Sashe 66
Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Shuru officce ɗin ya ɗauka na dan wani lokaci,kana daga bisani Alhaji Rufa'i ya ja doguwar ajiyar zuciya tare da maida duban sa kan Dady jafar,yace" jafar akwai al'amari mai matukar ruɗarwa a cikin rayuwar iyalan mai gida,ɗan gyara zaman sa yayi tare da ƙara fuskantar Abdallah ya cigaba da cewa,tun a shekarun baya na fuskanci yadda al amuran ahlin ALHAJI BALARABE yake sauyawa da wani irin san zuciya da san duniya,kasan cewar Ni ba mazaunin Abuja bane ballantana na sa ido akan wasu miyagun abubawan da suke faruwa cikin ESTATE ɗin,to kuma ina cikin taraddadi da tunanin hanyar da zan ɓullowa al'amarin kawai saiga tayin da su Alhaji Hashir suka kawo min na san in shiga cikin su saboda sun san nima zan taimaka, kuma akwai manyan kadarorin Alhaji Baba A hannuna,ganin wannan ma wata dama ce na samu ta samun zaƙulo abinda ake ta ɓoyan sa da kuma makircin da ake son ƙullawa uban gidana kawai sai na amshi wannan tayin cikin nuna farin ciki,nan kuma aka shiga gwagwarmayar dani da faɗi tashin yadda za a samu wannan ajiyar da kowa yake harinta, A lokacin na samu na tara wujjoji masu yawa akan su Alhaji Hashir,sai dai har kawo rana irin ta yau na kasa gano abin da ake nema,duk iya bincikena da bin diddigina amma hakan ya gagara,kuma abinda na fahimta kamar dai nine kawai acikin su ban san wannan sirrin ba Ni kaɗai suka rufewa wanda nakasa gano dalilin haka, har ma na fara tunanin ko sun harbo jirgina ne nasan tona musu Asiri,sai kuma na lura sam ba haka bane kawai dai har yanzu basu gamsu dani bane,ba yanzu suka shirya sanar dani ba har sai sun gamsu da gaskiyata acikin su,kuma ina zargin Alhaji shamsi yasan ko mai akan abinda suke fafutukar nema, wanda shine baya cikin wannan kungiya tasu hasali ma nuna musu yake baza a haɗa baki dashi aci amanar ALHAJI BALARABE ba, duk da cewa zargina bai tsananta A kansa ba amma ya kamata abi sahunsa dan ina da tabbacin zamu sami wani abu daga ɓangaren sa!'yana tsayawa nan A bayanin sa Dady jafar ya ɗauka da cewa, Alhaji Rufa'i duk wan nan bayanan dakayi mana kamar tuni ne a wajen mu sai ɗan abinda ba A rasa ba,da kuma manufar ka ta shiga cikin su Alhaji Mansur,saboda ba a zaune muke ba kuma in Sha Allah muna gab da tonawa kowa asiri!'miƙewa Abdallah yayi tare da duban Dady jafar,gane abinda yake nufi da yayi ne yasa yace"Abdallah baka ce komai ba kuma kana shirin tafiya,ko baka yadda da gaskiyar Rufa'i ba?ɗan jim Abdallah yayi tare da cewa zan neme shi idan na tabbatar da abinda ya faɗa gaskiya ne!' daga haka ya fita daga officce ɗin ya barsu,Dady jafar yace" da Alhaji Rufa'i kar ka damu nasan zaiyi nazarine akan maganarka,saboda Abdallah mutum ne da bayayin abu cikin gaggawa komai yana yinsa cikin nutsuwa ne shi yasa ba zai saurin baka yarda nan take ba!'Alhaji Rufa'i yace" wannan shine halin manya,kuma hakan Abune mai kyau kayi dacen haihuwa yaron ka yana da ƙwazo da himma da kuma uwa uba san tabbatar da gaskiya, murmushin jin daɗi Dady jafar yayi,batare da yace komai ba,kana yaji daɗi da Alhaji Rufa'i bai san matsayin Abdallah a gurin sa ba,hakan yana masa nuni da cewa har yanzu su Alhaji Hashir basu san waye Abdallah ba,kuma hakan yana nufin sune da nasara akansu Alhaji Nasir ɗin.
Fitowar sa daga officce ɗin kai tsaye mota ya shiga Yahya yajashi zuwa asibiti,duk da yadda ƙwaƙwalwar sa ta ɗauki zafi da wannan al'amari hakan bai hanashi nutsuwa ya duba marasa lafiyar da suke buƙatar sa ba,duk da a can ƙasar zuciyar sa ji yake kamar ya koma gidan awan nan lokacin ko dan duba lafiyar Bintu, sai dai kuma hakan ba mai yuwuwa bane dan da akwai ayyuka da yawa da suke gaban sa,wayar sa ya zaro daga gefan aljihun rigar sa, danna wa yayi tare da ɗora ta akunnen sa,ba ayi minti ɗaya ba aka daga wayar,cikin lafiyayyar Muryar shi yace"sani idan kana cikin Kano ina so kayi min wani aiki A nan!'banji mai akace ta ɗaya ɓangaren ba naji dai Abdallah ya ɗora da bashi bayanai akan Alhaji Rufa'i,ya ɗora da cewa inaso bayanan shigo da da sauri,ok kawai yace"tare da kashe wayar ya turata ma zaunin ta..
