Sashe 89
Kudurar Allah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gyaran muryar da Alhaji Baba yayi ita ta sakawa kowa nutsuwa,tare da maida duk hankulan su kansa,cikin nutsuwar da bata hana damuwar sa baiyana ba,yace"duk hasashen ku bai zama daidai ba,domin nasan abinda zan fada muku bashi kuke tunanin zan faɗa ba,saboda nima yau tunanin ya fito daga zuciya ta zuwa kan harshena,ɗan shuru yayi,yayin da zuciyoyi suka ƙagauta da jin wannan batu,duk iya tunanin su akan dimon ne saboda su waɗan da suke abun sun san cewa Alhaji Baba bai san maganar dimon ɗin ta fita ba,balle yasan muguwar rigima da cutar data haifar a cikin zuri'arsa,Alhaji Baba yaci gaba da cewa,shi yasa zan sanar daku dan mu haɗu muyiwa kanmu da zuriar mu maganin abinda yake damunta,dan fitar da iska yayi ta bakin sa tare da sauke numfashin damuwar dake cunkushe a zuciyar sa,kana yaci gaba da cewa maganar Abubakar ce,,,wata irin zabura Dady Mansur yayi yayin da sauran mutanen ɗakin sukayi ɗif kamar babu wata halitta a falon,kowa da irin bugun da zuciyar sa keyi masa, Hajjah kuwa wasu hawaye ne suka sauko mata tana cewa Alhamdulillah godiya ta tabbata ga Allah wanda yayi zuciya,kawai sai ta fashe da kukan farinciki nanatawa take Allah kasa lokacine yayi da gaskiya zata bayyana!'kowa ka kalla afalon nan da akwai abinda ke damun sa na matukar ruɗani da firgicin jin maganar Abubakar ta taso lokaci ɗaya, Dady Mansur kuwa kuka ya saka sosai wanda kana ji kasan kukane da yake fita tun daga ƙarƙashin zuciyar sa,ya kasa cewa komai sai sautin kukan sa dake fita gwanin tausayi,Dady Habib ne ya ɗan goge fuskarsa kana cikin nutsuwa yace"haba yaya bai kamata ba da girman ka kadinga abin yara!'wani Irin mahaukacin kallo me cike da fassarori da ma'anoni masu yawa Dady Mansur ya jefawa ɗan uwan nasa,ba tare kuma da ya iya ce masa komai ba,karon farko ke nan da yayiwa Mansur irin haka batare da ya tanka masa ba,ɗauke kansa yayi cike da mamakin wannan kallon da Mansur yake masa,ko me yake nufi da haka?
Alhaji Baba yayi wani ɗan murmushi na takaici kana ya cigaba da cewa,a yau kuma a yanzu nasa afara rokon ALLAH ba dare ba rana idan Abubakar yana lafiya Allah ya baiyana mana shi idan baya cikin haicinsa kuma Allah ya bashi lafiya ya dawo min dashi cikin gidan nan,idan kuma ya mutu,,,,,kukan Hajiya Babba ne ya dakatar da shi daga barin abinda zai faɗa,cikin kuka da matsanancin tashin hankali tace"dan Allah Alhaji karka ƙarasa,inason ganin jagora araye (dake sunan da take gaya masa mafi lokata acikin mutane saboda karar ɗan fari)taci gaba da cewa Wallahi inaso yazo gidan nan araye inaso naga waɗanda suka gurgunta min rayuwar sa akan abin ɗun,,,,bata ƙarasa ba inno ta rufe mata baki tare da girgiza mata kai,alamun kar ta faɗi abinda ke cikin zuciyar ta,tunda shi Alhaji Baba baƙo ne akan sanin hakan,zai iya zurfafa bincike akan al'amarin,shurun kuwa tayi bata sake cewa komai ba,sai dai kukan da taci gaba dayi ƙasa ƙasa,yayin da Hajjah ta zuba musu idanun ayar tambaya da wannan sabon Al'amarin, wai meke shirin faruwa a gidan nan ne haka? Alhaji Baba yace"dama abinda nake son sanar daku kenan kowa zai iya tafiya!'daga haka ya miƙe ya shige can cikin ƙuryar ɗakin sa,jiki asan yaye suka dinga ficewa daga falon kowa ya kasa magana dan sun rasa abin cewa,wasu farin cikine ya hana su magantuwa wasu kuma bakin ciki,kowa ya fita daga falon sai Abba Umar da Aliyu,da kuma Dady