Sashe 107
Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Baffa Hashir cikin tsananin jin kunya da nadama wadda take neman karya garkuwar jiki da ruhin sa, yace"ɗan uwa ina mai neman gafarar ka da kafemin cin amanar da nayi maka duk da cewa ban cutar da rayuwarka ko wani daga cikin ahlinka ba, amma naci dukiyar ka kuma naso aikata babban kuskure akan abinda ba nawa ba ba kuma na ɗana ba,a yanzu ina mai cikin tsananin nadamar abinda na aikata,tabbas na kasance maci amana mai saka Alkhairi da sharri,ka yafe min ɗan uwana ina cikin wani hali na na rashin samun yafiyar ka!'ya ƙarasa maganar da rushewa da wani matsanan cin kuka wanda har saida Alhaji Baba ya runtse idanun sa,daga nan suma suka samu damar neman gafara da yafiya magiya da kukan da suke shi ya tabbatar wa da jama ar gurin cewa sunyi taubatun nasuha,dan haka Alhaji Baba yayi gyaran murya tare da cewa haƙika kunyi kuskure a cikin tafiyar da al'amuran duniya da rayuwarku,kamar ba kuyi karatuba kai Hashir kamanta da hadisin da mahaifina yake yawan yi mana maimaicin sa,cewa Annabi Muhammad (s.w.a) yace"duk jikin da ta ginu da haramun ba zata shiga aljanna ba,haka kuma duk mai annami manci ba zai shiga aljanna ba,kai kuma gashi a wannan gaɓar duk sai gashi ka aikata waɗan nan laifukan,dan haka ina mai jan hankalin mu anan da mu gujewa cin haram komai ƙan ƙantar ta,mugujewa ha'inci,da cin amana,domin Allah baya yafe laifin da akayiwa bayinsa,daga ƙarshe ina mai tunatar daku muhimmancin gaskiya da rikon amana,na yafe muku Allah ya yafe mana baki ɗaya,amma ku sani duk wanda yake aikata wani mummunan laifi to ya dinga tunawa da mutuwa san nan kuma duk abinda yake yi Ubangijin sammai da ƙassai yana kallon sa,ko da ka mutu asirin ka bai tonuba to tabbas a lahira za a nuna maka dukan aiyukan ka,da kunyar lahira kuwa gara ta duniya,zanso idan ina aikata mugun aiki asirina ya tonu ko hakan zai iya zama sanadin shiriyata, Allah yasa mu dace ya kuma karemu daga ruɗin zuciya ya tsare imanin mu!'da Amin suka amsa yayin da jikkuna su kayi sanyi zuciyoyi suka mutu hankula suka fara dawowa jiki,kiran sallar da akayi shi ya dakatar dasu daga ci gaba da gabatar da al'amuran da suke faruwa,Alhaji Baba yace"ya kamata muje muyi sallah ina yaso sai mu dawo mu ɗora daga inda muka tsaya idan akwai wani abun kenan!'Abdallah ne ya fara miƙewa idanun sa suna shawagi akan Dady Habib da Hajjah gani yake kamar zasu iya guduwa dan haka kawai sai yace" da Dady Mansur da Dady jafar su tafi suyi Sallah da Dady Habib saboda yanayin jikinsa su sun fahimci abinda yake nufi,yayin da wasu sukayi tunanin ko Dady Habib ɗin bai da lafiya ne,a hankali aka shiga watsewa daga falon, Abdallah yana fitowa ya kira wayar Safwan yace"su ke waye gaba ɗaya estate din Nan kar su bari ko ƙwaro ya fita,har gefan Hajjah bai bari ba sai da ya tabbatar da tsaron wajen.
A bangaren Anty Nafisa kuwa tunda ta fita sai taji bata da kwarin gwiwar shiga ɓangaren ta,tunanin makomar ta a wajen Abba Umar shine abinda ya da baibaye ƙwaƙwalwarta,jikin ta asanyaye haka ta shiga falon tana mai jin tsananin faɗuwar gaba akan abinda zai biyo bayan tonuwar asirin ta,
Duk da cewa kowa ɗokance yake da ya keɓe da iyalan sa,tsakanin Abba Umar da Fafi,amma hakan suka hakura suka nufi masallaci bayan sunyi alwala da tunanin ai yanzu komai ya wuce babu abinda zai kuma rabasu da iyalansu idan ba mutuwaba,lokaci lokaci zaka ga murmushi kan fuskar Abba Umar wanda yake nuni da tsananin farincikin da yake ciki ga matar shi Laila ga gudan jininshi Bintu babu abunda zaice da Allah sai godiya Alhamdulillah masha Allah.