Dije kin san dalilin da yasa nace ki dawo ko?ba tare da ta jira amsar Dijen ba ta cigaba da cewa,gagarumin aikine ya taso min wanda dole sai da mataimaki,dan haka ina so ki maida hankali kan abinda zan sanar dake, ban ɗaukoki dan kici amanata ba ɗauko ki nayi dan kiyi min aiki,Dije lallai ina buƙatar ki shiga jikin Bintu ba dan kanki ba sai dan kaina da biyan buƙatata,danƙo kunnen Dijen tayi cikin ƙara yi mata kashedi da gargaɗi tace"wallahi wallahi wallahi Dije in dai na sameki da kuskewa daga kan maganata ko cin amanata to ki tabbatar da cewa ƙarshen rayuwar iyalan ki yazo ke nan,ke kuma sai na ƙarar da rayuwarki ta hanyar gana miki azaba iri iri wadda ita kaɗai ta ishi mai irin halinki na cin amana izina,salon da kika fara dashi nakeso ki ɗora ki barta a yadda tasan ki,sonake ki lulluɓeta da kalaman yaudara ki nuna mata kinatare da ita, ki tayata yaƙin nemo wancan shu umin,ni kuma abinda nake buƙata ke nan daga gareta tunda ita da mijinta suna da baiwar gano mugu to Ni kuma da ita zan jingina dan cimma burina!'babu abinda Dije take sai kuka wanda yake tafe da wani irin baƙin ciki na kasancewar rayuwar ta a haka, tabbas da tana da damar canja ƙaddarar ta ta zuwa aƙasan wannan shu'umar mata,sai dai ina, bakin alƙalami ya riga ya bushe Allah da yayo rayuwarta ahaka shi yasan dalilin haɗa ta da wannan mata,insha Allah sai ta zama sanadin bankaɗuwar asirin wan nan makirar mata,duk duniya babu abinda yafi ƙarfin Ubangiji dan haka bazata karaya da waɗan nan mugayen kalaman nata ba,ta riga tayiwa Bintu alƙawari kuma tayi alƙawari ita da Ubangijin ta saita tona asirinta,koda kuwa shine abu na ƙarshe da zatayi arayuwarta,wata gigitacciyar tsawa ta dakawa Dijen wadda har sai da ta toshe kunnuwanta,tare da runtse idanun ta tana kuma mai fatan Ubangiji ya bata dama da nasara akan wannan azzalumar mata,koma wacece,matar tace"kinaji na kina kumajin alwashina akanki dan haka ki tabbatar da cewa ba asamu matsala cikin wannan aikin ba domin shine kwanciyar hankalin ki da rufuwar asirinki da cigaban rayuwar zuri arki!'ki tashi yanzu ki koma cikin ESTATE ki gayawa uwar ɗakin ki cewa kin dawo daga zaman jinyar da kika tafi,daga karshe ina mai kuma tunasar dake muhimmancin amanata!' cikin sanyin jiki da kuma ƙwarin gwiwar rusa rayuwar ta, Dije ta miƙe tare da kama hanya ta fita daga gurin wanda kullum zasu haɗu sai ta canja gurin haɗuwar tasu kai wannan mata ta iya takunta.
Dide ta dawo cikin ESTATE da kyakykyawar niya,da kuma burin hada hannu da Bintu dan su cimma kyakykyawar manufarsu wadda abaya ta dakatar dasu,zasu ɗora daga inda suka tsaya, saboda yanzu tana da cikakken ikon tarayya da Bintun zasu kashe su binne batare da tasani ba ta yadda ita take yiwa aiki amma ta wani gefan aikin rusa rayuwarta da farin cikin ta zasuyi ita da Bintu,cikin ƙudurar Allah gashi ita da kanta ta bata damar fallasa sirrinta da kuma rusa duk wani shiri da takeyi dan cimma mummunar manufar ta,ita da kanta ta bata lasisin tarayya da Bintu,tabbas lokacin karya alƙadarin waɗan nan azzalumai yayi lokacin banƙaduwar sirrin su yayi,zatayi abinda ya dace dan kuɓutar da bayin Allah da basuji ba basu gani ba,ko dan haka tasan Allah bazai taɓa bawa wannan tsohuwar azzalumar ikon cutar da ita ba,dan haka da ƙwarin gwiwar ta ta koma aikin ta ka in da na'in.
