Sashe 78
Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
A ɓangaren Nafisa ma dai kusan haka din ne,tarasa abin kamawa,ta kai mari ta kai gauro,duk wani shirin ta neman kwancewa yake,shin ya akayi ta bari har Umar yake zargin ta?wane irin sakaci tayi haka,da balli yake neman tsinke mata?shar ce hawayen fuskar ta tayi tare da cewa me yasa al'amuran suke ƙoƙarin dagule min?shin basu Babe sun bani tabbacin sun mutu ba,me ya jawo duk wan nan?idan sun mutu ai bai kamata na dinga jin tashin hankali irin haka ba!'wayar ta tayi saurin rarimowa lambar da tayi shekara kusan goma sha takwas rabon ta da ita, ita ta dan nawa kira a yanzu,bata jima tana ringin ba aka daga,cikin matuƙar ƙasa da murya tace"da Babe nake magana?wata irin dariya irin ta cikakkun ƴan daba akayi tare da cewa hajjaju Nafisa gaskiya baki da amana,ko dan kiran nan a gaisa baki taɓa yi mana ba tun bayan da buƙatar ki ta biya,yanzu ma wata buƙatar ce ta taso miki ko?cikin sauri ta dakatar dashi tare da cewa,babe ba wannan ne abinda yasa nakiraka ba,tambayar ka zanyi,shin a wan can ranar baka ce min kun kashe matar nan da ɗiyar taba? tabbas haka na gaya miki amma nima sai kwanakin nan naji yarana suna hirar gaskiyar yadda abin ya faru, ashe nima muna funtata suka yi,a taƙaice dai basu kashe su ba dan ɓace musu sukayi suka rasa su,dan haka gaskiya bani da tabbacin sun mutu ko basu mutu ba,,,wata razanniyar ƙara ta saki tare da sakin wayar ta faɗi ta tar watse,zubewa tayi tana wani irin kuka mai cike da tashin hankali da tunanin makomar,shike nan su baku kashe su ba Ni kun kashe Ni ƙarshe na yazo, tabbas tunda Umar yace"zai nemosu sai ya nemo su in dai suna raye,yanzu ya zanyi?kaicona,me ye amfanin abinda nayi tunda ban samu riba ba,yanzu kam anzo gaɓar da dole sai na gayawa Bintu abinda na aikata, da bakina,domin ta samo min mafitar da zan tsira koda da rayuwata ce,ranar idanun Anty Nafisa basuga bacci ba duk iya satar sa kuwa.
Washe garin safiyar kuwa Umar ko ƙeyar Anty Nafisa bai gani ba,bai kuma neme taba shima, haka ya gama shirin sa na tafiya suleja,ai nahin inda ya mayar da su Hajjon Laila,shi yasa zuwa baya yi masa wuya,tunda ya dawo dasu cikin Abuja, ɓangaren Hajiya Babba ya fara zuwa su kayi sallama kasan cewar ita kaɗai ce tasan inda zashi,daga nan ya wuce sauran sashen suka gaisa, ya ɗan jima a bangaren inno dan kawai yana son ganin su Bintu sai dai ganin lokaci na ja basu fito ba yasa ya haƙura yayi sallama da inno ya ɗauki hanyar suleja, tare da ɗan rakiyar da bai san da yana bin sa ba.
A can ɓangaren Samira kuwa yau ta tashi ne cikin farin cikin babbar nasarar data ke tunkaro su,don kuwa a yau ɗin ne misalin ƙarfe huɗu na yamma zasu haɗu da Alhaji Sama'ila,kuma da alƙawarin zai gaya mata abinda suke nema suke yaki suka hana idon su bacci dare da rana,suka zalinci wasu suka ha inci wasu duk akan sa,yayi alƙawarin saboda yar dar da yayi mata da kuma gudummawar da ta kawo masa,zai gaya mata wannan abun da suke nema,wanda Ni kaina na ƙagu da naji ko menene wannan abun da ake ta zaluntar bayin Allah akansa.