Habib,sai su inno,Abba Umar yace"Hajiya Babba ku daina kuka komai ya kusa wucewa insha Allah tun da har muka samu Alhaji Baba da kansa yayi maganar yaya,kuma daga nan nima gurin wani malami na zan wuce Musa aƙara tsanan ta rokon Allah!'Dady Habib yace"tabbas maganar Umar haka take nima ina da malaman da zan saka cikin lamarin, san nan a ganina ya kamata a hada da cigiya gidajen rediyo ko za a dace!'Hajjah tace"hakan yayi Allah yayi muku albarka!'shi Abba Aliyu ma atake nan ya fara kiran malaman sa kasan cewar shi malamin addinni ne ya fara shela yana sanar dasu asaka almajirai sauka,yanzu zai taho da kayan sadaka,inno tace"masha Allah Ubangiji Allah ya baiyana mana shi cikin farin ciki da cikakken lafiya!'gaba ɗaya suka amsa da Amin summa Amin.
Tunda ya fito yaji wani irin jiri na san kayar dashi,amma duk da haka sai da ya nufi ɓangaren ƙonannen dakin,zubewa yayi agurin yana cigaba da wani irin kuka mai matuƙar ciwo da saka mutum zazzafan zazzaɓi,Dady Mansur fa ya haukace da wannan al'amarin,shin ina Abubakar yake?ina kuma aka kaishi yanzu?kukan ya cigaba da yi,ya kuma kasa koda motsawa daga wajen,ji yayi an tsaya akan sa,da sauri ya juyo ganin Dije yasa shi saurin tashi tsaye yana kade jikin sa, ƙoƙarin barin gurin yake ta dakatar dashi da maganar ta data kusan saka shi fitsari a wando,shin yallaɓai Mansur wai meye haɗin ka da dakin nan ne?can kwanaki kai ne ka fara hanani zuwa gurin nan dan cika umarnin uwar dakina kuma har kayi min gargaɗin sake ganina agurin,san nan ina yawan ganin ka a gurin shin me ka ɓoye acikin ɗakin da yanzu rasashi yasa ka irin wannan kukan da tunda nake ban taɓa ganin magidan ci kamar ka nayin irinsa ba?Dady Mansur kallon Dije kawai yake amma bai bata amsar ko ɗaya daga cikin tambayoyin ta ba,saima kaucewa da ya kuma yi dan barin wajen,cikin sauri Dije ta kuma cewa,Mansur kaji tsoran Allah ka bayyanawa mutane abinda kake aikatawa!'ko da bai bayyana ba ai yanzu mun gane shi kuma ko baka faɗa ba Mansur a kwai mugun abinda kake aikatawa!'cewar Dady Habib ke nan da isowar sa gurin kenan,Dady Mansur sakato yayi yana buɗe Habib da wani shegen kallo,tsawan sakanni shuru ya gifta ratsa tawajen,daga baya kuma Dady Mansur ya ɗauke kan sa daga kallon Dady Habib,tare da cigaba da tafiya ba tare da ya tanka musu ba,yanaji Dady Habib yana cewa tabbas anfara yin walƙiya acikin estate ɗin ALHAJI BALARABE kuma da sannu zamu ci gaba da binciko irin ku!'ya faɗa yana mai juyawa dan barin gurin.
Cikin sauri Dije ta koma ɗakin ta,ba abun da take sai kaiwa da kawowa, tabbas itama lokacin da tayiwa uwar ɗakin ta alƙawari yayi,so sai take son ganin ta dan sanar mata da abinda ta daɗe tana nema,yayin da ita kuma nata burin ita da Bintu zai cika na tona mata asiri dan sun riga sun shirya mata gadar zaren da baza ta iya fidda kanta ba,tun tuni wannan ranar take jira dan tabbas tasan idan ta kaiwa uwar ɗakinta wannan labarin ita kuma zata cika mata alƙawarin ta na bayyana mata fuskarta da kuma sakar mata yaran ta,ita kuma tuni ta shirya yadda wasan zai kasan ce,dan tasan yanzu matar ta sakan kan ce akanta dan kwantar da kanta tayi ta nuna mata tabbatas tana tare da ita ɗari bisa ɗari,dan haka tona asirin ta ba wani abun wahala bane agurin ta,wayar ta takalla tare da cizon yatsa dole sai dai ta jira kiranta,amma tasan dole zata kirata a cikin tsukin nan dan haka tana nan tana addu'a tare da jiran kiran ta ako da yaushe.