Su inno dai da Hajiya Babba su sukayi ma sauƙin baƙi,Hajiya Babba kamar yadda ta saba tayiwa inno kara da alkunya ita tabarwa ragamar karrama surukar tata tare da ririta ta tamkar basu taɓa yin suruka acikin ESTATE ba,Hajiya zulaihat ma tana manne da Laila,dan ko ɓangaren ta bata koma ba,Bintu kuwa gatan har nema yake yayi mata yawa sai dai duk da haka ta kasa sukunin rashin ganin Oganta Abdallah maganin kukanta,wata irin kewar sa takeji tare da tsananin bege,wanda har kawo yanzu ta kasa fassara hakan da cewa ƙauna ce mara algus,
Bayan idar da sallar ne mazan duk suka hallara a falon Alhaji Baba,yayin da ya bada umarnin akawo abinci a fara ci kafin ci gaba da tattaunawa,a lokacin ne kuma ya saka waya yayi kiran Alhajin Nafisa ya sanar dashi yana buƙatar ganin sa tare da Hajiya ladidi,kowa yana sabga cikin walwala amma banda Dady Habib wanda bugun da zuciyarsa take yi tafi ƙarfin a misalta,yanzu yafi kowa shiga tashin hankali tabbas da ya samu hanya sai ya gudu dan yana ganin guduwar ita ce kadai mafita
agareshi da kuma samun sauki a gareshi.
Hajja kam tun komawarta bangaren ta take zawo har sai da Nana karama tace"wai Hajja lafiyar ki kuwa naga sai sunturin banɗaki kike?bata iya bawa ƴar tata amsa ba sai komawa da tayi ban dakin dan ta ga alama zaman cikin sa sai yafi mata sauƙi,a kwai abinda take ɓoyewa wanda babu wanda yasan shi kuma tana ganin lallai lokacin tonuwar wannan sirri yayi shi yasa abun ya haɗe mata bata jin cewa duk sanyin zuciyar Alhaji Baba zai iya yafe mata wan nan al'amari,a yanzu kaico da nadama take,shin tayaya zata iya fuskantar Alhaji Baba da wannan sirrin wanda tasan cewa koda su Abdallah sun san wancan to tabbas basu san wannan ba,yaya duniya zata kalleta da sauran ƴaƴan ta idan sukaji abinda ta aikata,dole tasa ta ci gaba da zaman banɗakin domin tun yanzu ta fara jin kunyar haɗa idanu da iyalanta,
Oga Abdallah kuwa mai gaiya mai aiki duk yadda ya kai ka san yin juriyar hakura da ganin Bintu abun gagara yayi, cikin rashin sukuni ya nufi ɓangaren inno,yana shiga falon yaci karo da Dije zata shiga kiching inda suke hada hadar dafa abinci,tsayawa tayi tare da cewa,a'a yallaɓai ko kana buƙatar wani abunne? cikin ɗan basarwa da farincikin da yaji na samun dama yace"ki bawa Bintu ruwa ta kawo min!'daga haka yayi saurin faɗawa falon sa,wani ɗan murmushi tayi tare da shigewa ɗakin inno inda Bintun suke tare da su Laila da Hajjo,yafito Bintu tayi,suna fita ta miƙa mata ruwan da ta ɗauko,ba ta haɗa da komai ba,dan tasan ba wai ruwan yake buƙata ba,tace"maza jeki kaiwa mijinki yana cikin falonsa!'ai kafin ta kai ga rufe bakinta tuni ta tsinci Bintu abakin kofar falon Abdallah,riƙe baki tayi cike da dariyar yarintar Bintun.