Alhaji Baba ne ya zubawa kyakykyawar fuskar matar sa Hajiya Babba ido cike da son gano wani abu atare da ita, sam ya kasa gane mata kwana biyu kamar tana cikin damuwa,cikin taushin murya yace"meke damun ki ƴar Agadez?ɗan murmushi ta kalato wanda kana ganin sa kasan na yaƙe ne,tace"babu abinda yake damuna, halin rayuwa ne kawai,bai takura ta ba ya rabu da ita,sai ma can ja maganar da yayi da cewa,kin san dalilin kiran danayi miki? girgiza kanta tayi,yace"akan wannan ajiyar da na binne ne kin san dalilin da yasa naƙi gayawa kowa inda take,kuma bayan ke da Abubakar bana tunanin wani yasan da ita,duk saboda gudun fitina,to yanzu lokaci yayi da nake ga zan sanar da sauran ƴaƴana da matana, inda na ajiye wannan d....ɗan shuru yayi ganin kamar yaji motsi a tabayan ɗakin nasa,dan haka yace"Safiya mu bar maganar da sauran lokaci ban yadda da wajen nan ba kamar anyi mana laɓe a ta wajen nan....
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ¼*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
```Page 46 ```
Hajiya Babba tace"shike nan Allah ya baka ikon sanar da zuri'arka wan nan sirrin,tunda kaga dai dani da kai duk ba dauwama zamuyi a duniyar ba,shekaru ja suke yi,shi kuma wanda ya sani bashi ba labarin sa Allah ne kaɗai yasan halin da yake ciki!'ta ƙara sa maganar cikin fashewa da wani irin kuka wanda daga ji kasan ya daɗe yana cin ranta da zuciyar ta,ta kuma jima tana son yin sa,Alhaji Baba shuru yayi yana kallon ta bai katse mata kukan ta ba,dan ji yake inama shine ya samu damar yin wannan kuka da ya ji sauƙin abinda yake cunkushe a zuciyar sa,ɗan jingina yayi da jikin gadon yana fidda wani irin nishi mai fita da tsananin wahala da damuwa,baka jin sautin komai sai kukan Hajiya Babba da takeyin sa cikin wani irin baƙin ciki da tarin damuwa,cikin rawar murya tace"ya Allah ya Ubangiji na roƙeka ka bayyana min farin cikina kafin ƙasa ta rufe idanuna,ina roƙon ka bayyana sirrin dake ɓoye,ka fiddani daga cikin duhun da na shiga,ka kuma kawo farin ciki acikin rayuwar ɗana Umar ka bayyana masa sashin sa farin cikin sa, Allah ka nuna min ranar da zanga farin ciki da walwala a kan fuskar sa wanda yake daga cikin zuciyar sa!'amin Alhaji Baba yake ta cewa yana jin tururin dake kwance cikin zuciyar sa na lafawa,saboda tasirin addu'ar dayake ta nanatawa a duk lokacin da wata damuwa ta taso masa,allahumma la sahlan,itace addu'a mafi sauƙaƙa damuwar zuciya.