A hankali ya ke tashin ta har ta buɗe idanun ta dasu ka kunbura saboda kuka da damuwar da take ciki, tashi tayi tana ɗan duban wajen da suke ,amma dai batace masa komai ba,ganin damuwar dake cikin fuskarta ne yasa duk yaji jikin sa ya mutu,haɗa goshin sa yayi da nata sai ya zamana dogon hancin sa na gogar tsinin nata hancin,cikin sanyin murya yace", Bint ba son damuwar Nan,na daukar miki alƙawarin kamar yadda kika zama sanadin farinciki na nima sai na zama sanadin farin cikin ki,bazan bari kiyi kuka ba zan toshe duk wata hanyar damuwar ki,zan kawar da duk wani abun cutuwa A gareki,Bint zan samo miki fafinki da ummin ki aduk inda suke a faɗin duniyar nan!'.....
Fatima y AdamâœðŸ½
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ¼*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
```Page 51 ```
Ko yanzu ma na tanadar miki da abinda zai iya rage miki damuwa!'ya faɗa yana goga siririn hancin sa kan tsinin hancin ta,rufe idanun ta tayi tana ƙoƙarin maida hawayen da suke san zubo mata,A hankali yasa hannu yana goge mata fuskar tare da ɗan gyara mata ita,ɗage mata gira yayi tare da cewa har kin ɗan yi kyau,bana so su ganki cikin damuwa da yawa!'zata yi magana yayi mata alamar tayi shiru,haka ta haƙura da tambayar da take bakin ta,fita sukayi sai faman kallan anguwar take yi saboda har yanzu bata fahimci inda suke ba.
Duban ta yayi tare da cewa ki shiga sai kiyi min iso!:ɗan jim tayi kamar tana tunanin wani abu,sai kuma ta gyada masa kai tare da saka kanta cikin madaidai cin gidan na bulo,sallama tayi cikin sassanyar Muryar ta,HAJJO dake zaune jikin bishiyar mango dake girke a faffaɗan tsakar gidan tayi wata irin zabura har zanin ta na ƙoƙarin kuncewa,cewa take yi, wa nake ji kamar Lailata Allah Ubangiji ka amsa addu'a ta na ganin Laila araye,idan mafarki ne kuma ka barni a haka karka farkar dani!'ta faɗa tana ƙarasawa bakin ƙofar da Bintu ta cokare agurin,zaro ido Hajjo tayi tare da dafe kirji bakinta har rawa yake gurin kiran Asma'u, Asma'u dake cikin daki tana haɗa wanki ta fito da gudu tana cewa lafiya Hajjo me yasa mek,,,,maganar ce ta maƙale mata sakamakon tozali da tayi da Bintu.
