun sa ne kawai keyin motsi sai bugawar zuciyar da ita ke nuni da har yanzu yana raye, zagaye shi ya shiga yi yana tafa hannayen sa ya cigaba da cewa babu wanda zai mallaki wannan abu idan har ina numfashi,duk masu bulayi da neman inda kake kallon su kawai nakeyi waɗan can mutanen da wani shu'umin ya sace su babu abinda zasu karan kawai dai ina ƙoƙarin rage yawan sune saboda zasu iya zama bara zana cikin samun farin cikina, Laila da ɗan uwanki duk ranar da na haɗa ido da wanda ya ɗaukeku gaba ɗayan ku zan haɗa na kashe bana so ki bayyana cikin ahlin ALHAJI BALARABE dake da shegiyar yariyar ki,duk da cewa ita ta bayyana amma tunda babu wanda yasan da labarin auren uwarta babu ta yadda za ayi ajingina ta da ahlin ESTATE ,kafun suma lokacinsu ya ƙara so ita da gwarzan mijinta,dariya yakeyi cike da farin cikin yana samun duk yadda yake so, tsarin sa yana tafiya dai dai da yadda ya buƙata,wani farin cikin ma sai nan gaba.
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ¼*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
```Page 35 ```
Wata irin mahaukaciyar dariya ya bushe da ita, tare da cewa lallai yaro bai san wuta ba sai ya taka yan zu aka fara wasan su atunanin su zasu iya rusani?tabbas kunyi gan yancin fara yaƙata domin bazaku taɓa cin nasara akaina ba,haƙiƙa naji daɗin wannan himma taku domin ta haka ne zan cimma burina dole kune ginshiƙin burina daku zanyi garkuwa domin sanin inda wannan ɓoyayyan sirri yake wanda ake tunanin bamu san dashi ba,hhhh ya kuma bushewa da wata ibilishiyar dariya tare da cewa Ni da nake da Jack ga kuma shugaba ai babu abinda zai gagareni samu adunayar nan (wa iya zubilla Allah ka shirya waɗanda suka ɓata dan Alfarmar shugaba)duk ta inda kuka ɓullo sai na ɓullo muku, Abubakar dole ka buɗe baki kasanar dani inda sirrin nan yake a ina aka ɓoyeshi?lokacin faɗarka yayi saboda fansar rayuwar yaronka da ƴar ɗan uwanka, lokacin ta shinka ya kusa saboda biyan buƙatata da nasamu kuma shikenan zan ƙara saka domin nasamu abinda ya hanani kasheka,ɗan taɓa kan kyakkyawan mutumin da yake a daskare kamar ƙanƙara yayi,sai ga wani irin farin hayaƙi na fitowa daga jikin sa idanun sa ne kawai keyin motsi sai bugawar zuciyar da ita ke nuni da har yanzu yana raye, zagaye shi ya shiga yi yana tafa hannayen sa ya cigaba da cewa babu wanda zai mallaki wannan abu idan har ina numfashi,duk masu bulayi da neman inda kake kallon su kawai nakeyi waɗan can mutanen da wani shu'umin ya sace su babu abinda zasu karan kawai dai ina ƙoƙarin rage yawan sune saboda zasu iya zama bara zana cikin samun farin cikina, Laila da ɗan uwanki duk ranar da na haɗa ido da wanda ya ɗaukeku gaba ɗayan ku zan haɗa na kashe bana so ki bayyana cikin ahlin ALHAJI BALARABE dake da shegiyar yariyar ki,duk da cewa ita ta bayyana amma tunda babu wanda yasan da labarin auren uwarta babu ta yadda za ayi ajingina ta da ahlin ESTATE ,kafun suma lokacinsu ya ƙara so ita da gwarzan mijinta,dariya yakeyi cike da farin cikin yana samun duk yadda yake so, tsarin sa yana tafiya dai dai da yadda ya buƙata,wani farin cikin ma sai nan gaba.
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ¼*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
```Page 35 ```