Kamar an jehota haka ya ganta a gabansa kasan cewar tun shigarsa bai zaunaba,zuba mata idanunsa masu saukar mata gajiya yayi,haka nan ta dinga jin wani irin sanyi har cikin kashinta sunkuyar da kanta tayi tana jin wasu ƙwallan da bata san daga ina suke ba,ɗan ware idan sa ya kuma yi akanta,kana a hankali ya riƙota kamar wanda yake tsoran kar yaji mata ciwo,ɗagowa tayi ta shiga yi masa wani irin kallo daya fara sashi kokuwa da numfashinsa, cikin wani irin salo da shauƙi ya haɗe ta jikin sa,tare da ɗora fuskarshi saman kanta,zame ɗan kwalin kanta yayi ya shiga shinshina gashinta kamar wanda ya samu turare,Bintu cikin wata irin kasala ta kuma lafkewa cikin faffaɗan ƙirjinsa,can kasan maƙoshi ta tsinkayi Muryar sa yana cewa my Bint,sai kuma me kike bukata? Ummm faɗa min!"ya faɗa cikin cusa kanshi a wuyanta yana goga fuskarsa da ɗan gemun sa akan uyan nata, cikin wata iriyar kasala da yake saukar mata ta shiga goga fuskar ta a kan ƙirjin sa tare da cewa"Ni kam ka gama min komai bani da wata sauran damuwa,ka cika min burina ka dawo min da farin ciki na, wannan ma kaɗai ya isheni!'ɗan murmushin gefan baki yayi tare da cewa a'a faɗa min dai ina sauraren ki da akwai wani farin cikin da kike bukata!'girgiza kanta ta shiga yi jikin ta yana kuma mutuwa da salon da ogan nata yake mata,kamar daga sama taji bakin shi cikin nata wata doguwar sumba yayi mata tare da cewa hmm Bint ki duba mana bakya bukatar wan Nan?a ruɗe ta kuma girgiza masa kanta,ya kuma sumbatar idanunta yana cewa da wannan ma,ya sumbaci goshinta da wannan ma,daga nan ya zarce da yiwa bakinta wata irin tsotsa tamkar wanda ya samu sweet.....
Mu haÉ—u a falon Alhaji Baba zama na biyu
Fatima y AdamâœðŸ½
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ¼*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
```Page 59 ```
A bangaren Anty Nafisa kuwa tunda ta fita sai taji bata da kwarin gwiwar shiga ɓangaren ta,tunanin makomar ta a wajen Abba Umar shine abinda ya da baibaye ƙwaƙwalwarta,jikin ta asanyaye haka ta shiga falon tana mai jin tsananin faɗuwar gaba akan abinda zai biyo bayan tonuwar asirin ta,
Duk da cewa kowa ɗokance yake da ya keɓe da iyalan sa,tsakanin Abba Umar da Fafi,amma hakan suka hakura suka nufi masallaci bayan sunyi alwala da tunanin ai yanzu komai ya wuce babu abinda zai kuma rabasu da iyalansu idan ba mutuwaba,lokaci lokaci zaka ga murmushi kan fuskar Abba Umar wanda yake nuni da tsananin farincikin da yake ciki ga matar shi Laila ga gudan jininshi Bintu babu abunda zaice da Allah sai godiya Alhamdulillah masha Allah.
Su inno dai da Hajiya Babba su sukayi ma sauƙin baƙi,Hajiya Babba kamar yadda ta saba tayiwa inno kara da alkunya ita tabarwa ragamar karrama surukar tata tare da ririta ta tamkar basu taɓa yin suruka acikin ESTATE ba,Hajiya zulaihat ma tana manne da Laila,dan ko ɓangaren ta bata koma ba,Bintu kuwa gatan har nema yake yayi mata yawa sai dai duk da haka ta kasa sukunin rashin ganin Oganta Abdallah maganin kukanta,wata irin kewar sa takeji tare da tsananin bege,wanda har kawo yanzu ta kasa fassara hakan da cewa ƙauna ce mara algus,
Bayan idar da sallar ne mazan duk suka hallara a falon Alhaji Baba,yayin da ya bada umarnin akawo abinci a fara ci kafin ci gaba da tattaunawa,a lokacin ne kuma ya saka waya yayi kiran Alhajin Nafisa ya sanar dashi yana buƙatar ganin sa tare da Hajiya ladidi,kowa yana sabga cikin walwala amma banda Dady Habib wanda bugun da zuciyarsa take yi tafi ƙarfin a misalta,yanzu yafi kowa shiga tashin hankali tabbas da ya samu hanya sai ya gudu dan yana ganin guduwar ita ce kadai mafita
agareshi da kuma samun sauki a gareshi.