Fitowar sa daga officce ɗin kai tsaye mota ya shiga Yahya yajashi zuwa asibiti,duk da yadda ƙwaƙwalwar sa ta ɗauki zafi da wannan al'amari hakan bai hanashi nutsuwa ya duba marasa lafiyar da suke buƙatar sa ba,duk da a can ƙasar zuciyar sa ji yake kamar ya koma gidan awan nan lokacin ko dan duba lafiyar Bintu, sai dai kuma hakan ba mai yuwuwa bane dan da akwai ayyuka da yawa da suke gaban sa,wayar sa ya zaro daga gefan aljihun rigar sa, danna wa yayi tare da ɗora ta akunnen sa,ba ayi minti ɗaya ba aka daga wayar,cikin lafiyayyar Muryar shi yace"sani idan kana cikin Kano ina so kayi min wani aiki A nan!'banji mai akace ta ɗaya ɓangaren ba naji dai Abdallah ya ɗora da bashi bayanai akan Alhaji Rufa'i,ya ɗora da cewa inaso bayanan shigo da da sauri,ok kawai yace"tare da kashe wayar ya turata ma zaunin ta..
Dije kin san dalilin da yasa nace ki dawo ko?ba tare da ta jira amsar Dijen ba ta cigaba da cewa,gagarumin aikine ya taso min wanda dole sai da mataimaki,dan haka ina so ki maida hankali kan abinda zan sanar dake, ban ɗaukoki dan kici amanata ba ɗauko ki nayi dan kiyi min aiki,Dije lallai ina buƙatar ki shiga jikin Bintu ba dan kanki ba sai dan kaina da biyan buƙatata,danƙo kunnen Dijen tayi cikin ƙara yi mata kashedi da gargaɗi tace"wallahi wallahi wallahi Dije in dai na sameki da kuskewa daga kan maganata ko cin amanata to ki tabbatar da cewa ƙarshen rayuwar iyalan ki yazo ke nan,ke kuma sai na ƙarar da rayuwarki ta hanyar gana miki azaba iri iri wadda ita kaɗai ta ishi mai irin halinki na cin amana izina,salon da kika fara dashi nakeso ki ɗora ki barta a yadda tasan ki,sonake ki lulluɓeta da kalaman yaudara ki nuna mata kinatare da ita, ki tayata yaƙin nemo wancan shu umin,ni kuma abinda nake buƙata ke nan daga gareta tunda ita da mijinta suna da baiwar gano mugu to Ni kuma da ita zan jingina dan cimma burina!'babu abinda Dije take sai kuka wanda yake tafe da wani irin baƙin ciki na kasancewar rayuwar ta a haka, tabbas da tana da damar canja ƙaddarar ta ta zuwa aƙasan wannan shu'umar mata,sai dai ina, bakin alƙalami ya riga ya bushe Allah da yayo rayuwarta ahaka shi yasan dalilin haɗa ta da wannan mata,insha Allah sai ta zama sanadin bankaɗuwar asirin wan nan makirar mata,duk duniya babu abinda yafi ƙarfin Ubangiji dan haka bazata karaya da waɗan nan mugayen kalaman nata ba,ta riga tayiwa Bintu alƙawari kuma tayi alƙawari ita da Ubangijin ta saita tona asirinta,koda kuwa shine abu na ƙarshe da zatayi arayuwarta,wata gigitacciyar tsawa ta dakawa Dijen wadda har sai da ta toshe kunnuwanta,tare da runtse idanun ta tana kuma mai fatan Ubangiji ya bata dama da nasara akan wannan azzalumar mata,koma wacece,matar tace"kinaji na kina kumajin alwashina akanki dan haka ki tabbatar da cewa ba asamu matsala cikin wannan aikin ba domin shine kwanciyar hankalin ki da rufuwar asirinki da cigaban rayuwar zuri arki!'ki tashi yanzu ki koma cikin ESTATE ki gayawa uwar ɗakin ki cewa kin dawo daga zaman jinyar da kika tafi,daga karshe ina mai kuma tunasar dake muhimmancin amanata!' cikin sanyin jiki da kuma ƙwarin gwiwar rusa rayuwar ta, Dije ta miƙe tare da kama hanya ta fita daga gurin wanda kullum zasu haɗu sai ta canja gurin haɗuwar tasu kai wannan mata ta iya takunta.
Dide ta dawo cikin ESTATE da kyakykyawar niya,da kuma burin hada hannu da Bintu dan su cimma kyakykyawar manufarsu wadda abaya ta dakatar dasu,zasu ɗora daga inda suka tsaya, saboda yanzu tana da cikakken ikon tarayya da Bintun zasu kashe su binne batare da tasani ba ta yadda ita take yiwa aiki amma ta wani gefan aikin rusa rayuwarta da farin cikin ta zasuyi ita da Bintu,cikin ƙudurar Allah gashi ita da kanta ta bata damar fallasa sirrinta da kuma rusa duk wani shiri da takeyi dan cimma mummunar manufar ta,ita da kanta ta bata lasisin tarayya da Bintu,tabbas lokacin karya alƙadarin waɗan nan azzalumai yayi lokacin banƙaduwar sirrin su yayi,zatayi abinda ya dace dan kuɓutar da bayin Allah da basuji ba basu gani ba,ko dan haka tasan Allah bazai taɓa bawa wannan tsohuwar azzalumar ikon cutar da ita ba,dan haka da ƙwarin gwiwar ta ta koma aikin ta ka in da na'in.