Alhaji Baba yayi wani ɗan murmushi na takaici kana ya cigaba da cewa,a yau kuma a yanzu nasa afara rokon ALLAH ba dare ba rana idan Abubakar yana lafiya Allah ya baiyana mana shi idan baya cikin haicinsa kuma Allah ya bashi lafiya ya dawo min dashi cikin gidan nan,idan kuma ya mutu,,,,,kukan Hajiya Babba ne ya dakatar da shi daga barin abinda zai faɗa,cikin kuka da matsanancin tashin hankali tace"dan Allah Alhaji karka ƙarasa,inason ganin jagora araye (dake sunan da take gaya masa mafi lokata acikin mutane saboda karar ɗan fari)taci gaba da cewa Wallahi inaso yazo gidan nan araye inaso naga waɗanda suka gurgunta min rayuwar sa akan abin ɗun,,,,bata ƙarasa ba inno ta rufe mata baki tare da girgiza mata kai,alamun kar ta faɗi abinda ke cikin zuciyar ta,tunda shi Alhaji Baba baƙo ne akan sanin hakan,zai iya zurfafa bincike akan al'amarin,shurun kuwa tayi bata sake cewa komai ba,sai dai kukan da taci gaba dayi ƙasa ƙasa,yayin da Hajjah ta zuba musu idanun ayar tambaya da wannan sabon Al'amarin, wai meke shirin faruwa a gidan nan ne haka? Alhaji Baba yace"dama abinda nake son sanar daku kenan kowa zai iya tafiya!'daga haka ya miƙe ya shige can cikin ƙuryar ɗakin sa,jiki asan yaye suka dinga ficewa daga falon kowa ya kasa magana dan sun rasa abin cewa,wasu farin cikine ya hana su magantuwa wasu kuma bakin ciki,kowa ya fita daga falon sai Abba Umar da Aliyu,da kuma Dady Habib,sai su inno,Abba Umar yace"Hajiya Babba ku daina kuka komai ya kusa wucewa insha Allah tun da har muka samu Alhaji Baba da kansa yayi maganar yaya,kuma daga nan nima gurin wani malami na zan wuce Musa aƙara tsanan ta rokon Allah!'Dady Habib yace"tabbas maganar Umar haka take nima ina da malaman da zan saka cikin lamarin, san nan a ganina ya kamata a hada da cigiya gidajen rediyo ko za a dace!'Hajjah tace"hakan yayi Allah yayi muku albarka!'shi Abba Aliyu ma atake nan ya fara kiran malaman sa kasan cewar shi malamin addinni ne ya fara shela yana sanar dasu asaka almajirai sauka,yanzu zai taho da kayan sadaka,inno tace"masha Allah Ubangiji Allah ya baiyana mana shi cikin farin ciki da cikakken lafiya!'gaba ɗaya suka amsa da Amin summa Amin.
Tunda ya fito yaji wani irin jiri na san kayar dashi,amma duk da haka sai da ya nufi ɓangaren ƙonannen dakin,zubewa yayi agurin yana cigaba da wani irin kuka mai matuƙar ciwo da saka mutum zazzafan zazzaɓi,Dady Mansur fa ya haukace da wannan al'amarin,shin ina Abubakar yake?ina kuma aka kaishi yanzu?kukan ya cigaba da yi,ya kuma kasa koda motsawa daga wajen,ji yayi an tsaya akan sa,da sauri ya juyo ganin Dije yasa shi saurin tashi tsaye yana kade jikin sa, ƙoƙarin barin gurin yake ta dakatar dashi da maganar ta data kusan saka shi fitsari a wando,shin yallaɓai Mansur wai meye haɗin ka da dakin nan ne?can kwanaki kai ne ka fara hanani zuwa gurin nan dan cika umarnin uwar dakina kuma har kayi min gargaɗin sake ganina agurin,san nan ina yawan ganin ka a gurin shin me ka ɓoye acikin ɗakin da yanzu rasashi yasa ka irin wannan kukan da tunda nake ban taɓa ganin magidan ci kamar ka nayin irinsa ba?Dady Mansur kallon Dije kawai yake amma bai bata amsar ko ɗaya daga cikin tambayoyin ta ba,saima kaucewa da ya kuma yi dan barin wajen,cikin sauri Dije ta kuma cewa,Mansur kaji tsoran Allah ka bayyanawa mutane abinda kake aikatawa!'ko da bai bayyana ba ai yanzu mun gane shi kuma ko baka faɗa ba Mansur a kwai mugun abinda kake aikatawa!'cewar Dady Habib ke nan da isowar sa gurin kenan,Dady Mansur sakato yayi yana buɗe Habib da wani shegen kallo,tsawan sakanni shuru ya gifta ratsa tawajen,daga baya kuma Dady Mansur ya ɗauke kan sa daga kallon Dady Habib,tare da cigaba da tafiya ba tare da ya tanka musu ba,yanaji Dady Habib yana cewa tabbas anfara yin walƙiya acikin estate ɗin ALHAJI BALARABE kuma da sannu zamu ci gaba da binciko irin ku!'ya faɗa yana mai juyawa dan barin gurin.