Hajja kam tun komawarta bangaren ta take zawo har sai da Nana karama tace"wai Hajja lafiyar ki kuwa naga sai sunturin banɗaki kike?bata iya bawa ƴar tata amsa ba sai komawa da tayi ban dakin dan ta ga alama zaman cikin sa sai yafi mata sauƙi,a kwai abinda take ɓoyewa wanda babu wanda yasan shi kuma tana ganin lallai lokacin tonuwar wannan sirri yayi shi yasa abun ya haɗe mata bata jin cewa duk sanyin zuciyar Alhaji Baba zai iya yafe mata wan nan al'amari,a yanzu kaico da nadama take,shin tayaya zata iya fuskantar Alhaji Baba da wannan sirrin wanda tasan cewa koda su Abdallah sun san wancan to tabbas basu san wannan ba,yaya duniya zata kalleta da sauran ƴaƴan ta idan sukaji abinda ta aikata,dole tasa ta ci gaba da zaman banɗakin domin tun yanzu ta fara jin kunyar haɗa idanu da iyalanta,
Oga Abdallah kuwa mai gaiya mai aiki duk yadda ya kai ka san yin juriyar hakura da ganin Bintu abun gagara yayi, cikin rashin sukuni ya nufi ɓangaren inno,yana shiga falon yaci karo da Dije zata shiga kiching inda suke hada hadar dafa abinci,tsayawa tayi tare da cewa,a'a yallaɓai ko kana buƙatar wani abunne? cikin ɗan basarwa da farincikin da yaji na samun dama yace"ki bawa Bintu ruwa ta kawo min!'daga haka yayi saurin faɗawa falon sa,wani ɗan murmushi tayi tare da shigewa ɗakin inno inda Bintun suke tare da su Laila da Hajjo,yafito Bintu tayi,suna fita ta miƙa mata ruwan da ta ɗauko,ba ta haɗa da komai ba,dan tasan ba wai ruwan yake buƙata ba,tace"maza jeki kaiwa mijinki yana cikin falonsa!'ai kafin ta kai ga rufe bakinta tuni ta tsinci Bintu abakin kofar falon Abdallah,riƙe baki tayi cike da dariyar yarintar Bintun.
Kamar an jehota haka ya ganta a gabansa kasan cewar tun shigarsa bai zaunaba,zuba mata idanunsa masu saukar mata gajiya yayi,haka nan ta dinga jin wani irin sanyi har cikin kashinta sunkuyar da kanta tayi tana jin wasu ƙwallan da bata san daga ina suke ba,ɗan ware idan sa ya kuma yi akanta,kana a hankali ya riƙota kamar wanda yake tsoran kar yaji mata ciwo,ɗagowa tayi ta shiga yi masa wani irin kallo daya fara sashi kokuwa da numfashinsa, cikin wani irin salo da shauƙi ya haɗe ta jikin sa,tare da ɗora fuskarshi saman kanta,zame ɗan kwalin kanta yayi ya shiga shinshina gashinta kamar wanda ya samu turare,Bintu cikin wata irin kasala ta kuma lafkewa cikin faffaɗan ƙirjinsa,can kasan maƙoshi ta tsinkayi Muryar sa yana cewa my Bint,sai kuma me kike bukata? Ummm faɗa min!"ya faɗa cikin cusa kanshi a wuyanta yana goga fuskarsa da ɗan gemun sa akan uyan nata, cikin wata iriyar kasala da yake saukar mata ta shiga goga fuskar ta a kan ƙirjin sa tare da cewa"Ni kam ka gama min komai bani da wata sauran damuwa,ka cika min burina ka dawo min da farin ciki na, wannan ma kaɗai ya isheni!'ɗan murmushin gefan baki yayi tare da cewa a'a faɗa min dai ina sauraren ki da akwai wani farin cikin da kike bukata!'girgiza kanta ta shiga yi jikin ta yana kuma mutuwa da salon da ogan nata yake mata,kamar daga sama taji bakin shi cikin nata wata doguwar sumba yayi mata tare da cewa hmm Bint ki duba mana bakya bukatar wan Nan?a ruɗe ta kuma girgiza masa kanta,ya kuma sumbatar idanunta yana cewa da wannan ma,ya sumbaci goshinta da wannan ma,daga nan ya zarce da yiwa bakinta wata irin tsotsa tamkar wanda ya samu sweet.....
Mu haÉ—u a falon Alhaji Baba zama na biyu
Fatima y AdamâœðŸ½
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ¼*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
```Page 59 ```