Dadyn Sayyid nifa na gaji da gafara sa har yanzu kuma banga ƙaho ba,kullum cewa kakeyi Sayyid zai dawo,amma har yanzu da muke cikin kwana na uku da ɓatan sa,babu wani labari mai daɗi akan sa, gaskiya ka nemo min yarona dan na gaji da wannan daɗin bakin naka!'Dady Mansur ya zaburo cikin masifa yace"au Nine nake miki daɗin bakin?ko kina tunanin kin fini shiga tashin hankalin rasa shi?ke baki san ko mai akan abinda nake tunani ba shi yasa bazaki gane tashin hankalin da nake ciki ba,amma saboda wuyan ki yayi kauri har Ni zaki duba kice ina miki daɗin baki!'ya faɗa yana ƙureta da kallon sa,bata ce masa ko mai ba sai da taje bakin step ɗin da zai kaita ɗakinta,ta juyo kana tace"ai dole hankalin ka yafi nawa tashi tunda kasan baka shuka gaskiya ba, yarona yana can za aɗauki fansar abinda kake yi akan sa,to kasani shi Allah babu ruwan sa, dan da wanda yayi zina da wanda ya tsaya akayi agabansa yana kallo duk ɗaya suke,tunda cewa yayi la taƙrabuzzina kada ku kasanci zina,to kaga kuwa baka da wata mafita laifin duk ɗaya ne kuma hukun ci daya,Ni dai kawai kasa waɗan da suka ɗauke min ɗana su dawo min dashi tunda shi baiji ba bare gani!'tana gama faɗar haka ta haura dakin ta da gudu,dan tasan kaɗan daga aikin Mansur ya faffalla mata maruka,a lallai wuyan ki yayi ƙauri,to zan ɗauki mummunan mataki akanki kuwa,da idan ba tsoro ba ki tsaya mana,da kuwa kin sha mamakin abinda zai biyo bayan waɗan nan mugayen kalaman naki!'fita yayi ran sa amatuƙar ɓace.
Washe garin safiyar kuwa Umar ko ƙeyar Anty Nafisa bai gani ba,bai kuma neme taba shima, haka ya gama shirin sa na tafiya suleja,ai nahin inda ya mayar da su Hajjon Laila,shi yasa zuwa baya yi masa wuya,tunda ya dawo dasu cikin Abuja, ɓangaren Hajiya Babba ya fara zuwa su kayi sallama kasan cewar ita kaɗai ce tasan inda zashi,daga nan ya wuce sauran sashen suka gaisa, ya ɗan jima a bangaren inno dan kawai yana son ganin su Bintu sai dai ganin lokaci na ja basu fito ba yasa ya haƙura yayi sallama da inno ya ɗauki hanyar suleja, tare da ɗan rakiyar da bai san da yana bin sa ba.
A can ɓangaren Samira kuwa yau ta tashi ne cikin farin cikin babbar nasarar data ke tunkaro su,don kuwa a yau ɗin ne misalin ƙarfe huɗu na yamma zasu haɗu da Alhaji Sama'ila,kuma da alƙawarin zai gaya mata abinda suke nema suke yaki suka hana idon su bacci dare da rana,suka zalinci wasu suka ha inci wasu duk akan sa,yayi alƙawarin saboda yar dar da yayi mata da kuma gudummawar da ta kawo masa,zai gaya mata wannan abun da suke nema,wanda Ni kaina na ƙagu da naji ko menene wannan abun da ake ta zaluntar bayin Allah akansa.
Alhaji Baba ne ya zubawa kyakykyawar fuskar matar sa Hajiya Babba ido cike da son gano wani abu atare da ita, sam ya kasa gane mata kwana biyu kamar tana cikin damuwa,cikin taushin murya yace"meke damun ki ƴar Agadez?ɗan murmushi ta kalato wanda kana ganin sa kasan na yaƙe ne,tace"babu abinda yake damuna, halin rayuwa ne kawai,bai takura ta ba ya rabu da ita,sai ma can ja maganar da yayi da cewa,kin san dalilin kiran danayi miki? girgiza kanta tayi,yace"akan wannan ajiyar da na binne ne kin san dalilin da yasa naƙi gayawa kowa inda take,kuma bayan ke da Abubakar bana tunanin wani yasan da ita,duk saboda gudun fitina,to yanzu lokaci yayi da nake ga zan sanar da sauran ƴaƴana da matana, inda na ajiye wannan d....ɗan shuru yayi ganin kamar yaji motsi a tabayan ɗakin nasa,dan haka yace"Safiya mu bar maganar da sauran lokaci ban yadda da wajen nan ba kamar anyi mana laɓe a ta wajen nan....