Cikin sauri Dije ta koma ɗakin ta,ba abun da take sai kaiwa da kawowa, tabbas itama lokacin da tayiwa uwar ɗakin ta alƙawari yayi,so sai take son ganin ta dan sanar mata da abinda ta daɗe tana nema,yayin da ita kuma nata burin ita da Bintu zai cika na tona mata asiri dan sun riga sun shirya mata gadar zaren da baza ta iya fidda kanta ba,tun tuni wannan ranar take jira dan tabbas tasan idan ta kaiwa uwar ɗakinta wannan labarin ita kuma zata cika mata alƙawarin ta na bayyana mata fuskarta da kuma sakar mata yaran ta,ita kuma tuni ta shirya yadda wasan zai kasan ce,dan tasan yanzu matar ta sakan kan ce akanta dan kwantar da kanta tayi ta nuna mata tabbatas tana tare da ita ɗari bisa ɗari,dan haka tona asirin ta ba wani abun wahala bane agurin ta,wayar ta takalla tare da cizon yatsa dole sai dai ta jira kiranta,amma tasan dole zata kirata a cikin tsukin nan dan haka tana nan tana addu'a tare da jiran kiran ta ako da yaushe.
A hankali ya ke tashin ta har ta buɗe idanun ta dasu ka kunbura saboda kuka da damuwar da take ciki, tashi tayi tana ɗan duban wajen da suke ,amma dai batace masa komai ba,ganin damuwar dake cikin fuskarta ne yasa duk yaji jikin sa ya mutu,haɗa goshin sa yayi da nata sai ya zamana dogon hancin sa na gogar tsinin nata hancin,cikin sanyin murya yace", Bint ba son damuwar Nan,na daukar miki alƙawarin kamar yadda kika zama sanadin farinciki na nima sai na zama sanadin farin cikin ki,bazan bari kiyi kuka ba zan toshe duk wata hanyar damuwar ki,zan kawar da duk wani abun cutuwa A gareki,Bint zan samo miki fafinki da ummin ki aduk inda suke a faɗin duniyar nan!'.....
Fatima y AdamâœðŸ½
💕
*KUDURAR ALLAH* 💕
*NA*
*FATIMA Y. ADAM*
_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'SâœðŸ¼*
*🇦SSOCIATIONðŸ¤ðŸ»*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
```Page 51 ```
Ko yanzu ma na tanadar miki da abinda zai iya rage miki damuwa!'ya faɗa yana goga siririn hancin sa kan tsinin hancin ta,rufe idanun ta tayi tana ƙoƙarin maida hawayen da suke san zubo mata,A hankali yasa hannu yana goge mata fuskar tare da ɗan gyara mata ita,ɗage mata gira yayi tare da cewa har kin ɗan yi kyau,bana so su ganki cikin damuwa da yawa!'zata yi magana yayi mata alamar tayi shiru,haka ta haƙura da tambayar da take bakin ta,fita sukayi sai faman kallan anguwar take yi saboda har yanzu bata fahimci inda suke ba.
Duban ta yayi tare da cewa ki shiga sai kiyi min iso!:ɗan jim tayi kamar tana tunanin wani abu,sai kuma ta gyada masa kai tare da saka kanta cikin madaidai cin gidan na bulo,sallama tayi cikin sassanyar Muryar ta,HAJJO dake zaune jikin bishiyar mango dake girke a faffaɗan tsakar gidan tayi wata irin zabura har zanin ta na ƙoƙarin kuncewa,cewa take yi, wa nake ji kamar Lailata Allah Ubangiji ka amsa addu'a ta na ganin Laila araye,idan mafarki ne kuma ka barni a haka karka farkar dani!'ta faɗa tana ƙarasawa bakin ƙofar da Bintu ta cokare agurin,zaro ido Hajjo tayi tare da dafe kirji bakinta har rawa yake gurin kiran Asma'u, Asma'u dake cikin daki tana haɗa wanki ta fito da gudu tana cewa lafiya Hajjo me yasa mek,,,,maganar ce ta maƙale mata sakamakon tozali da tayi da Bintu.