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ¼*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
```Page 46 ```
Hajiya Babba tace"shike nan Allah ya baka ikon sanar da zuri'arka wan nan sirrin,tunda kaga dai dani da kai duk ba dauwama zamuyi a duniyar ba,shekaru ja suke yi,shi kuma wanda ya sani bashi ba labarin sa Allah ne kaɗai yasan halin da yake ciki!'ta ƙara sa maganar cikin fashewa da wani irin kuka wanda daga ji kasan ya daɗe yana cin ranta da zuciyar ta,ta kuma jima tana son yin sa,Alhaji Baba shuru yayi yana kallon ta bai katse mata kukan ta ba,dan ji yake inama shine ya samu damar yin wannan kuka da ya ji sauƙin abinda yake cunkushe a zuciyar sa,ɗan jingina yayi da jikin gadon yana fidda wani irin nishi mai fita da tsananin wahala da damuwa,baka jin sautin komai sai kukan Hajiya Babba da takeyin sa cikin wani irin baƙin ciki da tarin damuwa,cikin rawar murya tace"ya Allah ya Ubangiji na roƙeka ka bayyana min farin cikina kafin ƙasa ta rufe idanuna,ina roƙon ka bayyana sirrin dake ɓoye,ka fiddani daga cikin duhun da na shiga,ka kuma kawo farin ciki acikin rayuwar ɗana Umar ka bayyana masa sashin sa farin cikin sa, Allah ka nuna min ranar da zanga farin ciki da walwala a kan fuskar sa wanda yake daga cikin zuciyar sa!'amin Alhaji Baba yake ta cewa yana jin tururin dake kwance cikin zuciyar sa na lafawa,saboda tasirin addu'ar dayake ta nanatawa a duk lokacin da wata damuwa ta taso masa,allahumma la sahlan,itace addu'a mafi sauƙaƙa damuwar zuciya.
Dadyn Sayyid nifa na gaji da gafara sa har yanzu kuma banga ƙaho ba,kullum cewa kakeyi Sayyid zai dawo,amma har yanzu da muke cikin kwana na uku da ɓatan sa,babu wani labari mai daɗi akan sa, gaskiya ka nemo min yarona dan na gaji da wannan daɗin bakin naka!'Dady Mansur ya zaburo cikin masifa yace"au Nine nake miki daɗin bakin?ko kina tunanin kin fini shiga tashin hankalin rasa shi?ke baki san ko mai akan abinda nake tunani ba shi yasa bazaki gane tashin hankalin da nake ciki ba,amma saboda wuyan ki yayi kauri har Ni zaki duba kice ina miki daɗin baki!'ya faɗa yana ƙureta da kallon sa,bata ce masa ko mai ba sai da taje bakin step ɗin da zai kaita ɗakinta,ta juyo kana tace"ai dole hankalin ka yafi nawa tashi tunda kasan baka shuka gaskiya ba, yarona yana can za aɗauki fansar abinda kake yi akan sa,to kasani shi Allah babu ruwan sa, dan da wanda yayi zina da wanda ya tsaya akayi agabansa yana kallo duk ɗaya suke,tunda cewa yayi la taƙrabuzzina kada ku kasanci zina,to kaga kuwa baka da wata mafita laifin duk ɗaya ne kuma hukun ci daya,Ni dai kawai kasa waɗan da suka ɗauke min ɗana su dawo min dashi tunda shi baiji ba bare gani!'tana gama faɗar haka ta haura dakin ta da gudu,dan tasan kaɗan daga aikin Mansur ya faffalla mata maruka,a lallai wuyan ki yayi ƙauri,to zan ɗauki mummunan mataki akanki kuwa,da idan ba tsoro ba ki tsaya mana,da kuwa kin sha mamakin abinda zai biyo bayan waɗan nan mugayen kalaman naki!'fita yayi ran sa amatuƙar ɓace.